< 2 Ljetopisa 28 >

1 Ahazu je bilo dvadeset godina kad se zakraljio, a kraljevao je šesnaest godina u Jeruzalemu, ali nije činio što je pravo u Jahvinim očima kao što je činio njegov otac David.
Ahaz yana da shekara ashirin sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara goma sha shida. Ba kamar Dawuda kakansa ba, bai yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji ba.
2 Živio je poput izraelskih kraljeva, pa je i likove salio baalima.
Ya yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra’ila ya kuma yi zubin gumaka domin a bauta wa Ba’al.
3 Sam je prinosio kad u dolini Hinomova sina i proveo vlastite sinove kroz oganj, po gnusnom običaju krivobožačkih naroda što ih je Jahve protjerao pred Izraelovim sinovima.
Ya ƙone hadayu a Kwarin Ben Hinnom, ya kuma miƙa’ya’yansa maza a cikin wuta, yana bin hanyoyi banƙyama na al’umman da Ubangiji ya kora a gaban Isra’ilawa.
4 Prinosio je žrtve i kadio po uzvišicama i brežuljcima i pod svakim zelenim drvetom.
Ya miƙa hadayu, ya kuma ƙone turare a masujadan kan tudu, a bisa tuddai da kuma ƙarƙashin kowane itace mai inuwa.
5 Zato ga Jahve, njegov Bog, predade u ruke aramejskom kralju te ga on potuče, zarobi mu veliko mnoštvo ljudi i odvede ih u Damask. Još je bio predan u ruke izraelskom kralju koji ga je hametice porazio.
Saboda haka Ubangiji Allahnsa ya miƙa shi ga sarkin Aram. Arameyawa suka ci shi a yaƙi, suka kuma kwashe mutanensa da yawa a matsayin’yan kurkuku, suka kawo Damaskus. Ya kuma ba da shi ga sarkin Isra’ila, wanda ya jijji masa a yaƙi.
6 Remalijin je sin Pekah pobio među Judejcima sto dvadeset tisuća hrabrih junaka u jedan dan, jer su bili ostavili Jahvu, Boga svojih otaca.
A rana ɗaya Feka ɗan Remaliya ya kashe sojoji dubu ɗari da dubu ashirin a Yahuda, domin Yahuda sun yashe Ubangiji Allah na kakanninsu.
7 A junak od Efrajimova plemena Zikri pogubio je kraljeva sina Maaseju i dvorskoga upravitelja Azrikama i Elkanu, drugoga do kralja.
Zikri, wani jarumin Efraim, ya kashe Ma’asehiya ɗan sarki, Azrikam hafsa mai lura da fada, da kuma Elkana, mataimakin sarki.
8 Izraelovi su sinovi zarobili od svoje braće dvjesta tisuća žena, sinova i kćeri, a zadobili su i silan plijen od njih i odnijeli ga u Samariju.
Isra’ilawa suka kame kamammu daga’yan’uwansu mata,’ya’ya maza da kuma’ya’ya mata dubu ɗari biyu. Suka kuma kwashe ganima mai yawan gaske, waɗanda suka kwasa zuwa Samariya.
9 Ondje bijaše Jahvin prorok po imenu Oded; izašao on pred vojsku što je išla u Samariju i rekao: “Gle, Jahve, Bog vaših otaca, razjario se na Judejce i zato ih je predao u vaše ruke te ste ih gnjevno pobili da je do neba doprlo.
Amma wani annabin Ubangiji mai suna Oded yana a can, sai ya fito don yă sadu da mayaƙa sa’ad da suke komowa zuwa Samariya. Ya ce musu, “Domin Ubangiji Allah na kakanninku yana fushi da Yahuda, ya ba da su cikin hannunku. Sai kuka kashe su cikin fushin da ya kai sama.
10 A sada još mislite podjarmiti Judejce i Jeruzalemce da vam budu robovi i robinje; a ipak, niste li i vi puni krivice prema Jahvi, svome Bogu?
Yanzu kuma kuna niyya ku mai da maza da matan Yahuda da Urushalima bayinku. Amma ku ɗin ba ku da laifin zunubi ga Ubangiji Allahnku ne?
11 Zato me poslušajte sada i vratite to roblje što ga zarobiste od svoje braće, jer će se izliti na vas Jahvin gnjev.”
To, ku saurare ni! Ku mai da’yan’uwanku da kuka kama a matsayin’yan kurkuku, gama fushin Ubangiji yana a kanku.”
12 Tada ustadoše neki između glavara Efrajimovih sinova, i to Johananov sin Azarja, Mešilemotov sin Berekja i Šalumov sin Ezekija, Hadlajev sin Amasa, na one što su se vraćali s vojske.
Sai waɗansu shugabanni a Efraim, Azariya ɗan Yehohanan, Berekiya ɗan Meshillemot, Hezekiya ɗan Shallum da Amasa ɗan Hadlai, suka tasar wa waɗanda suke isowa daga yaƙi.
13 Pa im rekoše: “Nemojte dovoditi ovamo toga roblja, jer, uz krivicu koja je na nama pred Jahvom, vi mislite još dometnuti na naše grijehe i na našu krivicu, kao da nije dosta velika naša krivica i jarosni gnjev na Izraelu.”
Suka ce, “Dole ku kawo waɗannan’yan kurkukun a nan, ko kuwa za ku yi laifi a gaban Ubangiji. Kuna niyya ku ƙara ga zunubinmu da kuma laifinmu? Gama laifinmu ya riga ya yi yawa, kuma fushinsa mai tsanani yana a kan Isra’ila.”
14 Tada ostaviše ratnici roblje i plijen pred knezovima i svim zborom.
Saboda haka sojoji suka ba da’yan kurkukun da ganima a gaban hafsoshi da dukan taron.
15 Onda su poimence prozvani ljudi ustali, osokolili robove, obukli sve gole u odjeću iz plijena; a kad su ih obukli, obuli, nahranili, napojili i namazali, poveli su na magarcima sve iznemogle i odveli ih u palmov grad Jerihon do njihove braće, a potom se vratili u Samariju.
Sai mutanen da aka kira sunansu suka tashi, suka ɗauki kamammun, da ganimar, suka sa wa dukan waɗanda suke tsirara sutura. Suka sa musu sutura, suka ba su takalma, suka ba su abinci da abin sha, suka shafa musu mai. Suka hawar da dukan raunana a kan jakuna, suka kai su wurin’yan’uwansu a Yeriko, wato, Birnin Itatuwan Dabino, sa’an nan suka koma Samariya.
16 U to je doba kralj Ahaz zamolio asirske kraljeve da mu pomognu.
A lokacin nan Sarki Ahaz ya aika wurin sarkin Assuriya neman taimako.
17 Edomci bijahu opet navalili i porazili Judejce te ih odveli u roblje.
Mutanen Edom sun sāke zuwa suka yaƙi Yahuda suka kuma kwashe’yan kurkuku,
18 Filistejci se raširili po gradovima Judejske Šefele i Negeba i, zauzevši Bet-Šemeš, Ajalon, Gederot i Soko sa selima, Timnu sa selima i Gimzo sa selima, nastanili se ondje.
yayinda Filistiyawa suka kai hari wa garuruwa a gindin tuddai da kuma a Negeb na Yahuda. Suka kame su suka kuma zauna a Bet-Shemesh, Aiyalon da Gederot, haka ma Soko, Timna da Gimzo tare da ƙauyuka kewayensu.
19 Jahve je počeo ponižavati Judejce zbog judejskoga kralja Ahaza, jer je Ahaz razuzdao Judejce i teško se iznevjerio Jahvi.
Ubangiji ya ƙasƙantar da Yahuda saboda Ahaz sarkin Isra’ila, gama ya hadasa mugunta a Yahuda kuma ya kasance marar aminci ga Ubangiji.
20 Došao je na nj asirski kralj Tiglat-Pileser i pritijesnio ga umjesto da ga utvrdi.
Tiglat-Fileser sarkin Assuriya ya zo wurinsa, sai ya wahalar da sarki Ahaz maimakon taimakonsa.
21 Ahaz bijaše opljačkao Jahvin Dom, kraljevski dvor i knezove, i sve to dao asirskom kralju, ali mu ništa nije pomoglo.
Ahaz ya ɗauki waɗansu abubuwa daga haikalin Ubangiji da kuma daga fadan sarki da kuma daga sarakuna, ya ba da su ga sarkin Assuriya, amma wannan bai taimake shi ba.
22 Dok je bio u nevolji, postao je još nevjerniji Jahvi; takav je bio kralj Ahaz.
Cikin lokacin wahalarsa Sarki Ahaz ya ƙara zama marar aminci ga Ubangiji.
23 Počeo je žrtvovati damaščanskim bogovima koji su ga porazili, misleći: “Kad bogovi aramejskih kraljeva njima pomažu, žrtvovat ću im da bi i meni pomagali.” Ali su oni bili na propast njemu i svem Izraelu.
Ya miƙa hadayu ga allolin Damaskus, waɗanda suka ci shi a yaƙi; gama ya yi tunani, “Da yake allolin sarakunan Aram sun taimake su, zan miƙa hadayu domin su taimake ni.” Amma suka zama sanadin fāɗuwarsa da kuma fāɗuwar dukan Isra’ila.
24 Ahaz je pokupio posuđe iz Božjega Doma, slupao ga, zatvorio vrata Jahvina Doma i podigao žrtvenike po svim uglovima u Jeruzalemu.
Ahaz ya tattara kayayyaki daga haikalin Allah ya kwashe su. Ya kulle ƙofofin haikalin Ubangiji ya kakkafa bagadai a kowace kusurwa a titin Urushalima.
25 I u svakom je pojedinom judejskom gradu podigao uzvišice da kadi tuđim bogovima, dražeći Jahvu, Boga otaca.
A kowane gari a Yahuda, ya gina masujadan kan tudu don ƙone hadayu ga waɗansu alloli, ya kuma tsokane Ubangiji Allah na kakanninsa ya yi fushi.
26 Ostala su njegova djela i svi njegovi putovi, od prvih do posljednjih, zapisani u Knjizi o judejskim i izraelskim kraljevima.
Sauran ayyukan mulkinsa da dukan hanyoyinsa, daga farko zuwa ƙarshe, suna a rubuce a littafin sarakunan Yahuda da Isra’ila.
27 Onda je Ahaz počinuo kod otaca. Sahranili su ga u Gradu, u Jeruzalemu, ali ga nisu unijeli u grobnicu judejskih kraljeva. Na njegovo se mjesto zakraljio sin mu Ezekija.
Ahaz ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a birnin Urushalima, amma ba a sa shi a makabartan sarakunan Isra’ila ba. Sai Hezekiya ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.

< 2 Ljetopisa 28 >