< 1 Samuelova 7 >

1 Tada dođoše ljudi iz Kirjat Jearima i odnesoše Kovčeg Jahvin sebi. Unesoše ga u kuću Abinadabovu, na uzvišici, i posvetiše njegova sina Eleazara da čuva Kovčeg Jahvin.
Mutanen Kiriyat Yeyarim suka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji. Suka kai a gidan Abinadab da ke kan tudu, suka keɓe Eleyazar ɗansa yă lura da akwatin alkawarin Ubangiji.
2 Od dana kad je Kovčeg bio postavljen u Kirjat Jearimu, prođe mnogo vremena - dvadeset godina - i sav je dom Izraelov uzdisao za Jahvom.
Akwatin Alkawarin ya daɗe a Kiriyat Yeyarim ya kai shekara ashirin cif. Sai dukan mutanen Isra’ila suka yi makoki suka nemi Ubangiji.
3 Tada Samuel progovori svemu domu Izraelovu ovako: “Ako se od svega srca svoga vraćate Jahvi, uklonite iz svoje sredine tuđe bogove, baale i aštarte, i upravite srce svoje Jahvi i njemu jedinome služite. Tada će vas on izbaviti iz ruke Filistejaca.”
Saboda haka Sama’ila ya yi magana da dukan gidan Isra’ila ya ce, in har da zuciya ɗaya kuke juyowa ga Ubangiji sai ku raba kanku da baƙin alloli da gunkin nan Ashtarot, ku ba da kanku ga Ubangiji. Ku yi masa bauta shi kaɗai, zai kuɓutar da ku daga hannun Filistiyawa.
4 Sinovi Izraelovi ukloniše nato baale i aštarte i služahu jedinome Jahvi.
Sai Isra’ilawa suka rabu da gumakan Ba’al da Ashtarot suka bauta wa Ubangiji kaɗai.
5 Samuel tada zapovjedi: “Skupite sve sinove Izraelove u Mispu da se pomolim Jahvi za vas.”
Sama’ila ya ce, “Ku tattara dukan Isra’ila a Mizfa, ni kuwa zan yi addu’a ga Ubangiji dominku.”
6 Oni se dakle skupiše u Mispi; ondje su grabili vodu i izlijevali je pred Jahvom. I postili su onaj dan i priznavali: “Sagriješili smo Jahvi!” I Samuel je sudio sinovima Izraelovim u Mispi.
Sa’ad da suka taru a Mizfa, suka kawo ruwa suka zuba a gaban Ubangiji. A wannan rana suka yi azumi suka tuba, suka ce, “Mun yi wa Ubangiji zunubi!” Sama’ila kuwa ya zauna a Mizfa ya yi mulkin Isra’ilawa.
7 Kad su Filistejci čuli da su se sinovi Izraelovi skupili u Mispi, krenu filistejski knezovi da napadnu na Izraela. Kad to vidješe sinovi Izraelovi, uplašiše se Filistejaca.
Da Filistiyawa suka ji cewa Isra’ila sun taru a Mizfa, sai shugabanninsu suka zo don su yaƙe Isra’ila. Da Isra’ilawa suka ji labarin, sai suka tsorata saboda Filistiyawa.
8 I zamoliše sinovi Izraelovi Samuela: “Ne prestaj vapiti za nas Jahvi, Bogu našemu, da nas izbavi iz ruke Filistejaca.”
Suka ce wa Sama’ila, “Kada ka fasa kai kukanmu ga Ubangiji Allahnmu saboda mu, don yă cece mu daga hannun Filistiyawa.”
9 Samuel uze jedno janje sisanče i prinese ga Jahvi kao žrtvu paljenicu i glasno se pomoli Jahvi za Izraela, i Jahve ga usliša.
Sama’ila ya kama ɗan rago ya miƙa shi ɗungum hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji. Ya yi roƙo ga Ubangiji a madadin Isra’ila, Ubangiji kuwa ya amsa addu’arsa.
10 Dok je Samuel prinosio žrtvu paljenicu, Filistejci su došli da udare na Izraela, ali Jahve toga dana zagrmi silnom grmljavinom na Filistejce i tako ih prestraši i smete da su podlegli Izraelu.
Lokacin da Sama’ila yana miƙa hadaya ta ƙonawa, Filistiyawa suka matso kusa don su yi yaƙi da Isra’ila. A ranar Ubangiji ya sa babban tsawa ya ruɗar da Filistiyawa har suka gudu a gaban Isra’ilawa.
11 Ratnici izraelski iziđoše iz Mispe i potjeraše Filistejce, tukući ih sve do ispod Bet Kara.
Isra’ilawa suka fito a guje daga Mizfa suka fafari Filistiyawa suka yi ta karkashe su a hanya har kwarin Bet-Kar.
12 A Samuel uze jedan kamen i postavi ga između Mispe i Ješane i nazva ga imenom Eben Haezer govoreći: “Dovde nam je Jahve pomogao.”
Sa’an nan Sama’ila ya ɗauki dutse ya kafa tsakanin Mizfa da Shen, ya sa masa suna, Ebenezer ma’ana, “Har zuwa wannan lokaci Ubangiji ya taimake mu.”
13 Tako su Filistejci bili poniženi i nikada više ne navališe na zemlju Izraelovu, a ruka je Jahvina pritiskivala Filistejce svega vijeka Samuelova.
Ta haka Isra’ilawa suka ci Filistiyawa. Daga ranan Filistiyawa ba su ƙara yin nasara a kan Isra’ila ba. Ubangiji ya yi gāba da Filistiyawa har ƙarshen zamanin Sama’ila.
14 I gradove koje Filistejci bijahu zauzeli od Izraela vratiše se njemu, od Ekrona do Gata, i Izrael oslobodi njihovo područje iz ruke filistejske. I bio je mir između Izraela i Amorejaca.
Filistiyawa suka mayar wa Isra’ila da garuruwan da suka ƙwato, wato, daga Ekron zuwa Gat, dukan yankin ƙasarsu da yake ƙarƙashin ikon Filistiyawa. Aka kuma sami zaman lafiya tsakanin Isra’ilawa da Amoriyawa.
15 Samuel je bio sudac u Izraelu svega svoga vijeka.
Sama’ila kuwa ya ci gaba da mulkin Isra’ila dukan rayuwarsa.
16 Svake je godine obilazio Betel, Gilgal i Mispu i u svim je tim mjestima sudio Izraelu.
Shekara-shekara Sama’ila yakan fita rangadi zuwa Betel, da Gilgal da Mizfa inda yakan yi musu shari’a.
17 Zatim se vraćao u Ramu, jer je ondje imao svoju kuću i ondje je sudio Izraelu. Ondje je podigao i žrtvenik Jahvi.
Amma yakan komo Rama inda gidansa yake, a nan yakan yi wa Isra’ila shari’a. A nan ne kuma ya gina wa Ubangiji bagade.

< 1 Samuelova 7 >