< 1 Kraljevima 14 >

1 U ono se vrijeme razbolje Abija, sin Jeroboamov,
A lokacin Abiya, ɗan Yerobowam ya kamu da ciwo,
2 i Jeroboam reče svojoj ženi: “Ustani i preobuci se da te ne bi prepoznali da si žena Jeroboamova; i idi u Šilo. Ondje je prorok Ahija: onaj koji mi je prorokovao da ću biti kraljem ovoga naroda.
sai Yerobowam ya ce wa matarsa, “Ki tafi, ki ɓad da kama, don kada a gane ke a matsayin matar Yerobowam. Ki je Shilo. Annabi Ahiya yana a can, wannan wanda ya ce mini zan zama sarki a bisa wannan mutane.
3 I ponesi deset hljebova, kolača i posudu meda i otiđi k njemu! On će ti reći što će biti s dječakom.”
Ki ɗauki dunƙulen burodi goma tare da ke, da waina, da tulun zuma, ki tafi wurinsa. Zai faɗa miki abin da zai faru da yaron.”
4 I učini tako žena Jeroboamova: ustade, ode u Šilo i uđe u kuću Ahijinu. A on nije više vidio, oslabile mu oči od duboke starosti.
Saboda haka matar Yerobowam ta yi abin da ya faɗa, ta kuma tafi gidan Ahiya a Shilo. Yanzu dai Ahiya ba ya gani; idanunsa sun tafi saboda tsufa.
5 Ali mu je Jahve rekao: “Evo dolazi žena Jeroboamova da od tebe traži savjeta za svoga sina jer je bolestan; a ti ćeš joj reći tako i tako. Kad bude ulazila, pretvarat će se kao da je druga.”
Amma Ubangiji ya ce wa Ahiya, “Matar Yerobowam tana zuwa tă tambaye ka game da ɗanta, gama yana ciwo, za ka kuwa ba ta amsa kaza da kaza. Sa’ad da ta iso za tă yi kamar wata ce dabam.”
6 Kad Ahija ču šum njenih koraka na vratima, reče joj: “Uđi, ženo Jeroboamova! Što se pretvaraš da si druga, kad imam tešku vijest za tebe?
Saboda haka sa’ad da Ahiya ya ji motsin sawunta a ƙofa, sai ya ce, “Ki shigo, matar Yerobowam. Me ya sa kike yi kamar wata ce dabam? An aiko ni wurinki da labari marar daɗi.
7 Idi, reci Jeroboamu: 'Ovako kaže Jahve, Bog Izraelov: Podigao sam te isred naroda i učinio sam te knezom nad mojim narodom Izraelom,
Je ki faɗa wa Yerobowam cewa ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Na tā da kai daga cikin mutane, na mai da kai shugaba a bisa mutanena Isra’ila.
8 istrgnuo sam kraljevstvo iz kuće Davidove i dao ga tebi. Ali ti nisi bio kao moj sluga David, koji je držao moje zapovijedi i koji me slijedio svim srcem svojim i činio samo ono što je pravedno u mojim očima.
Na yage mulki daga gidan Dawuda na ba da shi gare ka, amma ba ka zama kamar bawana Dawuda wanda ya kiyaye umarnaina ya kuma bi ni da dukan zuciyarsa, yana yin abin da yake daidai kaɗai a idanuna ba.
9 Ti si radio kudikamo gore od svojih prethodnika, otišao si i načinio sebi druge bogove, salio si im likove da me dražiš, mene si bacio za leđa.
Ka aikata mugunta fiye da dukan waɗanda suka rayu kafin kai. Ka yi wa kanka waɗansu alloli, gumakan da aka yi da ƙarfe; ka tsokane ni na yi fushi, ka kuma juye mini baya.
10 Zato, evo, puštam zlo na kuću Jeroboamovu, istrijebit ću iz obitelji Jeroboamove sve što mokri uza zid, robove i slobodnjake u Izraelu; ja ću netragom pomesti kuću Jeroboamovu kao što se mete nečist, da ga ništa ne ostane.
“‘Saboda wannan, zan kawo masifa a gidan Yerobowam. Zan yanke kowane ɗa na ƙarshe a Isra’ila, bawa ko’yantacce. Zan ƙone gidan Yerobowam kamar yadda mutum yakan ƙone juji, sai duk ya ƙone ƙurmus.
11 One koji iz Jeroboamove obitelji umru u gradu, proždrijet će psi, a one koji umru u polju, pojest će ptice nebeske.' - Eto tako je Jahve rekao.
Karnuka za su ci waɗanda suka mutu na Yerobowam a cikin birni, kuma tsuntsayen sararin sama za su cinye waɗanda suka mutu a jeji. Ni Ubangiji na faɗa!’
12 A ti ustani i pođi svome domu: tek što nogama stupiš u grad, dječak će umrijeti.
“Ke kuma, ki koma gida. Sa’ad da kika taka ƙafa a birninki, yaron zai mutu.
13 Sav će ga Izrael oplakati i pokopat će ga. On će biti jedini iz obitelji Jeroboamove položen u grob, jer se jedino na njemu našlo nešto što se u kući Jeroboamovoj svidjelo Jahvi, Bogu Izraelovu.
Dukan Isra’ila kuwa za su yi makoki dominsa. Shi ne kaɗai na Yerobowam wanda za a binne, domin shi ne kaɗai a gidan Yerobowam wanda Ubangiji, Allah na Isra’ila ya sami wani ɗan abu mai kyau a kansa.
14 Jahve će sebi postaviti kralja nad Izraelom i taj će istrijebiti kuću Jeroboamovu. Evo dana! Što? Čak i trenutka!
“Ubangiji zai tā da wani sarki wa kansa a bisa Isra’ila wanda zai hallaka iyalin Yerobowam. Ko yanzu ma, wannan zai fara faruwa.
15 Jahve će udariti Izraela te će se njihati kao trska u vodi. Iščupat će Izraela iz ove dobre zemlje koju je dao njihovim ocima i rasijat će ih s onu stranu Rijeke, jer su načinili sebi ašere koje srde Jahvu.
Ubangiji kuma zai bugi Isra’ila, har tă zama kamar kyauro mai girgiza a bakin rafi. Zai tumɓuke Isra’ila daga wannan ƙasa mai kyau da ya ba wa kakanninsu, yă watsar da su gaba da Kogin Yuferites domin sun tsokane Ubangiji har ya yi fushi, ta wurin yin ginshiƙan Ashera.
16 Odbacit će Izraela kao smeće, zbog grijeha što ih je učinio Jeroboam i na koje je navodio Izraela.”
Zai kuma ba da Isra’ila saboda zunuban da Yerobowam ya yi, da ya kuma sa Isra’ila suka yi.”
17 Žena Jeroboamova ustade i ode. Stigla je u Tirsu, a kad je prelazila kućni prag, dječak bijaše mrtav.
Sai matar Yerobowam ta tashi ta tafi, ta kuwa tafi Tirza. Nan da nan da ta taka madogarar ƙofar gidan, sai yaron ya mutu.
18 Pokopali su ga i sav ga je Izrael oplakao prema riječi koju je Jahve rekao po sluzi svome proroku Ahiji.
Suka binne shi, dukan Isra’ila kuwa suka yi makoki dominsa, yadda Ubangiji ya faɗa ta wurin bawansa annabi Ahiya.
19 Ostala povijest Jeroboamova, kako je ratovao i kraljevao, to je zapisano u knjizi Ljetopisa kraljeva izraelskih.
Sauran ayyukan sarautar Yerobowam, da yaƙe-yaƙensa, da yadda ya yi mulki, ba a rubuce suke a littafin tarihi na sarakunan Isra’ila ba?
20 Jeroboamovo kraljevanje trajalo je dvadeset i dvije godine, zatim je Jeroboam počinuo kraj otaca svojih, a sin mu Nadab zakraljio se mjesto njega.
Ya yi mulki shekaru ashirin da biyu, sai ya huta tare da kakanninsa. Sai Nadab ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
21 Roboam, sin Salomonov, bio je kralj Judejaca; bijaše mu četrdeset i jedna godina kad je postao kraljem, a sedamnaest je godina kraljevao u Jeruzalemu, u gradu koji Jahve izabra između svih izraelskih plemena da ondje postavi svoje Ime. Majka mu se zvala Naama, a bila je Amonka.
Rehobowam ɗan Solomon ya zama sarki a Yahuda. Yana da shekara arba’in da ɗaya sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekaru goma sha bakwai a Urushalima, birnin da Ubangiji ya zaɓa daga cikin dukan kabilan Isra’ila don yă sa Sunansa. Sunan mahaifiyarsa Na’ama, ita mutuniyar Ammon ce.
22 I Juda učini zlo u očima Jahvinim. Grijesima koje su počinili razjarili su ga više od svega što su učinili njihovi oci.
Yahuda ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. Ta wurin zunuban da suka yi, sun tā da fushin kishinsa fiye da yadda kakanninsu suka yi.
23 Jer su i oni podigli uzvišice, stupove i ašere na svakom brežuljku i pod svakim zelenim drvetom.
Sun kuma kafa wa kansu masujadai da suke kan tuddai, da a kan keɓaɓɓun duwatsu, suka kuma gina ginshiƙan Ashera a kowane tudu, da kuma a ƙarƙashin kowane duhuwar itace.
24 Bilo je čak posvećenih bludnica u zemlji. Oponašao je sve grozote naroda što ih je Jahve otjerao ispred sinova Izraelovih.
Har ma akwai maza karuwai na masujada. Mutane suka sa kansu ga yin kowane abin ƙyama na al’umman da Ubangiji ya kora kafin Isra’ilawa.
25 Pete godine Roboamova kraljevanja egipatski kralj Šišak navali na Jeruzalem.
A shekara ta biyar ta Sarki Rehobowam, Shishak sarkin Masar ya kai wa Urushalima yaƙi.
26 Opljačka sve blago iz Doma Jahvina i riznicu kraljevskog dvora; sve je uzeo; uze i sve zlatne štitove što ih bijaše napravio Salomon.
Ya kwashe dukiyar haikalin Ubangiji da kuma dukiyar fadan sarki. Ya ɗauki kome, har da dukan garkuwoyi na zinariya da Solomon ya yi.
27 Namjesto njih kralj Roboam napravi tučane štitove i povjeri ih zapovjednicima straže koja je čuvala vrata kraljevskog dvora.
Saboda haka sarki Rehobowam ya yi garkuwoyin tagulla ya mayar da su. Ya kuma naɗa waɗannan shugabannin matsara ya sa su aiki a ƙofar zuwa fadan sarki.
28 Kad je god kralj išao u Jahvin Dom, stražari su ih uzimali, a poslije ih vraćali u stražaru.
Duk sa’ad da sarki ya tafi wurin haikalin Ubangiji, matsara sukan riƙe garkuwoyinsu, daga baya kuma sai su mai da su ɗakin tsaro.
29 Ostala povijest Roboamova, sve što je učinio, zar nije zapisano u knjizi Ljetopisa kraljeva judejskih?
Game da sauran ayyukan mulkin Rehobowam kuwa, da kuma dukan abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
30 Za sve vrijeme bio je rat između Roboama i Jeroboama.
Aka ci gaba da yaƙe-yaƙe tsakanin Rehobowam da Yerobowam.
31 Roboam je počinuo sa svojim ocima i bi sahranjen sa svojim ocima u Davidovu gradu. Majka mu se zvala Naama, a bila je Amonka. Na njegovo se mjesto zakraljio sin mu Abijam.
Sai Rehobowam ya huta da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a Birnin Dawuda. Sunan mahaifiyarsa Na’ama, ita kuwa mutuniyar Ammon ce. Sai Abiyam ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.

< 1 Kraljevima 14 >