< 1 Ljetopisa 13 >
1 David je vijećao s tisućnicima, stotnicima i sa svim vođama.
Sai Dawuda ya tattauna da kowane ɗaya daga cikin shugabanninsa, shugabannin sojoji na dubu-dubu da na ɗari-ɗari.
2 I reče on svemu zboru Izraelovu: “Ako vam je pravo te ako je naš Bog Jahve odlučio tako, poslat ćemo glasnike k svojoj ostaloj braći u svim izraelskim zemljama, a tako i svećenicima s njima i levitima po gradovima pašnjaka njihovih, da se ujedine s nama.
Sa’an nan ya ce wa dukan taron Isra’ila, “In ya yi muku kyau kuma in nufin Ubangiji Allahnmu ne, bari mu aika da saƙo nesa da kuma ko’ina zuwa ga sauran’yan’uwanmu a duk iyakokin Isra’ila, da kuma zuwa ga firistoci da Lawiyawa waɗanda suke tare da su a garuruwansu da makiyayansu, su zo wurinmu.
3 Prenijet ćemo k sebi Kovčeg svoga Boga, jer ga nismo doista tražili za Šaulovih dana.”
Bari mu ɗauko akwatin alkawarin Allahnmu mu kawo wurinmu, gama ba mu neme shi a lokacin mulkin Shawulu ba.”
4 Sav zbor odluči da se tako učini, jer je to bilo pravo u očima svega naroda.
Dukan taron jama’a suka yarda su yi haka, domin ya yi daidai ga dukan mutane.
5 Tako je David sabrao sav narod Izraelov od Egipatskoga Šihora pa do Ulaza u Hamat da donesu Kovčeg Božji iz Kirjat Jearima.
Saboda haka Dawuda ya tattara dukan Isra’ilawa, daga Kogin Shihor a Masar zuwa Lebo Hamat, don su kawo akwatin alkawarin Allah daga Kiriyat Yeyarim.
6 Pošao je David sa svim Izraelom u Baalu, u Kirjat Jearim, koji je u Judi, da odande ponesu Kovčeg Božji nazvan imenom Jahve, koji stoluje nad kerubinima.
Dawuda da dukan Isra’ilawa tare da shi suka tafi Ba’ala na Yahuda (Kiriyat Yeyarim) don su haura daga can su kawo akwatin alkawarin Allah Ubangiji, wanda yake zama tsakanin kerubobi, akwatin alkawarin da ake kira da Sunan.
7 Povezli su Kovčeg Božji na novim kolima iz Abinadabove kuće; a Uza i Ahjo upravljali su kolima.
Suka ɗauki akwatin alkawarin Allah daga gidan Abinadab a kan sabon keken shanu, Uzza da Ahiyo ne suke lura da shi.
8 David i sav Izrael igrali su pred Bogom iz sve snage pjevajući uza zvuke citara, harfa, bubnjeva, cimbala i truba.
Dawuda da dukan Isra’ilawa suka yi shagali da dukan ƙarfinsu a gaban Allah, tare da waƙoƙi da garayu, molaye, ganguna, kuge da ƙahoni.
9 Kad su došli do Kidonova gumna, posegnu Uza rukom da pridrži Kovčeg jer ga volovi umalo ne prevrnuše.
Sa’ad da suka kai masussukar Kidon, Uzza ya miƙa hannunsa don yă gyara akwatin alkawarin, gama shanun sun yi tuntuɓe.
10 Ali se Jahve razgnjevio na Uzu i udario ga zato što je pružio ruku prema Kovčegu. Umro je ondje pred Bogom.
Sai fushin Ubangiji ya ƙuna a kan Uzza, ya kuma buge shi domin ya sa hannunsa a kan akwatin alkawarin. Sai ya mutu a can a gaban Allah.
11 Davidu bijaše žao što je Jahve onako udario Uzu i on prozva ono mjesto Peres Uza, kako se zove i dan-danas.
Ran Dawuda ya ɓace domin Ubangiji ya husata a kan Uzza, kuma har wa yau ana ce da wannan wuri Ferez Uzza.
12 Toga se dana David uplaši Boga i reče: “Kako ću donijeti k sebi Kovčeg Božji?”
Dawuda ya ji tsoron Allah a wannan rana ya kuma yi tambaya, “Yaya zan taɓa kawo akwatin alkawarin Allah gare ni?”
13 Nije dao svratiti Kovčega k sebi u Davidov grad nego ga skloni u kuću Obed-Edoma Gitejca.
Don haka bai ɗauki akwatin alkawarin ya kasance tare da shi a Birnin Dawuda ba. A maimakon haka, ya kai shi gidan Obed-Edom mutumin Gat.
14 I ostade Kovčeg Božji kod Obed-Edomove obitelji, u njegovoj kući, tri mjeseca. Jahve stoga blagoslovi Obed-Edomovu kuću i sve što je imao.
Akwatin Alkawarin Allah ya zauna tare da iyalin Obed-Edom a gidansa wata uku, Ubangiji kuwa ya albarkaci gidan Obed-Edom da kome da yake da shi.