< 詩篇 66 >

1 一篇詩歌,交與伶長。 全地都當向上帝歡呼!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Waƙa. Zabura. Ku yi sowa ta farin ciki ga Allah, dukan duniya!
2 歌頌他名的榮耀! 用讚美的言語將他的榮耀發明!
Ku rera ɗaukaka ga sunansa; ku sa yabonsa yă zama da ɗaukaka!
3 當對上帝說:你的作為何等可畏! 因你的大能,仇敵要投降你。
Ku ce wa Allah, “Ayyukanka da banmamaki suke! Ikonka da girma yake har abokan gābanka suna durƙusa a gabanka.
4 全地要敬拜你,歌頌你, 要歌頌你的名。 (細拉)
Dukan duniya sun rusuna a gabanka suna rera yabo gare ka, suna rera yabo ga sunanka.” (Sela)
5 你們來看上帝所行的, 他向世人所做之事是可畏的。
Ku zo ku ga abin da Allah ya yi, ayyukansa masu banmamaki a madadin mutum!
6 他將海變成乾地,眾民步行過河; 我們在那裏因他歡喜。
Ya juya teku zuwa busasshiyar ƙasa, sun wuce cikin ruwaye da ƙafa, ku zo, mu yi farin ciki a cikinsa.
7 他用權能治理萬民,直到永遠。 他的眼睛鑒察列邦; 悖逆的人不可自高。 (細拉)
Yana mulki har abada ta wurin ikonsa, idanunsa suna duban al’ummai, kada’yan tawaye su tayar masa. (Sela)
8 萬民哪,你們當稱頌我們的上帝, 使人得聽讚美他的聲音。
Ku yabi Allahnku, ya mutane, bari a ji ƙarar yabonsa;
9 他使我們的性命存活, 也不叫我們的腳搖動。
ya adana rayukanmu ya kuma kiyaye ƙafafunmu daga santsi.
10 上帝啊,你曾試驗我們, 熬煉我們,如熬煉銀子一樣。
Gama kai, ya Allah, ka gwada mu; ka tace mu kamar azurfa.
11 你使我們進入網羅, 把重擔放在我們的身上。
Ka kawo mu cikin kurkuku ka kuma jibga kaya masu nauyi a bayanmu.
12 你使人坐車軋我們的頭; 我們經過水火, 你卻使我們到豐富之地。
Ka bar mutane suka hau a kawunanmu; mun bi ta wuta da ruwa, amma ka kawo mu zuwa wurin yalwa.
13 我要用燔祭進你的殿, 向你還我的願,
Zan zo haikalinka da hadayun ƙonawa zan kuwa cika alkawurana gare ka,
14 就是在急難時我嘴唇所發的、 口中所許的。
alkawuran da leɓunana suka yi alkawari bakina kuma ya faɗa sa’ad da nake cikin wahala.
15 我要把肥牛作燔祭, 將公羊的香祭獻給你, 又把公牛和山羊獻上。 (細拉)
Zan miƙa kitsen dabbobi gare ka da kuma baye-baye na raguna; zan miƙa bijimai da awaki. (Sela)
16 凡敬畏上帝的人,你們都來聽! 我要述說他為我所行的事。
Ku zo ku saurara, dukanku waɗanda suke tsoron Allah; bari in faɗa muku abin da ya yi mini.
17 我曾用口求告他; 我的舌頭也稱他為高。
Na yi kuka gare shi da bakina; yabonsa yana a harshena.
18 我若心裏注重罪孽, 主必不聽。
Da a ce na ji daɗin zunubi a zuciyata, da Ubangiji ba zai saurara ba;
19 但上帝實在聽見了; 他側耳聽了我禱告的聲音。
amma tabbatacce Allah ya saurara ya kuma ji muryata a cikin addu’a.
20 上帝是應當稱頌的! 他並沒有推卻我的禱告, 也沒有叫他的慈愛離開我。
Yabo ga Allah, wanda bai ƙi addu’ata ba ko yă janye ƙaunarsa daga gare ni!

< 詩篇 66 >