< 詩篇 60 >

1 大衛與兩河間的亞蘭並瑣巴的亞蘭爭戰的時候,約押轉回,在鹽谷攻擊以東,殺了一萬二千人。那時,大衛作這金詩,叫人學習,交與伶長。調用為證的百合花。 上帝啊,你丟棄了我們,使我們破敗; 你向我們發怒,求你使我們復興!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin Alkawari.” Wani miktam ta Dawuda. Don koyarwa. Sa’ad da ya yaƙi Aram-Naharayim da Aram-Zoba, da kuma sa’ad da Yowab ya dawo ya bugi mutanen Edom dubu goma sha biyu a Kwarin Gishiri. Ka ki mu, ya Allah, ka kuma fashe kāriyarmu; ka yi fushi da mu, yanzu ka mai da mu!
2 你使地震動,而且崩裂; 求你將裂口醫好,因為地搖動。
Ka girgiza ƙasar ka kuma tsaga ta; ka daure karayarta, gama tana rawa.
3 你叫你的民遇見艱難; 你叫我們喝那使人東倒西歪的酒。
Ka nuna wa mutanenka lokutan wahala; ka ba mu ruwan inabin da ya sa muka bugu.
4 你把旌旗賜給敬畏你的人, 可以為真理揚起來。 (細拉)
Amma ga waɗanda suke tsoronka, ka ɗaga tuta don a buɗe gāba da baka. (Sela)
5 求你應允我們,用右手拯救我們, 好叫你所親愛的人得救。
Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.
6 上帝已經指着他的聖潔說:我要歡樂; 我要分開示劍,丈量疏割谷。
Allah ya yi magana daga wurinsa mai tsarki, “Da nasara zan rarraba Shekem in kuma auna Kwarin Sukkot.
7 基列是我的,瑪拿西也是我的。 以法蓮是護衛我頭的; 猶大是我的杖。
Gileyad nawa ne, Manasse kuma nawa ne; Efraim shi ne hular kwanona, Yahuda kuma sandar mulkina.
8 摩押是我的沐浴盆; 我要向以東拋鞋。 非利士啊,你還能因我歡呼嗎?
Mowab shi ne kwanon wankina, a kan Edom zan jefa takalmina; a bisa Filistiya zan yi kirarin nasara.”
9 誰能領我進堅固城? 誰能引我到以東地?
Wa zai kawo ni birnin katanga? Wa zai bishe ni zuwa Edom?
10 上帝啊,你不是丟棄了我們嗎? 上帝啊,你不和我們的軍兵同去嗎?
Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
11 求你幫助我們攻擊敵人, 因為人的幫助是枉然的。
Ka ba mu gudummawa a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
12 我們倚靠上帝才得施展大能, 因為踐踏我們敵人的就是他。
Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattake abokan gābanmu.

< 詩篇 60 >