< 詩篇 18 >

1 耶和華的僕人大衛的詩,交與伶長。當耶和華救他脫離一切仇敵和掃羅之手的日子,他向耶和華念這詩的話。說: 耶和華,我的力量啊,我愛你!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Ya rera ta ga Ubangiji kalmomin wannan waƙa sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa da kuma daga hannun Shawulu, ya ce, Ina ƙaunarka, ya Ubangiji, ƙarfina.
2 耶和華是我的巖石,我的山寨,我的救主, 我的上帝,我的磐石,我所投靠的。 他是我的盾牌, 是拯救我的角,是我的高臺。
Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona; Allahna shi ne dutsena, a gare shi nake neman mafaka. Shi ne garkuwata da ƙahon cetona, mafakata.
3 我要求告當讚美的耶和華; 這樣我必從仇敵手中被救出來。
Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa kuɓuta daga abokan gābana.
4 曾有死亡的繩索纏繞我, 匪類的急流使我驚懼,
Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni; rigyawan hallaka sun sha kaina.
5 陰間的繩索纏繞我, 死亡的網羅臨到我。 (Sheol h7585)
Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe kewaye da ni; tarkon mutuwa ya yi mini arangama. (Sheol h7585)
6 我在急難中求告耶和華, 向我的上帝呼求。 他從殿中聽了我的聲音; 我在他面前的呼求入了他的耳中。
Cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; Na yi kuka ga Allahna don taimako. A Haikalinsa ya ji muryata, Kukana na neman taimako ya kai kunnensa.
7 那時,因他發怒,地就搖撼戰抖; 山的根基也震動搖撼。
Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, tussan duwatsu sun girgiza; sun yi rawa domin ya yi fushi.
8 從他鼻孔冒煙上騰; 從他口中發火焚燒,連炭也着了。
Hayaƙi ya tashi daga kafan hancinsa; wuta mai ci daga bakinsa, garwashi wuta mai ci daga bakinsa.
9 他又使天下垂,親自降臨, 有黑雲在他腳下。
Ya buɗe sammai ya sauko; baƙaƙen gizagizai suna a ƙarƙashin ƙafafunsa.
10 他坐着基路伯飛行; 他藉着風的翅膀快飛。
Ya hau kerubobi ya kuma yi firiya; ya yi shawagi a fikafikan iska.
11 他以黑暗為藏身之處, 以水的黑暗、天空的厚雲為他四圍的行宮。
Ya mai da duhu abin rufuwarsa, rumfa kewaye da shi, baƙaƙen gizagizan ruwan sama na sarari,
12 因他面前的光輝, 他的厚雲行過便有冰雹火炭。
daga cikin hasken kasancewarsa gizagizai suka yi gaba, da ƙanƙara da kuma walƙiya.
13 耶和華也在天上打雷; 至高者發出聲音便有冰雹火炭。
Ubangiji ya yi tsawa daga sama; muryar Mafi Ɗaukaka ya yi kāra.
14 他射出箭來,使仇敵四散; 多多發出閃電,使他們擾亂。
Ya harba kibiyoyinsa ya kuma watsar da abokan gāba, walƙiya mai girma ya fafare su.
15 耶和華啊,你的斥責一發, 你鼻孔的氣一出, 海底就出現, 大地的根基也顯露。
Kwarin teku sun bayyana tussan duniya sun bayyana a fili sa’ad da ka tsawata, ya Ubangiji, sa’ad da ka numfasa daga hancinka.
16 他從高天伸手抓住我, 把我從大水中拉上來。
Ya miƙa hannunsa daga sama ya kama ni; ya ja ni daga zurfin ruwaye.
17 他救我脫離我的勁敵和那些恨我的人, 因為他們比我強盛。
Ya cece ni daga abokin gābana mai ƙarfi, daga abokan gābana, waɗanda suka fi ƙarfina.
18 我遭遇災難的日子,他們來攻擊我; 但耶和華是我的倚靠。
Sun yi arangama da ni a ranar masifa, amma Ubangiji ya zama mai taimakona.
19 他又領我到寬闊之處; 他救拔我,因他喜悅我。
Ya fitar da ni zuwa wuri mai sarari; ya kuɓutar da ni, gama yana jin daɗina.
20 耶和華按着我的公義報答我, 按着我手中的清潔賞賜我。
Ubangiji ya yi haka da ni bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya ba ni lada.
21 因為我遵守了耶和華的道, 未曾作惡離開我的上帝。
Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi mugunta ta wurin juyewa daga Allahna ba.
22 他的一切典章常在我面前; 他的律例我也未曾丟棄。
Dukan dokokinsa suna a gābana; ban juye daga ƙa’idodinsa ba.
23 我在他面前作了完全人; 我也保守自己遠離我的罪孽。
Na kasance marar laifi a gabansa na kuma kiyaye kaina daga zunubi.
24 所以,耶和華按我的公義, 按我在他眼前手中的清潔償還我。
Ubangiji ya ba ni lada bisa ga adalcina, bisa ga tsabtan hannuwana a gabansa.
25 慈愛的人,你以慈愛待他; 完全的人,你以完全待他。
Ga mai aminci ka nuna kanka mai aminci, ga marar laifi ka nuna kanka marar laifi,
26 清潔的人,你以清潔待他; 乖僻的人,你以彎曲待他。
ga mai tsabta ka nuna kanka mai tsabta, amma ga karkatacce, ka nuna kanka mai wayo.
27 困苦的百姓,你必拯救; 高傲的眼目,你必使他降卑。
Kakan cece mai sauƙinkai amma kakan ƙasƙantar da masu girman kai.
28 你必點着我的燈; 耶和華-我的上帝必照明我的黑暗。
Kai Ya Ubangiji, ka sa fitilata ta yi ta ci; Allahna ya mai da duhu ya zama haske.
29 我藉着你衝入敵軍, 藉着我的上帝跳過牆垣。
Da taimakonka zan iya fāɗa wa runduna; tare da Allahna zan iya rinjayi katanga.
30 至於上帝,他的道是完全的; 耶和華的話是煉淨的。 凡投靠他的,他便作他們的盾牌。
Game da Allah kuwa, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji marar kuskure ne. Shi garkuwa ne ga dukan waɗanda suke neman mafaka a gare shi.
31 除了耶和華,誰是上帝呢? 除了我們的上帝,誰是磐石呢?
Gama wane ne Allah in ba Ubangiji ba? Wane ne kuwa Dutse in ba Allahnmu ba?
32 惟有那以力量束我的腰、 使我行為完全的,他是上帝。
Allah ne ya ƙarfafa ni da ƙarfi ya kuma sa hanyarta ta zama cikakkiya.
33 他使我的腳快如母鹿的蹄, 又使我在高處安穩。
Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsaya a kan ƙwanƙoli.
34 他教導我的手能以爭戰, 甚至我的膀臂能開銅弓。
Ya horar da hannuwana don yaƙi; hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
35 你把你的救恩給我作盾牌; 你的右手扶持我; 你的溫和使我為大。
Ka ba ni garkuwar nasara, kuma hannunka na dama yana riƙe ni; ya sunkuya don ka mai da ni mai girma.
36 你使我腳下的地步寬闊; 我的腳未曾滑跌。
Ka fadada hanyar da yake a ƙarƙashina, don kada ɗiɗɗigena yă juya.
37 我要追趕我的仇敵,並要追上他們; 不將他們滅絕,我總不歸回。
Na bi abokan gābana na kuma cim musu; ban juya ba sai da na hallaka su.
38 我要打傷他們,使他們不能起來; 他們必倒在我的腳下。
Na ragargaza su har ba za su iya tashi ba; sun fāɗi a ƙarƙashin ƙafafuna.
39 因為你曾以力量束我的腰,使我能爭戰; 你也使那起來攻擊我的都服在我以下。
Ka ƙarfafa ni da ƙarfi saboda yaƙi; ka sa abokan gābana suka rusuna mini.
40 你又使我的仇敵在我面前轉背逃跑, 叫我能以剪除那恨我的人。
Ka sa abokan gābana suka juya suka gudu, na kuma hallaka abokan gābana.
41 他們呼求,卻無人拯救; 就是呼求耶和華,他也不應允。
Sun nemi taimako, amma ba su sami wanda zai cece su ba, ga Ubangiji, amma bai amsa ba.
42 我搗碎他們,如同風前的灰塵, 倒出他們,如同街上的泥土。
Na murƙushe su kamar ƙura mai laushi da iska ke kwashewa; na zubar da su kamar laka a tituna.
43 你救我脫離百姓的爭競, 立我作列國的元首; 我素不認識的民必事奉我。
Ka cece ni daga harin mutane; ka mai da ni kan al’ummai. Mutanen da ban sani ba sun zama bayina,
44 他們一聽見我的名聲就必順從我; 外邦人要投降我。
da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya; baƙi suna rusuna a gabana.
45 外邦人要衰殘, 戰戰兢兢地出他們的營寨。
Duk sukan karai; suna zuwa da rawan jiki daga mafakansu.
46 耶和華是活神。 願我的磐石被人稱頌; 願救我的上帝被人尊崇。
Ubangiji mai rai ne! Yabo ya tabbata ga Dutsena! Girma ya tabbata ga Allah Mai cetona!
47 這位上帝,就是那為我伸冤、 使眾民服在我以下的。
Shi ne Allah mai sāka mini, wanda yake sa al’ummai a ƙarƙashina,
48 你救我脫離仇敵, 又把我舉起,高過那些起來攻擊我的; 你救我脫離強暴的人。
wanda yakan cece ni daga abokan gābana. Ana girmama ka bisa abokan gābana; daga masu tā-da-na-zaune-tsaye ka kuɓutar da ni.
49 耶和華啊,因此我要在外邦中稱謝你, 歌頌你的名。
Saboda haka zan yabe ka a cikin al’ummai, ya Ubangiji; zan rera yabai ga sunanka.
50 耶和華賜極大的救恩給他所立的王, 施慈愛給他的受膏者, 就是給大衛和他的後裔,直到永遠。
Yakan ba sarkinsa nasarori; yakan nuna alheri marar ƙarewa ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.

< 詩篇 18 >