< 民數記 33 >
1 以色列人按着軍隊,在摩西、亞倫的手下出埃及地所行的路程記在下面。
Ga wuraren da Isra’ilawa suka yi sansani sa’ad da suka fito runduna-runduna a ƙarƙashin Musa da Haruna daga Masar.
2 摩西遵着耶和華的吩咐記載他們所行的路程,其路程乃是這樣:
Bisa ga umarnin Ubangiji, Musa ya rubuta wuraren tafiye-tafiyensu da sansaninsu. Ga yadda tafiye-tafiyen suka kasance.
3 正月十五日,就是逾越節的次日,以色列人從蘭塞起行,在一切埃及人眼前昂然無懼地出去。
Isra’ilawa sun tashi daga Rameses a rana ta goma sha biyar, ga watan fari, kashegarin Bikin Ƙetarewa. Suka fita gabagadi a gaban dukan Masarawa,
4 那時,埃及人正葬埋他們的長子,就是耶和華在他們中間所擊殺的;耶和華也敗壞他們的神。
waɗanda suke binne gawawwakin’ya’yan farinsu da Ubangiji ya karkashe; gama Ubangiji ya hukunta allolinsu.
Isra’ilawa suka tashi daga Rameses, suka yi sansani a Sukkot.
Suka tashi daga Sukkot, suka yi sansani a Etam, a gefen hamada.
7 從以倘起行,轉到比‧哈希錄,是在巴力‧洗分對面,就在密奪安營。
Suka tashi daga Etam, suka koma baya zuwa Fi Hahirot, wajen gabashin Ba’al-Zafon, suka yi sansani kusa da Migdol.
8 從比‧哈希錄對面起行,經過海中到了書珥曠野,又在伊坦的曠野走了三天的路程,就安營在瑪拉。
Suka tashi daga Fi Hahirot, suka ratsa cikin teku zuwa hamada, bayan sun yi tafiya kwana uku a cikin Hamadan Etam, sai suka yi sansani a Mara.
9 從瑪拉起行,來到以琳(以琳有十二股水泉,七十棵棕樹),就在那裏安營。
Suka tashi daga Mara, suka tafi Elim, inda akwai maɓulɓulan ruwa goma sha biyu, da itatuwan dabino guda saba’in, suka yi sansani a can.
Suka tashi daga Elim, suka yi sansani kusa da Jan Teku.
Suka tashi daga Jan Teku, suka yi sansani a Hamadan Sin.
Suka tashi daga Hamadan Sin, suka yi sansani a Dofka.
Suka tashi daga Dofka, suka yi sansani a Alush.
14 從亞錄起行,安營在利非訂;在那裏,百姓沒有水喝。
Suka tashi daga Alush, suka yi sansani a Refidim, inda babu ruwan da mutane za su sha.
Suka tashi daga Refidim, suka yi sansani a Hamadan Sinai.
Suka tashi daga Hamadan Sinai, suka yi sansani a Kibrot Hatta’awa.
Suka tashi daga Kibrot Hatta’awa, suka yi sansani a Hazerot.
Suka tashi daga Hazerot, suka yi sansani a Ritma.
Suka tashi daga Ritma, suka yi sansani a Rimmon Ferez.
Suka tashi daga Rimmon Ferez, suka yi sansani a Libna.
Suka tashi daga Libna, suka yi sansani a Rissa.
Suka tashi daga Rissa, suka yi sansani a Kehelata.
Suka tashi daga Kehelata, suka yi sansani a Dutsen Shefer.
Suka tashi daga Dutsen Shefer, suka yi sansani a Harada.
Suka tashi daga Harada, suka yi sansani a Makhelot.
Suka tashi daga Makhelot, suka yi sansani a Tahat.
Suka tashi daga Tahat, suka yi sansani a Tera.
Suka tashi daga Tera, suka yi sansani a Mitka.
Suka tashi daga Mitka, suka yi sansani a Hashmona.
Suka tashi daga Hashmona, suka yi sansani a Moserot.
Suka tashi daga Moserot, suka yi sansani a Bene Ya’akan.
Suka tashi daga Bene Ya’akan, suka yi sansani a Hor Haggidgad.
Suka tashi daga Hor Haggidgad, suka yi sansani a Yotbata.
Suka tashi daga Yotbata, suka yi sansani a Abrona.
Suka tashi daga Abrona, suka yi sansani a Eziyon Geber.
36 從以旬‧迦別起行,安營在尋的曠野,就是加低斯。
Suka tashi daga Eziyon Geber, suka yi sansani a Kadesh, cikin Hamadan Zin.
Suka tashi daga Kadesh, suka yi sansani a Dutsen Hor, a iyakar Edom.
38 以色列人出了埃及地後四十年,五月初一日,祭司亞倫遵着耶和華的吩咐上何珥山,就死在那裏。
Bisa ga umarni Ubangiji, Haruna firist, ya hau Dutsen Hor, inda ya mutu a rana ta fari ga watan biyar, a shekara ta arba’in, bayan Isra’ilawa suka fito daga Masar.
Haruna yana da shekara ɗari da ashirin da uku, sa’ad da ya mutu a Dutsen Hor.
40 住在迦南南地的迦南人亞拉得王聽說以色列人來了。
Sarki Arad Bakan’ane, wanda yake zaune a Negeb na Kan’ana, ya ji labari cewa Isra’ilawa suna zuwa.
Suka tashi daga Dutsen Hor, suka yi sansani a Zalmona.
Suka tashi daga Zalmona, suka yi sansani a Funon.
Suka tashi daga Funon, suka yi sansani a Obot.
44 從阿伯起行,安營在以耶‧亞巴琳,摩押的邊界。
Suka tashi daga Obot, suka yi sansani a Iye Abarim, a iyakar Mowab.
Suka tashi daga Iyim, suka yi sansani a Dibon Gad.
Suka tashi daga Dibon Gad, suka yi sansani a Almon Dibilatayim.
47 從亞門‧低比拉太音起行,安營在尼波對面的亞巴琳山裏。
Suka tashi daga Almon Dibilatayim, suka yi sansani a duwatsun Abarim, kusa da Nebo.
48 從亞巴琳山起行,安營在摩押平原-約旦河邊、耶利哥對面。
Suka tashi daga duwatsun Abarim, suka yi sansani a filayen Mowab kusa da Urdun, ɗaura da Yeriko.
49 他們在摩押平原沿約旦河邊安營,從伯‧耶施末直到亞伯‧什亭。
A can filayen Mowab, suka yi sansani kusa da Urdun ɗaura da Bet-Yeshimot har zuwa Abel-Shittim.
50 耶和華在摩押平原-約旦河邊、耶利哥對面曉諭摩西說:
A filayen Mowab kusa da Urdun ɗaura da Yeriko ne Ubangiji ya ce wa Musa,
51 「你吩咐以色列人說:你們過約旦河進迦南地的時候,
“Ka gaya wa Isra’ilawa cewa, ‘Sa’ad da kuka haye Urdun zuwa Kan’ana,
52 就要從你們面前趕出那裏所有的居民,毀滅他們一切鏨成的石像和他們一切鑄成的偶像,又拆毀他們一切的邱壇。
ku kori dukan mazaunan ƙasar a gabanku. Ku rurrushe sassaƙaƙƙun duwatsu, da siffofinsu na zubi, ku kuma rurrushe dukan masujadansu na kan tudu.
53 你們要奪那地,住在其中,因我把那地賜給你們為業。
Ku mallaki ƙasar, ku kuma zauna a ciki, gama na ba ku ƙasar, ku mallake ta.
54 你們要按家室拈鬮,承受那地;人多的,要把產業多分給他們;人少的,要把產業少分給他們。拈出何地給何人,就要歸何人。你們要按宗族的支派承受。
Ku rarraba ƙasar ta wurin jefan ƙuri’a, bisa ga kabilanku. Kabilar da take babba, a ba ta babban gādo, ƙarami kabila kuwa, a ba ta ƙaramin gādo. Duk abin da ƙuri’a ta ba su, shi zai zama nasu. Ku rarraba wannan bisa zuriyar kakanninku.
55 倘若你們不趕出那地的居民,所容留的居民就必作你們眼中的刺,肋下的荊棘,也必在你們所住的地上擾害你們。
“‘Amma in ba ku kori mazaunan ƙasar ba, waɗanda kuka bari su ci gaba da zama, za su zama muku hakki a idanunku, da kuma ƙayayyuwa a bayanku. Za su ba ku wahala a ƙasar da kuke zama.
56 而且我素常有意怎樣待他們,也必照樣待你們。」
Sa’an nan kuwa zan yi muku abin da na shirya yin musu.’”