< 何西阿書 6 >

1 來吧,我們歸向耶和華! 他撕裂我們,也必醫治; 他打傷我們,也必纏裹。
“Ku zo, mu koma ga Ubangiji. Ya yayyage mu kucu-kucu amma zai warkar da mu; ya ji mana ciwo amma zai daure mana miyakunmu.
2 過兩天他必使我們甦醒, 第三天他必使我們興起, 我們就在他面前得以存活。
Bayan kwana biyu zai rayar da mu, a rana ta uku zai tashe mu, don mu rayu a gabansa.
3 我們務要認識耶和華, 竭力追求認識他。 他出現確如晨光; 他必臨到我們像甘雨, 像滋潤田地的春雨。
Bari mu yarda da Ubangiji; bari mu nace gaba don mu yarda da shi. Muddin rana tana fitowa, zai bayyana; zai zo mana kamar ruwan bazara, kamar ruwan saman farko da yake jiƙe ƙasa.”
4 主說:以法蓮哪,我可向你怎樣行呢? 猶大啊,我可向你怎樣做呢? 因為你們的良善如同早晨的雲霧, 又如速散的甘露。
“Me zan yi da kai Efraim? Me zan yi da kai Yahuda? Ƙaunarku tana kamar hazon safiya, kamar raɓar safiya da takan ɓace.
5 因此,我藉先知砍伐他們, 以我口中的話殺戮他們; 我施行的審判如光發出。
Saboda haka na yayyaga ku kucu-kucu tare da annabawana, na kashe ku da kalmomin bakina; hukuntaina sun haskaka kamar walƙiya a kanku.
6 我喜愛良善,不喜愛祭祀; 喜愛認識上帝,勝於燔祭。
Gama jinƙai nake bukata, ba hadaya ba, ku kuma san Allah a maimakon hadayun ƙonawa.
7 他們卻如亞當背約, 在境內向我行事詭詐。
Kamar Adamu, sun tā da alkawari, sun yi mini rashin aminci a can.
8 基列是作孽之人的城, 被血沾染。
Gileyad birni ce ta mugayen mutane, da tabon alamun jini.
9 強盜成群,怎樣埋伏殺人, 祭司結黨,也照樣在示劍的路上殺戮, 行了邪惡。
Kamar yadda mafasa sukan yi fakon mutum, haka ƙungiyoyin firistoci suke; suna kisa a hanya zuwa Shekem, suna aikata laifofi bankunya.
10 在以色列家,我見了可憎的事; 在以法蓮那裏有淫行, 以色列被玷污。
Na ga wani abu mai bantsoro a gidan Isra’ila. A can Efraim ya miƙa wuya ga karuwanci Isra’ila kuma ta ƙazantu.
11 猶大啊,我使被擄之民歸回的時候, 必有為你所命定的收場。
“Ku kuma, ya mutanen Yahuda, na shirya muku ranar girbi. “A duk sa’ad da zan mayar da dukiya wa mutanena,

< 何西阿書 6 >