< 约伯记 29 >
Ayuba ya ci gaba da jawabinsa,
2 惟愿我的景况如从前的月份, 如 神保守我的日子。
“Da ma ina nan lokacin da ya wuce baya can, kwanakin da Allah yake lura da ni,
lokacin da fitilarsa take haske a kaina na yi tafiya cikin duhu tare da haskensa.
4 我愿如壮年的时候: 那时我在帐棚中, 神待我有密友之情;
Kwanakin da nake tasowa, lokacin da abokantakar Allah ta sa wa gidana albarka,
lokacin da Maɗaukaki yana tare da ni, kuma’ya’yana suna kewaye da ni,
lokacin da ake zuba madara a inda nake takawa, duwatsu kuma suna ɓulɓulo mini man zaitun.
“Sa’ad da na je ƙofar birni na zauna a bainin jama’a,
matasan da suka gan ni sukan ja gefe tsofaffi kuma suka tashi tsaye;
sarakuna suka yi shiru suka rufe bakunansu da hannuwansu;
Muryar manya ta yi tsit harshensu ya manne a rufin bakunansu.
11 耳朵听我的,就称我有福; 眼睛看我的,便称赞我;
Duk wanda ya ji ni ya yaba mini waɗanda suka gan ni kuma sun amince da ni,
domin na ceci matalauta waɗanda suka nemi taimako, da marasa mahaifi waɗanda ba su da wanda zai taimake su.
Mutumin da yake bakin mutuwa ya sa mini albarka. Na faranta wa gwauruwa zuciya.
Na yafa adalci ya zama suturata; gaskiya ita ce rigata da rawanina.
Ni ne idon makafi kuma ƙafa ga guragu.
16 我为穷乏人的父; 素不认识的人,我查明他的案件。
Ni mahaifi ne ga masu bukata; na tsaya wa baƙo.
17 我打破不义之人的牙床, 从他牙齿中夺了所抢的。
Na karya ƙarfin mugaye na ƙwato waɗanda suke riƙe da haƙoransu.
18 我便说:我必死在家中, 必增添我的日子,多如尘沙。
“Na yi tunani cewa, ‘Zan mutu a cikin gidana, kwanakina da yawa kamar turɓayar ƙasa.
Jijiyoyina za su kai cikin ruwa, kuma raɓa za tă kwanta a rassana dukan dare.
Ɗaukakata za tă kasance tare da ni garau, bakana koyaushe sabo ne a hannuna.’
“Mutane suna mai da hankali su saurare ni, suna yin shiru don su ji shawarata.
22 我说话之后,他们就不再说; 我的言语像雨露滴在他们身上。
Bayan da na yi magana, ba su ƙara ce kome ba. Maganata ta shige su.
Sukan jira ni kamar yadda ake jiran ruwan sama. Sukan sha daga cikin maganganuna kamar mai shan ruwan bazara.
24 他们不敢自信,我就向他们含笑; 他们不使我脸上的光改变。
Sa’ad da na yi musu murmushi da ƙyar sukan yarda; hasken fuskata yana da daraja a gare su.
25 我为他们选择道路,又坐首位; 我如君王在军队中居住, 又如吊丧的安慰伤心的人。
Na zaɓar masu inda za su bi na kuma zauna kamar sarkinsu; na zauna kamar sarki a cikin rundunansu; ina nan kamar mai yi wa masu makoki ta’aziyya.