< 约伯记 18 >

1 书亚人比勒达回答说:
Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
2 你寻索言语要到几时呢? 你可以揣摩思想,然后我们就说话。
“Yaushe za ka gama maganganun nan? Ka dawo da hankalinka sa’an nan za mu iya yin magana.
3 我们为何算为畜生, 在你眼中看作污秽呢?
Don me muke kamar shanu a wurinka, ka ɗauke mu mutanen wofi?
4 你这恼怒将自己撕裂的, 难道大地为你见弃、 磐石挪开原处吗?
Kai da ka yayyage kanka don haushi, za a yashe duniya saboda kai ne? Ko kuma duwatsu za su matsa daga wurinsu?
5 恶人的亮光必要熄灭; 他的火焰必不照耀。
“An kashe fitilar mugu; harshen wutarsa ya daina ci.
6 他帐棚中的亮光要变为黑暗; 他以上的灯也必熄灭。
Wutar cikin tentinsa ta zama duhu; fitilar da take kusa da shi ta mutu.
7 他坚强的脚步必见狭窄; 自己的计谋必将他绊倒。
Ƙarfin takawarsa ya ragu; dabararsa ta ja fāɗuwarsa.
8 因为他被自己的脚陷入网中, 走在缠人的网罗上。
Ƙafafunsa sun kai shi cikin raga, yana ta yawo a cikin ragar.
9 圈套必抓住他的脚跟; 机关必擒获他。
Tarko ya kama ɗiɗɗigensa; tarko ya riƙe shi kam.
10 活扣为他藏在土内; 羁绊为他藏在路上。
An ɓoye masa igiya da za tă zarge shi a ƙasa; an sa masa tarko a kan hanyar da zai bi.
11 四面的惊吓要使他害怕, 并且追赶他的脚跟。
Tsoro duk ya kewaye shi ta kowane gefe yana bin shi duk inda ya je.
12 他的力量必因饥饿衰败; 祸患要在他旁边等候。
Masifa tana jiransa; bala’i yana shirye yă fāɗa masa a lokacin da zai fāɗi.
13 他本身的肢体要被吞吃; 死亡的长子要吞吃他的肢体。
Ya cinye wani sashe na gaɓar jikinsa; ɗan fari na mutuwa ya cinye ƙafafunsa.
14 他要从所倚靠的帐棚被拔出来, 带到惊吓的王那里。
An yage shi daga zaman lafiyar da yake yi a cikin tentinsa aka sa shi tsoro sosai.
15 不属他的必住在他的帐棚里; 硫磺必撒在他所住之处。
Wuta ta cinye tentinsa; farar wuta ta rufe wurin da yake zama.
16 下边,他的根本要枯干; 上边,他的枝子要剪除。
Jijiyoyinsa sun bushe a ƙasa rassansa sun mutu a sama.
17 他的记念在地上必然灭亡; 他的名字在街上也不存留。
An manta da shi a duniya; ba wanda yake ƙara tunawa da shi.
18 他必从光明中被撵到黑暗里, 必被赶出世界。
An tura shi daga cikin haske zuwa cikin duhu, an kore shi daga duniya.
19 在本民中必无子无孙; 在寄居之地也无一人存留。
Ba shi da’ya’ya ko zuriya cikin mutanensa, ba sauran wanda yake a raye a wurin da ya taɓa zama.
20 以后来的要惊奇他的日子, 好像以前去的受了惊骇。
Mutanen Yamma suna mamakin abin da ya faru da shi; tsoro ya kama mutanen gabas.
21 不义之人的住处总是这样; 此乃不认识 神之人的地步。
Ba shakka haka wurin zaman mugun mutum yake, haka wurin zaman wanda bai san Allah ba yake.”

< 约伯记 18 >