< 以赛亚书 64 >
Da ma za ka tsage sammai ka sauko, ai, da duwatsu za su yi rawar jiki a gabanka!
2 好像火烧干柴, 又像火将水烧开, 使你敌人知道你的名, 使列国在你面前发颤!
Kamar sa’ad da wuta takan ci rassa ta sa ruwa ya tafasa, ka sauko ka sanar da sunanka ga abokan gābanka ka kuma sa al’ummai su yi rawan jiki a gabanka!
3 你曾行我们不能逆料可畏的事。 那时你降临,山岭在你面前震动。
Gama sa’ad da ka aikata abubuwan bantsoron da ba mu sa tsammani ba, ka sauko, duwatsu kuma suka yi rawar jiki a gabanka.
4 从古以来,人未曾听见、未曾耳闻、未曾眼见 在你以外有什么神为等候他的人行事。
Tun fil azal babu wanda ya taɓa ji, babu kunnen da ya gane, babu idon da ya ga wani Allah in ban da kai, wanda ya aikata waɗannan al’amura a madadin waɗanda suke sa zuciya a gare shi.
5 你迎接那欢喜行义、记念你道的人; 你曾发怒,我们仍犯罪; 这景况已久,我们还能得救吗?
Kakan taimaki waɗanda suke murnan yin abin da yake daidai, waɗanda sukan tuna da hanyoyinka. Amma sa’ad da muka ci gaba da yin zunubi, kakan yi fushi. Ta yaya za mu sami ceto ke nan?
6 我们都像不洁净的人; 所有的义都像污秽的衣服。 我们都像叶子渐渐枯干; 我们的罪孽好像风把我们吹去。
Dukanmu mun zama kamar wanda yake marar tsabta, kuma dukan ayyukanmu masu adalci sun zama kamar ƙazaman tsummoki; duk mun zama kamar busasshen ganye, kamar iska haka zunubanmu sukan share mu.
7 并且无人求告你的名; 无人奋力抓住你。 原来你掩面不顾我们, 使我们因罪孽消化。
Babu wanda yake kira bisa sunanka ko ya yi ƙoƙarin riƙe ka; gama ka ɓoye fuskarka daga gare mu ka kuma sa muka lalace saboda zunubanmu.
8 耶和华啊,现在你仍是我们的父! 我们是泥,你是窑匠; 我们都是你手的工作。
Duk da haka, Ubangiji, kai ne Ubanmu. Mu yumɓu ne, kai kuma mai ginin tukwane; dukanmu aikin hannunka ne.
9 耶和华啊,求你不要大发震怒, 也不要永远记念罪孽。 求你垂顾我们, 我们都是你的百姓。
Kada ka yi fushi fiye da kima, ya Ubangiji; kada ka tuna da zunubanmu har abada. Da ma ka dube mu, muna roƙonka, gama dukanmu mutanenka ne.
10 你的圣邑变为旷野。 锡安变为旷野; 耶路撒冷成为荒场。
Biranenka masu tsarki sun zama hamada; har Sihiyona ma ta zama hamada; Urushalima ta zama kango.
11 我们圣洁华美的殿— 就是我们列祖赞美你的所在被火焚烧; 我们所羡慕的美地尽都荒废。
Haikalinmu mai tsarki da kuma mai daraja, inda kakanninmu suka yabe ka, an ƙone da wuta, kuma dukan abubuwan da muke ƙauna sun lalace.
12 耶和华啊,有这些事,你还忍得住吗? 你仍静默使我们深受苦难吗?
Bayan dukan wannan, ya Ubangiji, ba za ka yi wani abu ba? Za ka yi shiru ka hore mu fiye da kima?