< 何西阿书 5 >

1 众祭司啊,要听我的话! 以色列家啊,要留心听! 王家啊,要侧耳而听! 审判要临到你们, 因你们在米斯巴如网罗, 在他泊山如铺张的网。
“Ku ji wannan, ku firistoci! Ku kasa kunne, ku Isra’ilawa! Ku saurara, ya ku gidan sarauta! Wannan hukunci yana a kanku, kun zama tarko a Mizfa, ragar da aka shimfiɗa a kan Tabor.
2 这些悖逆的人肆行杀戮, 罪孽极深; 我却斥责他们众人。
’Yan tawaye sun yi zurfi cikin kisan gilla. Zan hore su duka.
3 以法莲为我所知; 以色列不能向我隐藏。 以法莲哪,现在你行淫了, 以色列被玷污了。
Na san Efraim ƙaf; Isra’ila ba a ɓoye take a gare ni ba. Efraim, yanzu ka juya ka shiga karuwanci; Isra’ila ta lalace.
4 他们所行的使他们不能归向 神; 因有淫心在他们里面, 他们也不认识耶和华。
“Ayyukansu ba su ba su dama su koma ga Allahnsu ba. Halin karuwanci yana cikin zuciyarsu; ba su yarda da Ubangiji ba.
5 以色列的骄傲当面见证自己。 故此,以色列和以法莲必因自己的罪孽跌倒; 犹大也必与他们一同跌倒。
Girmankan Isra’ila yana ba da shaida a kansu; Isra’ilawa, har ma Efraim, sun yi tuntuɓe a cikin zunubinsu; Yahuda ma ya yi tuntuɓe tare da su.
6 他们必牵着牛羊去寻求耶和华,却寻不见; 他已经转去离开他们。
Sa’ad da suka tafi tare da garkunan shanu, tumaki da awakinsu don su nemi Ubangiji, ba za su same shi ba; ya janye kansa daga gare su.
7 他们向耶和华行事诡诈,生了私子。 到了月朔,他们与他们的地业必被吞灭。
Su marasa aminci ne ga Ubangiji; suna haihuwar shegu. Yanzu bukukkuwar Sabon Watansu za su cinye su da gonakinsu.
8 你们当在基比亚吹角, 在拉玛吹号, 在伯·亚文吹出大声,说: 便雅悯哪,有仇敌在你后头!
“Amon kakaki a Gibeya, ƙaho a Rama. Ku yi kirarin yaƙi a Bet-Awen; ku ja gaba, ya Benyamin.
9 在责罚的日子,以法莲必变为荒场; 我在以色列支派中,指示将来必成的事。
Efraim za tă zama kango a ranar hukunci. A cikin kabilan Isra’ila na yi shelar abin da yake tabbatacce.
10 犹大的首领如同挪移地界的人, 我必将忿怒倒在他们身上,如水一般。
Shugabannin Yahuda suna kamar waɗanda suke matsar da duwatsun shaidar da aka sa a kan iyaka ne. Zan zubo musu da fushina a kansu kamar rigyawar ruwa.
11 以法莲因乐从人的命令, 就受欺压,被审判压碎。
An danne Efraim, an murƙushe ta a shari’a ta ƙudura ga bin gumaka.
12 我使以法莲如虫蛀之物, 使犹大家如朽烂之木。
Na zama kamar asu ga Efraim, kamar ruɓa ga mutanen Yahuda.
13 以法莲见自己有病, 犹大见自己有伤, 他们就打发人往亚述去见耶雷布王, 他却不能医治你们, 不能治好你们的伤。
“Sa’ad da Efraim ya ga ciwonsa, Yahuda kuwa miyakunta, sai Efraim ya juya ga Assuriya, ya aika wurin babban sarki don neman taimako. Amma bai iya warkar da kai ba, bai iya warkar da miyakunka ba.
14 我必向以法莲如狮子, 向犹大家如少壮狮子。 我必撕裂而去, 我要夺去,无人搭救。
Gama zan zama kamar zaki ga Efraim, kamar babban zaki ga Yahuda. Zan yage su kucu-kucu in tafi; zan kwashe su, ba wanda zai kuɓutar da su.
15 我要回到原处, 等他们自觉有罪,寻求我面; 他们在急难的时候必切切寻求我。
Sa’an nan zan koma wurina sai sun yarda da laifinsu. Za su kuma nemi fuskata; cikin azabansu za su nace da nemana.”

< 何西阿书 5 >