< 啟示錄 21 >

1 ,我看見了一個新天新地,因為先前的天與先前的地已不見了,海也沒有了。
Sa’an nan na ga sabon sama da sabuwar duniya, gama sama na farko da duniya ta farko sun shuɗe, babu kuma wani teku.
2 我看見那新耶路撒冷聖城,從天上由天主那裏降下,就如一位裝飾好迎接自己丈夫的新娘。
Na ga Birni Mai Tsarki, sabuwar Urushalima tana saukowa daga sama, daga Allah, a shirye kamar amaryar da aka yi mata ado mai kyau saboda mijinta.
3 我聽見由寶座那裏有一巨大聲音說:「這就是天主與人同在的帳幕,他要同他們住在一起;他們要作他的人民,他親自要『與他們同在,』作他們的天主;
Na kuma ji wata babbar murya daga kursiyin tana cewa, “Yanzu mazaunin Allah yana tare da mutane, zai kuma zauna tare da su. Za su zama mutanensa, Allah kansa kuwa zai kasance tare da su yă kuma zama Allahnsu.
4 他要拭去他們眼上的一切淚痕;以後再也沒有死亡,再也沒有悲傷,沒有哀號,沒有苦楚,因為先前的都已過去了。」
Zai share dukan hawaye daga idanunsu. Ba sauran mutuwa ko makoki ko kuka ko azaba, gama tsofaffin al’amura sun shuɗe.”
5 那位坐在寶座上的說:「看,我已更新了一切。」又說:「你寫下來!因為這些話都是可信而真實的。」
Wannan da yake zaune a kursiyin ya ce. “Ina yin kome sabo!” Sai ya ce, “Rubuta wannan, domin waɗannan kalmomi amintattu ne gaskiya ne kuma.”
6 他又給我說:「已完成了!我是「阿耳法」和「敖默加,」元始和終末。我要把生命的水白白地賜給口渴的人喝。
Ya ce mini, “An gama. Ni ne Alfa da kuma Omega, na Farko da kuma na Ƙarshe. Duk mai jin ƙishirwa zan ba shi abin sha kyauta daga maɓulɓular ruwan rai.
7 勝利者必要承受這些福分:我要作他的天主,他要作我的兒子。
Duk wanda ya ci nasara zai gāji dukan wannan, zan kuma zama Allahnsa, shi kuma zai zama ɗana.
8 可是,為那些怯懦的、失信的、可恥的、殺人的、姦淫的、行邪術的、拜偶像的,以及一切撒謊的人,他們的地方是在烈火與硫磺燃燒著的坑中:這就是第二次死亡。」 (Limnē Pyr g3041 g4442)
Amma matsorata, da marasa bangaskiya, masu ƙazanta, masu kisankai, masu fasikanci, masu sihiri, masu bautar gumaka da dukan maƙaryata, wurinsu zai kasance a cikin tafkin wutar da yake farar wuta mai ci. Wannan fa ita ce mutuwa ta biyu.” (Limnē Pyr g3041 g4442)
9 那拿著七個滿盛最後七種災禍盂的七位天使,其中有一位來告訴我說:「你來!我要把羔羊的淨配新娘指給你看。」
Ɗaya daga cikin mala’ikun nan bakwai masu kwanonin nan bakwai cike da annoban nan bakwai na ƙarshe, ya zo ya ce mini “Zo, zan nuna maka amaryar, matar Ɗan Ragon.”
10 天使就使我神魂超拔,把我帶到一座又大又高的山上,將那從天上,由天主那裏降下的聖城耶路撒冷,指給我看。
Ya kuwa ɗauke ni cikin Ruhu zuwa wani babban dutse mai tsayi, ya kuma nuna mini Birni Mai Tsarki, Urushalima, tana saukowa daga sama, daga Allah.
11 這聖城具有天主的光榮;城的光輝,好似極貴重的寶石,像水晶那麼明亮的蒼玉;
Ya haskaka da ɗaukakar Allah, haskensa kuwa ya yi kamar lu’ulu’u mai daraja sosai, kamar yasfa, yana ƙyalƙyali kamar madubi.
12 城牆高而且大,有十二座門,守門的有十二位天使,門上寫著以色列子民十二支派的名字。
Yana da babbar katanga mai tsayi, mai ƙofofi goma sha biyu, da kuma mala’iku goma sha biyu a ƙofofin. A bisa ƙofofin an rubuta sunayen kabilu goma sha biyu na Isra’ila.
13 東面三門,北面三門,南面三門,西面三門。
Akwai ƙofofi uku a gabas, uku a arewa, uku a kudu, uku kuma a yamma.
14 城牆有十二座基石,上面刻著羔羊的十二位宗徒的十二個名字。
An gina katangar birnin a kan tushen gini goma sha biyu, a kansu kuwa akwai sunayen manzannin sha biyu na Ɗan Ragon.
15 同我談話的那位天使拿著金蘆葦測量尺,要測量那城、城門和城牆。
Mala’ikan da ya yi magana da ni yana da sandan awo na zinariya don awon birnin, ƙofofinsa, da kuma katangarsa.
16 城是四方形的,長寬相同。天使用蘆葦測量尺測量了那城,共計一萬二千「斯塔狄,」長、寬、高都相等;
Birnin murabba’i ne, tsayinsa daidai ne da fāɗinsa. Ya auna birnin da sandarsa ya kuwa sami mil 1,400 (wajen kilomita 2,200) tsawonsa, fāɗinsa da kuma tsayinsa daidai suke.
17 又測量了城牆,有一百四十四肘;天使用的,是人的尺寸。
Ya auna katangarsa ya kuma sami ƙaurinta kamun 144, bisa ga ma’aunin mutum, wanda mala’ikan ya yi amfani da shi.
18 城牆是用水蒼玉建造的,城是純金的,好像明淨的玻璃。
An yi katangar da yasfa, birnin kuma da zinariya zalla, yana kuma ƙyalli kamar madubi.
19 城牆的基石,是用各種寶石裝飾的:第一座基石是水蒼玉,第二座是藍玉,第三座是玉髓,第四座是翡翠,
Tushen ginin katangar birnin kuwa an yi masa adon da kowane irin dutse mai daraja. Tushe na farko an yi shi yasfa, na biyu saffaya, na uku agat, na huɗu zumurrudu,
20 第五座是赤瑪瑙,第六座是斑瑪瑙,第七座是橄欖石,第八座是綠柱石,第九座是黃玉,第十座是綠玉,第十一座是紫玉,第十二座是紫晶。
na biyar onis, na shida yakutu, na bakwai kirisolit, na takwas beril, na tara tofaz, na goma kirisofuras, na goma sha ɗaya yasin, na goma sha biyu kuma ametis.
21 十二座門是十二種珍珠,每一座門是由一種珍珠造的;城中的街道是純金的,好似透明的玻璃。
Ƙofofi goma sha biyun nan lu’ulu’ai goma sha biyu ne, kowace ƙofa an yi ta da lu’ulu’u guda. Babban titin birnin kuwa an yi shi da zinariya zalla, yana kuma ƙyalli kamar madubi.
22 在城內我沒有看見聖殿,因為上主全能的天主和羔羊就是她的聖殿。
Ban ga haikali a cikin birnin ba, domin Ubangiji Allah Maɗaukaki da kuma Ɗan Ragon ne haikalin birnin.
23 那城也不需要太陽和月亮光照,因為有天主的光榮照耀她;羔羊就是她的明燈。
Birnin ba ya bukatar rana ko wata su haskaka shi, gama ɗaukakar Allah tana ba shi haske, Ɗan Ragon kuwa shi ne fitilar birnin.
24 萬民都要藉著她的光行走,世上的君王也要把自己的光榮帶到她內。
Al’ummai za su yi tafiya cikin hasken birnin, sarakunan duniya kuma za su kawo darajarsu cikin birnin.
25 她的門白日總不關閉,因為那裏已沒有黑夜。
Ba za a taɓa rufe ƙofofin birnin da rana ba, gama ba za a yi dare a can ba.
26 萬民都要把自己的光榮和財富運到她內。
Za a kawo ɗaukaka da girmar al’ummai a cikin birnin.
27 凡不潔淨、行可恥的事及撒謊的,絕對不得進入她內;只有那些記載在羔羊生命冊上的,纔得進入。
Babu wani abu marar tsarkin da zai taɓa shiga cikin birnin, babu kuma wani mai aikata abin kunya ko ruɗi da zai shiga, sai dai waɗanda aka rubuta sunayensu a cikin littafin rai na Ɗan Ragon.

< 啟示錄 21 >