< 詩篇 69 >
1 達味作,交與樂官,調寄「百合。」 天主,求您從速拯救我;因大水已到我的頸脖。
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin.” Ta Dawuda. Ka cece ni, ya Allah, gama ruwa ya kai wuyata
2 我陷於泥獰中,沒有立足的處所;我沈入深水中,波濤已掩蓋了我。
Na nutse cikin laka mai zurfi, inda babu wurin tsayawa. Na shiga cikin ruwaye masu zurfi; rigyawa ya sha kaina.
3 我呼號得筋疲力竭,我已咽喉焦乾;我常期望我的天主,我已望眼欲穿。
Na gaji da kira ina neman taimako; maƙogwarona ya bushe idanuna sun dushe, suna neman Allahna.
4 無故憎恨我的人,比我的頭髮更繁,無理敵對我的人,比我的骨頭更堅硬;我沒有搶奪過的,我反而應該償還。
Waɗanda suke ƙina ba dalili sun fi gashin kaina yawa; da yawa ne abokan gābana babu dalili, su da suke nema su hallaka ni. An tilasta mini in mayar da abin da ban sata ba.
5 天主,我的愚昧,您知道得更為周詳。我的過犯,不能向您掩蓋隱藏。
Ka san wautata, ya Allah; laifina ba a ɓoye yake daga gare ka ba.
6 上主,萬軍的上主,願那仰望您的人,不要因我而蒙羞,以色列人的天主,願那尋覓您的人,不要因我而受辱。
Bari waɗanda suke sa zuciya gare ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki; bari waɗanda suke neman ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Allah na Isra’ila.
7 因為,我為了您已飽受欺凌,羞愧已經籠罩了我的面容。
Gama na jimre da ba’a saboda kai, kunya kuma ta rufe fuskata.
8 連我的兄弟們都以我為外賓,我母親的兒子都拿我當客人。
Ni baƙo ne a cikin’yan’uwana, bare kuma ga’ya’yan mahaifiyata maza;
9 我對您殿宇所懷的熱忱把我耗盡,並且那侮辱您者的辱罵落於我身。
gama himma da nake yi wa gidanka yana ƙunata, kuma zagi na masu zaginka yana fāɗuwa a kaina.
Sa’ad da na yi kuka na kuma yi azumi dole in jimre da ba’a;
11 我身上穿著麻布當作衣裳,也竟成了他們取笑的對象。
sa’ad da na sanya rigunan makoki, mutane suna maishe ni abin dariya.
12 閒坐門口的人,對我議論紛紛,喝醉烈酒的人,對我歌唱戲弄。
Masu zama a ƙofa suna mini ba’a, na zama waƙa a bakin bugaggu da giya.
13 上主,在這困厄的時日,我只有求救於您;天主,求您按您豐厚的慈愛應允我,求您以您救援的忠誠俯聽我。
Amma na yi addu’a gare ka, ya Ubangiji, a lokacin da ka ga dama; a cikin ƙaunarka mai girma, ya Allah, ka amsa mini da tabbacin ceto.
14 求您救我於污泥中,不要讓我沉沒。救我脫離恨我的人,走出大水旋渦,
Ka fid da ni daga laka, kada ka bari in nutse; ka cece ni daga waɗanda suke ƙina, daga rurin ruwaye.
15 求您不要讓波浪淹沒我,深淵吞滅我,也不要讓地窖合上自己的口埋葬我。
Kada ka bar rigyawa yă sha kaina ko zurfafa su haɗiye ni ko rami yă rufe bakinsa a kaina.
16 上主,求您照您和藹的慈愛俯允我,求您按您深厚的仁慈眷顧我。
Ka amsa mini, ya Ubangiji cikin alherin ƙaunarka; cikin jinƙanka mai girma ka juyo gare ni.
17 求您不要向您的僕人隱藏您的慈顏,因為我正處在困厄中,求您從速垂憐。
Kada ka ɓoye fuskarka daga bawanka; ka amsa mini da sauri, gama ina cikin wahala.
18 求您親近我的靈魂,施予救贖,為了我的諸般仇敵,求您救護。
Ka zo kusa ka kuɓutar da ni; ka fanshe ni saboda maƙiyana.
19 我受的侮辱、欺凌和恥笑,您都識穿;欺凌迫害我的眾人,都在您的眼前。
Ka san yadda ake mini ba’a, ake kunyatar da ni da kuma yadda nake shan kunya; dukan abokan gābana suna a gabanka.
20 侮辱破碎了我心,使我憂傷難過;我期望有人同情,卻未尋到一個,我渴盼有人來安慰,也未找到一個。
Ba’a ta sa zuciyata ta karai ta bar ni ba mataimaki; Na nemi a ji tausayina, amma ban sami ko ɗaya ba, na nemi masu ta’aziyya, amma ban sami ko ɗaya ba.
21 他們在我的食物中,攙上了苦膽,我口渴時,竟遞來酸醋要我下嚥,
Sun sa abin ɗaci cikin abincina suka kuma ba ni ruwan inabi mai tsami sa’ad da nake jin ƙishi.
22 願他們的筵席變成網羅,為同席的友人變為圈套!
Bari teburin da aka shirya a gabansu yă zama musu tarko; bari yă zama sakamakon laifi da kuma tarko.
23 願他們的眼睛昏迷失明,使他們的雙腰顫抖不停!
Bari idanunsu yă dushe don kada su gani, bayansu kuma yă tanƙware har abada.
24 求您向他們傾洩您的盛怒,讓您的怒火把他們籠罩住。
Ka kwarara fushinka a kansu; bari fushinka mai zafi yă ci musu.
25 願他們的居所變成荒土,願他們的帳幕無人再住!
Bari wurinsu yă zama kufai; kada ka bar wani yă zauna a tentunansu.
26 因為他們繼續打擊您所打擊的人,他們另加苦害您所傷殘的人。
Gama sun tsananta wa waɗanda ka hukunta suna kuma taɗin wahalar waɗanda ka ji musu rauni.
27 願您在他們的罪罰上增加罪罰,不要使他們在您面前稱義自誇。
Ka neme su da laifi a kan laifi; kada ka bar su su sami rabo a cikin cetonka.
28 願他們從生命冊上全被塗去,不要讓他們與義人同被錄取:
Bari a shafe su sarai daga littafin rai kada a kuma lissafta su tare da adalai.
29 天主,我既貧乏而又憂苦,願您的救助賜給我衛護:
Ina cikin zafi da kuma azaba; bari cetonka, ya Allah, yă tsare ni.
30 我要用詩歌讚美天主的名號,並要用感恩的心給天主增耀:
Zan yabe sunan Allah cikin waƙa in kuma ɗaukaka shi tare wurin yin godiya.
Wannan zai gamshi Ubangiji fiye da saniya, fiye da bijimi da ƙahoninsa da kuma kofatansa.
32 卑微的人們,您們要觀看,並要喜慶,尋求天主的人,您們的心必要興奮,
Matalauta za su gani su kuma yi murna, ku da kuke neman Allah, bari zukatanku su rayu!
33 因為對貧苦的人,上主常予俯聽;對他的俘虜,他決不會看輕。
Ubangiji yakan ji masu bukata ba ya kuwa ƙyale kamammun mutanensa.
34 願上天下地都歌頌讚美他,海洋和一切水族都稱揚他!
Bari sama da ƙasa su yabe shi, tekuna da dukan abin da yake motsi a cikinsu,
35 因為天主要拯救熙雍,建造猶大的城池:使他的僕人住在那裏,並佔有作基地。
gama Allah zai cece Sihiyona yă sāke gina biranen Yahuda. Sa’an nan mutane za su zauna a can su mallake ta,
36 他僕人的後裔將要承繼此邑,愛慕他名的人也要住在這裏。
’ya’yan bayinsa za su gāje ta, waɗanda kuma suna ƙaunar sunansa za su zauna a can.