< 馬太福音 4 >

1 那時,耶穌被聖神領往曠野,為受魔鬼的試探。
Sa'an nan Ruhu ya bi da Yesu zuwa cikin jeji, domin Ibilis ya gwada shi.
2 衪四十天四十夜禁食,後來就餓了。
Da ya yi azumi kwana arba'in dare da rana, daga baya yunwa ta kama shi.
3 試探者就前來對衪說:「你若是天主子,就命這些石頭變成餅吧!
Sai mai jarabtar nan ya zo, ya ce masa, “Idan kai Dan Allah ne, ka umarci duwatsun nan su zama gurasa.”
4 衪回答說:「經上記載:『人生活不只靠餅,而也靠天主口中所發的一切言語。』」
Amma Yesu ya amsa ya ce masa, “A rubuce yake cewa, 'Ba da gurasa kadai mutum zai rayu ba, sai dai da kowace magana da ta ke fitowa daga wurin Allah.'''
5 那時,魔鬼引衪到了聖城,把衪立在聖殿頂上,
Sa'an nan Ibilis ya kai shi tsattsarkan birni ya dora shi can kan kololuwar ginin haikali,
6 對衪說:「你若是天主子,就跳下去,因經上記載:『衪為你吩咐了自己的天使,他們要用手托著你,免得你的腳碰在石頭上。』」
ya ce masa, “In kai Dan Allah ne, to dira kasa. Domin a rubuce yake cewa, 'Zai ba mala'ikunsa umarni game da kai,' kuma, 'Za su daga ka da hannuwansu, domin kada ka yi tuntube da dutse.'''
7 耶穌對他說:「經上又記載:『你不可試探上主,你的天主!』」
Yesu ya ce masa, “kuma a rubuce yake, 'Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.'''
8 魔鬼又把衪帶到一座極高的山頂上,將世上的一切國度及其榮華指給衪看
Kuma, sai Ibilis ya kai shi kan wani dutse mai tsawo kwarai, ya nuna masa dukan mulkokin duniya da darajarsu.
9 對衪說:「吧趴俯伏朝拜我,我必把這一切交給你。」
Ya ce masa, “Dukan wadannan zan baka idan ka rusuna ka yi mani sujada.''
10 那時,耶穌就對他說:「去吧! 撒殫!因為經上記載:『你要朝拜上主,你的天主,唯獨事奉衪!』」
Sai Yesu ya ce masa, “Tafi daga nan, Shaidan! Domin a rubuce yake, 'Ka yi wa Ubangiji Allahnka sujada, shi kadai za ka bauta wa.'''
11 於是魔鬼離開了衪,就有天有使前來瑟拉芬衪。
Sa'an nan Ibilis ya rabu da shi, sai kuma mala'iku suka zo suka yi masa hidima.
12 耶穌聽到若翰被監以後,就退避到加里肋亞去了;
To, da Yesu ya ji an kama Yahaya, sai ya tashi zuwa kasar Galili.
13 後又離開納匝肋,來住在海邊的葛法翁,即住在則步隆和納斐塔里境內。
Ya bar Nazarat, ya koma Kafarnahum da zama, can bakin tekun Galili, kan iyakar kasar Zabaluna da Naftali.
14 這應驗了依撒依亞先知所說的話:
Wannan ya faru domin a cika fadar annabi Ishaya cewa,
15 『則步隆與納斐塔里地,通海大路,約但河東,外方人的加里肋亞,
“Kasar Zabaluna da kasar Naftali, ta bakin teku, da hayin Kogin Urdun, Galili ta al'ummai!
16 那坐在黑暗中的百姓,看見了浩光;那坐在死亡陰影之地的,為他們出現了光明。』
Mutane mazauna duhu suka ga babban haske, sannan ga wadanda ke zaune a yankin da inuwar mutuwa, haske ya keto masu.”
17 從那時起,耶穌開始宣講說:「你們悔改吧!因為天國來近了。」
Daga lokacin nan, Yesu ya fara wa'azi, yana cewa, “Ku tuba domin mulkin sama ya kusa.”
18 耶穌沿加里肋亞海行走時,看見了兩個兄弟:稱為伯多碌的西滿,和他的兄弟安德肋,在海裏撒網,他們原是漁夫。
Yana tafiya a bakin tekun Galili, sai ya ga wadansu 'yan'uwa biyu, Saminu da ake kira Bitrus, da dan'uwansa Andarawas, suna jefa taru a teku, domin su masunta ne.
19 衪就對他們說:「來,跟隨我!我要使你們成為漁人的漁夫。」
Yesu ya ce masu, “Ku zo, ku biyo ni, zan mai da ku masuntan mutane.”
20 他們立刻捨下網,跟隨了衪。
Nan da nan sai suka bar tarunsu, suka bi shi.
21 衪從那裏再往前行,看見了另外兩個兄弟:載伯德的兒子亞各伯和他的弟弟若望,船上同自己的父親載伯德修理召們的網,召叫了他們
Da Yesu ya ci gaba da tafiya, sai ya ga wadansu mutum biyu, su kuma 'yan'uwa ne, Yakubu dan Zabadi, da dan'uwansa Yahaya, suna cikin jirgi tare da mahaifinsu Zabadi, suna gyaran tarunsu. Sai ya kira su.
22 他們立刻捨下了魚船和自己的父親,跟隨了衪。
Nan take suka bar mahaifinsu da jirgin, suka bi shi.
23 耶穌走遍了全加里肋亞,在他們的會堂內施教,宣講天國的福音,治好民間各種疾病,各種災殃。
Yesu ya zazzaga dukan kasar Galili, yana koyarwa a majami'unsu, yana shelar bisharar mulkin, yana kuma warkar da kowace cuta da rashin lafiya a cikin mutane.
24 衪的名聲傳遍了整個敘利亞。人就把一切有病的、受各種疾病痛苦煎熬的、附魔的、癲癇的,都給衪送來,衪都治好了他們。
Labarinsa ya bazu a cikin dukan kasar Suriya, kuma mutanen suka kakkawo masa dukan marasa lafiya, masu fama da cuta iri iri, da masu shan azaba, da kuma masu aljannu, da masu farfadiya, da shanyayyu. Yesu ya warkar da su.
25 於是有許多群眾從加里肋亞、「十城區」、耶路撒冷、猶太和約但河東岸來跟隨了衪。
Taro masu yawa suka bi shi daga kasar Galili, da Dikafolis, da Urushalima, da kasar Yahudiya, har ma daga hayin Urdun.

< 馬太福音 4 >