< 馬太福音 20 >
1 國好比一個家主,清晨出去為自己的葡萄園僱工人。
Gama mulkin sama yana kama da wani mai gona, wanda ya fita da asuba ya nemi 'yan kwadago da za su yi aiki a gonarsa.
2 他與工人約定一天一個「德納」,就派他們到葡萄園去了。
Bayan sun shirya kudin da zai biya ma'aikata kimanin dinari daya a kowanne yini, sai ya aike su gonarsa suyi aiki.
3 約在第三時辰,又出去,看見另有些人在街上閒站著,
Misalin sa'a ta uku sai ya sake fita, sai ya ga wasu ma'aikata suna tsaye a bakin kasuwa, babu aiki.
4 就對他們說:你們也到我的葡萄園裏去吧!凡照公義該給的,我必給你們。
Sai ya ce masu, 'Kuzo kuyi aiki a gonar, duk abinda ya wajaba, zan ba ku,' Sai suka tafi su yi aikin.
5 他們就去了。約在第六和在第九時辰,他又出去,也照樣做了。
Sai ya sake fita a sa'a ta shida ya kuma sake fita a sa'a ta tara, ya sake yin hakan din.
6 約在第十二時辰,他又出去,看見還有些人站在那裏,就對他們說:為什麼你們站在這裏整天閒著?
Ya kuma sake yin haka a sa'a ta sha daya, da ya fita sai ya ga wasu a tsaye da ba sa yin kome. Sai ya ce masu, 'Me yasa kuke tsaye ba ku yin kome dukan yini?'
7 他們對他說:因為沒有人僱我們。他給他們說:你們也到我的葡萄園裏去吧!
Sai suka ce masa, 'Ai babu wanda ya dauke mu aiki, shi yasa.' Sai ya ce masu, 'ku ma, kuje cikin gonar.
8 到了晚上,葡萄園的主人對他的管事人說:你叫他們來,分給他們工資,由最後的開始,直到最先的。
Da yamma ta yi, sai mai gonar ya ce wa manajansa, 'Ka kira ma'aikatan nan ka biya su hakkin su, amma ka fara da wadanda suka zo a karshe, zuwa na farkon.'
9 那些約在第十一時辰來的人,每人領了一個「德納」。
Sa'adda wadanda suka fara aiki da yamma suka zo, an biya su daidai yadda ake biya a yini.
10 那些最先僱來的,心想自己必會多領,但他們也只領了一個「德納」。
Da wadanda suka fara aiki tun safe suka zo, suna tsammani za a ba su fiye da wadanda sun zo daga baya, amma aka ba kowannensu dinari daya.
Da suka karbi hakkinsu, suka yi gunaguni game da mai gonar.
12 說:這些最後僱的人,不過工作了一個時辰,而你竟把他們與我們這整天受苦受熱的,同等看待。
Suka ce, 'Wadannan da suka zo a karshe, sa'a guda ce kadai suka yi aiki, amma ka ba su daidai da mu, mu da muka yi fama da aiki cikin zafin rana.'
13 他答覆其中的一個說:朋友!我並沒有虧負你,你不是和我議定了一個「德納」嗎?
Amma mai gonar ya amsa wa daya daga cikin su, ya ce, 'Aboki na, ban yi maku laifi ba. Ai mun shirya zan biya ku yadda ake biya a yini, ko ba haka ba?
14 拿你的走吧!我願意給這最後來的和給你的一樣。
Ku karbi abin da ke na ku, ku tafi. Ganin dama ta ne, in ba wadannan da suka zo a karshe daidai da ku.
15 難道不許我拿我所有的財物,行我所願意的嗎?或是因為我好,你就眼紅嗎?
Ashe, ba daidai bane a gare ni, in yi abin da na ga dama da mallaka ta? Ko kishi ne kuke yi saboda kirki na?'
16 這樣,最後的,將成為最先的,最先的將成為最後的。」
Haka yake, na karshe za su zama na farko, na farko kuma su zama na karshe.'' [An kira dayawa, amma kadan ne zababbu].
17 耶穌上耶路撒冷去,暗暗把十二個門徒帶到一邊,在路上對他們說:
Da Yesu zai tafi Urushalima, ya dauki sha-biyun nan a gefe, yayin da suke tafiya, sai ya ce masu,
18 「看,我們上耶路撒冷去,人子要被交於司祭和經師,他們要定的死罪;
“Ku duba fa, zamu tafi Urushalima, kuma za a bada Dan Mutum ga manyan firistoci da marubuta. Za su kuma yanke masa hukuncin kisa,
19 並且要把他給外邦人戲弄、鞭打、釘死;但第二天,他要復活。」
za su kuma bada shi ga al'ummai don suyi masa ba'a, su bulale shi, su kuma gicciye shi. Amma a rana ta uku, za a tada shi.''
20 那時,載伯德兒子的母親,同自己的兒子前來,叩拜耶穌,請求衪一件事。
Sai uwar 'ya'yan Zabadi ta zo wurin Yesu tare da 'ya'yanta. Ta rusuna a gabansa tana neman alfarma a wurinsa.
21 耶穌對她說:「妳要什麼? 」她回答說:「你叫我的這兩個兒子,在你王國內,一個坐在你的右邊,一個坐在你的左邊。」
Yesu ya ce mata, Me kike so in yi maki?'' Sai ta ce masa, ''Ina so ka ba 'ya'yana izinin zama a mulkinka, daya a hannun damanka, daya kuma a hannun hagunka.
22 耶穌回答說:「你們不知道你們所求的是什麼,你們能飲我將要飲的爵嗎? 」他們說:「我們能」
Amma Yesu ya amsa, ya ce, ''Baku san abin da kuke roko ba. Ko zaku iya sha daga cikin kokon da zan sha bada dadewa ba?'' Sai suka ce masa, ''Zamu iya.''
23 耶穌對他們說:「我的爵你們固然要飲,但坐在右邊或左邊,不是我可以給的,而是我父給誰預備了,就給誰。」
Sai ya ce masu, ''In dai kokon nan da zan sha ne, lallai zaku sha. Amma, zama a hannun dama na da kuma hannun hagu na, ba ni ne mai bayarwa ba, amma na wadanda Uba na ya shirya domin su ne.''
Sa'anda sauran almajirai goma suka ji haka, sun yi bacin rai da 'yan'uwan nan biyu.
25 耶穌叫過他們來說:「你們知道:外邦人有首長主宰他們,有大臣管轄他們。
Amma Yesu ya kira su wurin sa, ya ce, ''Kuna sane da cewa, sarakunan al'ummai suna gwada masu mulki, manyan-gari kuma na nuna masu iko.
26 在你們中間卻不可這樣,誰若在你們中願意成為大的,就當作你們的僕役;
Ba zai kasance haka a tsakanin ku ba. A maimakon haka, duk wanda ke da marmari ya zama da girma a tsakanin ku, ya zama baran ku.
Wanda kuma ke da marmari ya zama na farko a cikin ku, ya zama baran ku.
28 就如人子來不是受服,而是服事人,並交出自己的生命,為大眾作贖價。」
Kamar dai yadda Dan mutum bai zo don a bauta masa ba, amma yayi bauta, ya kuma bada ransa fansa domin mutane dayawa.''
Da suka fita daga Yariko, babban taro suka bi shi.
30 有兩個瞎子坐在路旁,聽說耶穌路過,就喊叫說:「主,達味之子,可憐我們吧!」民眾責斥他們,
Suka kuma ga makafi biyu zaune a bakin hanya. Da makafin suka ji cewa Yesu ne ke wucewa, sai suka tada murya suna cewa, ''Ya Ubangiji, Dan Dauda, kayi mana jinkai.''
31 他們不要作聲;他們反而更喊叫說:「主,達味之子,可憐我們吧!」
Amma jama'ar suka tsauta masu, suka ce suyi shiru. Duk da haka, makafin suka kara tada murya fiye da na da, suka ce, ''Ya Ubangiji, Dan Dauda, kayi mana jinkai.''
32 耶穌就站住,叫過他們來,說:「你們願意我給你們做什麼? 」
Sai Yesu ya tsaya cik, ya sa aka kira su, sai ya ce masu, ''Me kuke so in yi maku?''
Sai suka ce masa, Ya Ubangiji, muna so mu sami ganin gari.''
34 耶穌動了慈心,摸了他們的眼睛;他們就立刻看見了,也跟著衪去了。
Sai Yesu yayi juyayi a cikin sa, ya taba idanunsu. Nan da nan, suka sami ganin gari, suka kuma bi shi.