< 馬太福音 15 >

1 時,有法利塞人和經師,從耶路撒冷來到耶穌跟前說:「
Sai wadansu Farisawa da malamai suka zo wurin Yesu daga Urushalima. Su ka ce,
2 你的門徒為什麼違犯先人的傳受?他們吃飯時竟不洗手。」
“Meyasa almajiranka suke karya al'adar dattawa? Don ba su wanke hannayen su kafin su ci abinci.”
3 耶穌回答他們說:「你們為什麼為了你們的傳受,而惟犯天主的戒命呢?
Yesu ya amsa masu ya ce, “Kuma don me ku ke karya dokar Allah saboda al'adunku?
4 天主曾說過:『你要孝敬父親和父母。』又說過:『咒罵父親和母親的,應處以死行刑。』
Domin Allah ya ce, 'Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka; 'Shi wanda ya yi muguwar magana ga mahaifinsa ko mahaifiyarsa, lallai zai mutu.
5 你們卻說:誰若對父親或母親說:我所能供養你的,已成了獻儀;
Amma kun ce, “Duk wanda ya ce wa mahaifinsa ko mahaifiyarsa, “Kowanne taimako da za ka samu daga gare ni yanzu baiko ne ga Allah,'”
6 他就不必再孝敬父親或母親了。你們就為了你們的傳受,廢棄了天主的話。
wannan mutum ba ya bukatar ya girmama mahaifinsa. Ta wannan hanya kun maida maganar Allah wofi saboda al'adunku.
7 假善人哪!依撒意亞論你們預言的真好,他說:『
Ku munafukai, daidai ne Ishaya ya yi annabci akan ku da ya ce,
8 這民族用嘴唇尊敬我,他們的心卻是遠離我;
“Wadannan mutane girmama ni da baki kawai suke yi, amma zukatansu nesa suke da ni.
9 他更們恭敬我也是假的,因為他們講授的教義是人的規律。』」
Suna mani sujada a banza, domin suna koyar da dokokin mutane a matsayin rukunansu.”
10 耶穌便叫群眾來,對他們說:「你門聽,且要明白:
Sai ya kira taron mutane zuwa gare shi ya ce masu, “Ku saurara ku fahimta,
11 不是入於口的,纔始人污穢。」
ba abin da ke shiga baki ke kazantar da mutum ba. Sai dai, abin da ke fitowa daga baki, wannan shi ya ke kazantar da mutum.”
12 那時,們徒前來告訴耶穌說:「你知道法利塞人聽了這話,起了反感嗎﹖」
Sai al'majiran suka zo suka ce masa, “Ka san Farisawa ba su ji dadi ba da suka ji maganan nan?”
13 耶穌答說:「任何植物,凡不是我天父所栽種的,必要連根拔除。
Yesu ya amsa ya ce, “Kowace shuka wadda ba Ubana na sama ya shuka ba za a tuge ta.
14 由他們罷!他們是瞎子,且是瞎子的領路人;但若瞎子領瞎子兩人必要掉在坑裏。」
Ku kyale su kawai, su makafin jagora ne. In makaho ya ja wa wani makaho gora dukan su za su fada rami.”
15 伯多錄遂應聲對耶蘇說:「請你為我們講解這個比喻罷!」
Bitrus ya amsa ya ce wa Yesu, “Ka bayyana wannan misali a garemu,”
16 耶穌說:「連你們也不明白嗎?
Yesu ya ce, “Ku ma har yanzu ba ku da fahimta?
17 你們不曉得:凡如於口的,先到肚腹內,然後排泄到廁所裏去嗎?
Ko baku gani ba duk abin da ke shiga baki zuwa ciki ta haka yake fita zuwa salga?
18 但那從口裏出來的,都是由心裏發出來的,這些纔始人污穢,
Amma abubuwan da ke fita daga baki suna fitowa ne daga zuciya. Su ne abubuwan da ke kazantar da mutum.
19 因為由心裏發出來的是惡念、兄殺、姦淫、邪淫、盜竊、妄證、誹謗。
Domin daga zuciya mugayen tunani suke fitowa, kisan kai, zina, fasikanci, sata, shaidar zur, da zage-zage.
20 這些都使人污穢,至於不洗手吃飯,並不能使人污穢。」
Wadannan su ne abubuwan da ke kazantar da mutum. Amma ci da rashin wanke hannu baya kazantar da mutum.”
21 耶穌離開那裏,就退往提洛和漆冬一帶去了。
Sai Yesu ya tafi daga nan ya nufi yankin biranen Taya da Sidon.
22 看,有一個客納罕婦人,從那地方出來喊說:「主,達味之子,可憐我罷!我的女兒被魔糾纏的好苦啊!」
Sai wata mace Bakan'aniya ta zo daga wannan yanki. Ta daga murya ta ce,” Ka yi mani jinkai, Ubangiji, Dan Dauda; 'yata tana cikin bakar azaba da aljani.”
23 耶穌卻一句話也不回答她。他的們徒就上前求他說:「打發她走罷!因為她在我們後面不停地喊叫。」
Amma Yesu bai ce mata kome ba. Almajiransa suka zo suka roke shi, suna cewa, “Ka sallame ta, domin tana bin mu da ihu.”
24 耶穌回答說:「我被派遣,只是為了以色列家失迷的羔羊。」
Amma Yesu ya amsa ya ce, “Ba a aike ni gun kowa ba sai dai ga batattun tumakin gidan Isra'ila.”
25 那婦人卻前來叩拜他說:「主,援助我罷!」
Amma ta zo ta durkusa a gabansa, tana cewa, “Ubangiji ka taimake ni.”
26 耶穌回答說:「拿兒女的餅扔給小狗,是不對的。」
Ya amsa ya ce, “Ba daidai bane a dauki gurasar yara a jefa wa kananan karnuka.
27 但她說:「是啊!主,可是小狗也吃主人桌子上掉下來的碎屑。」
Ta ce, “I, Ubangiji, amma ko kananan karnuka suna cin barbashin da ke fadowa daga teburin maigida.”
28 耶穌回答她說:「啊! 婦人,妳的信德真大,就如妳所願望的,給妳成就罷!」從那時刻起,她的女兒就痊愈了。
Sai Yesu ya amsa ya ce mata, “Mace, bangaskiyarki tana da girma. Bari ya zamar maki yadda ki ke so.”'Yarta ta warke a lokacin.
29 耶穌離開了那裏,來到加里肋亞海岸,上了山坐在那裏。
Yesu ya bar wurin ya tafi kusa da tekun Galili. Sai ya hau tudu ya zauna a can.
30 於是有許多群眾帶著瘸子、瞎子、啞吧、和許多其他的病人來到耶穌跟前,把他們放在他的足前,他便治好了他們;
Taro mai yawa suka zo gunsa. Suka kawo masa guragu, makafi, bebaye da nakasassun mutane da yawa, da wadansu marasa lafiya. Suka kawo su gaban Yesu, sai ya warkar da su.
31 致始群眾見到啞吧說話,殘廢康復,瘸子行走,瞎子看見,都大為驚奇,頌揚以色列的天主。
Don haka mutane da yawa suka yi mamaki a lokacin da suka ga bebaye suna magana, nakasassu sun warke, guragu suna tafiya, makafi suna gani. Sai suka daukaka Allah na Isra'ila.
32 耶穌將自己的們徒召來說:「我很憐憫這群眾,因為他們同我在一起以經三天,也沒有什麼可吃的;我不願遣散他們空著肚子回去,怕他們在路上昏倒。」
Yesu ya kira almajiransa zuwa gun sa sai ya ce, “Ina jin tausayin taron, sun kasance tare da ni kwana uku ke nan kuma ba su da abin da za su ci. Bana so in sallame su ba tare da sun ci abinci ba, domin kada su suma a hanya.”
33 們徒對他說:「在荒野裏我們從那裏得這麼多的餅,使這麼多的群眾吃飽呢?」
Almajiran suka ce masa, “A ina zamu sami isasshiyar gurasa a wannan wuri da babu kowa har ta ishi babban taron nan.”
34 耶穌對他們說:「你們有多少餅 ?」他們說:「七個,還有幾條小魚。」
Yesu ya ce masu, “Gurasa nawa ku ke da ita?” Suka ce, “Bakwai da 'yan kifi marasa yawa.”
35 耶穌就吩咐群眾坐在地上,
Sai Yesu ya umarci taron su zauna a kasa.
36 拿起那七個餅和魚來,祝謝了,擘開,遞給們徒;門徒再分給群眾。
Ya dauki gurasar nan bakwai da kifin, bayan ya yi godiya, ya kakkarya gurasar ya bada ita ga almajiran Sai almajiran suka ba taron.
37 眾人都吃了,也都飽了,把剩下的碎塊收集了滿滿七籃子。
Jama'a duka suka ci suka koshi. Suka tattara gutsattsarin abincin da ya rage, kwando bakwai cike.
38 吃的人數,除婦女和孩子外,約有四千人。
Wadanda suka ci su dubu hudu ne maza, banda mata da yara.
39 耶穌遣散了群眾,就上船,來到瑪加丹境內。
Sai Yesu ya sallami taron ya shiga cikin jirgin ruwa ya tafi yankin Magadan.

< 馬太福音 15 >