< 馬可福音 5 >
Suka ƙetare tafkin suka je yankin Gerasenawa.
2 耶穌一下船,即刻有一個附邪魔的人,從墳墓裏出來,迎著他走來,
Da Yesu ya sauka daga jirgin ruwa, sai wani mutum mai mugun ruhu ya fito daga kaburbura, ya tarye shi.
3 原來那人居住在墳墓裏,再沒有人能捆住他,就是用鎖鍊也不能,
Wannan mutumin ya mai da kaburbura gidansa. Kuma ba wanda ya iya daure shi, ko da sarƙa ma.
4 因為人屢次用腳鐐和鎖鍊將他捆縛,他卻將鎖鍊掙斷,將腳鐐弄碎,沒有人能制服他。
Gama an sha daure shi hannu da ƙafa da sarƙa, amma yakan tsintsinke sarƙar, yă kuma karye ƙarafan da suke ƙafafunsa. Ba wanda yake da ƙarfin da zai iya yă riƙe shi.
Dare da rana, sai yă dinga kuka yana ƙuƙƙuje jikinsa da duwatsu a cikin kaburbura da kan tuddai.
Da ya hangi Yesu daga nesa, sai ya ruga da gudu, ya zo ya durƙusa a gabansa.
7 大聲喊說:「至高天主之子耶穌,我與你有什麼相干﹖我因著天主誓求你,不要苦害我!」
Ya yi ihu da babbar murya ya ce, “Ina ruwanka da ni Yesu, Ɗan Allah Mafi Ɗaukaka? Ka rantse da Allah cewa ba za ka ba ni azaba ba!”
Gama Yesu ya riga ya ce masa, “Ka fita daga jikin mutumin nan, kai mugun ruhu!”
9 耶穌問他說:「你名叫什麼﹖」他回答說:「我名叫『軍旅』,因為我們眾多。」
Sai Yesu ya tambaye shi ya ce, “Mene ne sunanka?” Sai ya amsa ya ce, “Sunana Lejiyon, wato, ‘Tuli,’ domin muna da yawa.”
Sai ya yi ta roƙon Yesu, kada yă kore su daga wurin.
A kan tudun da yake nan kusa kuwa, akwai wani babban garken aladu, suna kiwo.
12 他們懇求耶穌說:「請打發我們到那豬群,好讓我們進入牠們內。」
Sai aljanun suka roƙi Yesu, suka ce, “Tura mu cikin aladun nan, ka bari mu shiga cikinsu.”
13 耶穌准許了他們;邪魔就出來,進入了豬內。那群豬約有二千,便從山崖上直衝到海裏,在海裏淹死了。
Ya kuwa yarda musu, sai mugayen ruhohin suka fita suka shiga cikin aladun. Garken kuwa, yana da kusan aladu dubu biyu, suka gangara daga kan tudun zuwa cikin tafkin, suka nutse.
14 放豬的人就逃去,到城裏和鄉間傳報開了;人都出來看是發生了什麼事。
Masu kiwon aladun kuwa suka ruga da gudu zuwa cikin gari da ƙauyuka, suka ba da wannan labari. Sai mutanen suka fito, domin su ga abin da ya faru.
15 他們來到耶穌跟前,看見那個附魔的人,即為「軍旅」所附的人,坐在那裏,穿著衣服,神志清醒,就害怕起來。
Da suka kai wajen Yesu, sai suka ga mutumin da dā yake da tulin aljanun yana zaune a wurin, sanye da tufafi kuma cikin hankalinsa, sai suka ji tsoro.
16 看見的人就把附魔的人所遇到的事,和那群豬的事,都給他們逑說了。
Waɗanda suka ga abin da ya faru, suka ba da labarin abin da ya faru da mai aljanun, da kuma aladun.
Sai mutane suka fara roƙon Yesu yă bar yankinsu.
18 當耶穌上船時,那曾附過魔的人,懇求耶穌讓他同耶穌在一起。
Yesu yana kan shiga cikin jirgin ruwa ke nan, sai mutumin da dā yake da aljanun ya roƙa yă bi shi.
19 耶穌沒有允許他,但對他說:「你回家,到你的親屬那裏,給他們傳逑上主為你作了何等大事,怎樣憐憫了你。」
Yesu bai yardar masa ba, amma ya ce, “Ka tafi gida wurin iyalinka, ka gaya musu babban alherin da Ubangiji ya yi maka, da yadda ya yi maka jinƙai.”
20 那人就走了,在十城區開始傳揚耶穌為他所作的何等大事,眾人都驚奇不已。
Sai mutumin ya tafi, ya yi ta ba da labari a cikin Dekafolis a kan babban alherin da Yesu ya yi masa. Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
21 耶穌乘船又渡回對岸,有大夥群眾聚集在他周圍;他遂留在海濱。
Da Yesu ya sāke ƙetarewa cikin jirgin ruwa zuwa ɗaya hayen tafkin, sai taro mai yawa ya taru kewaye da shi yayinda yake a bakin tafkin.
22 那時,來了一個會堂長名叫雅依洛,一見耶穌,就跪伏在他腳前,
Sai ɗaya a cikin masu mulkin majami’a, wanda ake kira Yayirus ya zo wurin. Da ganin Yesu, sai ya durƙusa a gabansa,
23 懇切求他說:「我的小女兒快要死了,請你來,給他覆手,叫她得救回生。」
ya roƙe shi da gaske ya ce, “Ƙaramar diyata tana bakin mutuwa. In ka yarda, ka zo ka ɗibiya hannunka a kanta, domin ta warke, ta kuma rayu.”
24 耶穌就同他去了。有一大群人跟隨著他,擁擠著他。
Sai Yesu ya tafi tare da shi. Babban taron kuma ya bi shi, suna ta matsinsa a kowane gefe.
A can kuwa akwai wata mace, wadda ta yi shekaru goma sha biyu tana zub da jini.
26 她在許多醫生手裏,受了許多痛苦,花盡了自己所有的一切,不但沒有見效,反而病勢更加重了。
Ta kuma sha wahala ƙwarai a hannun likitoci da yawa, har ta kashe duk abin da take da shi, amma maimakon samun sauƙi, sai ciwon ya ƙara muni.
27 她聽了有關耶穌的傳說,便來到人群中,從後邊摸了耶穌的衣裳,
Da ta ji labarin Yesu, sai ta zo ta bayansa, a cikin taron, ta taɓa rigarsa,
28 因為她心裏想:「我只要一摸他的衣裳,必然會好的。」
domin ta yi tunani cewa, “Ko da rigunarsa ma na taɓa, zan warke.”
29 她的血源立刻涸竭了,並且覺得身上的疾病也好了。
Nan da take, zub da jininta ya tsaya, sai ta ji a jikinta ta rabu da shan wahalarta.
30 耶穌立時覺得有一種能力從自己身上出去,就在人群中回過頭來說:「誰摸了我的衣裳﹖」
Nan da nan Yesu ya gane cewa, iko ya fita daga gare shi. Sai ya juya a cikin taron ya yi tambaya, “Wa ya taɓa rigata?”
31 他的門徒向他說:「你看! 群眾四面擁擠著你,你還問:誰摸了我﹖」
Sai almajiransa suka ce, “Kana ganin mutane suna matsinka, duk da haka kana tambaya, ‘Wa ya taɓa ni?’”
Amma Yesu ya ci gaba da dubawa don yă ga wa ya taɓa shi.
33 那婦人明知在自己身上所成的事,就戰戰兢兢地前來,跪伏在耶穌前,把實情完全告訴他。
Matar, da yake ta san abin da ya faru da ita, sai ta zo ta durƙusa a gabansa, da tsoro da rawan jiki, ta kuma gaya masa dukan abin da ya faru.
34 耶穌便向他她說:「女兒,你的信德救了你,平安去罷! 你的疾病必得痊癒!」
Sai ya ce mata, “Diyata, bangaskiyarki ta warkar da ke. Ki sauka lafiya, kin kuma rabu da dukan wahalarki.”
35 他還說話的時候,有人從會堂長家裏來,說:「你的女兒死了,你還來煩勞師傅做什麼﹖」
Yayinda Yesu yana cikin magana, sai waɗansu mutane daga gidan Yayirus, mai mulkin majami’a, suka zo suka ce, “Diyarka ta rasu. Kada ma ka wahal da Malam.”
36 耶穌聽所說的話,就給會堂長說:「不要怕,祇管信。」
Yesu bai kula da abin da suka faɗa ba, sai ya ce wa mai mulkin majami’ar, “Kada ka ji tsoro, ka gaskata kawai.”
37 除伯多祿、雅各伯和雅各伯的弟弟若望外,他沒有讓任何人跟他去。
Bai bar kowa ya bi shi ba, sai Bitrus, Yaƙub da Yohanna ɗan’uwan Yaƙub.
38 他們到了會堂長的家裏,耶穌看見群眾非常喧噪:有的哭泣,有的哀號,
Da suka iso gidan mai mulkin majami’ar, sai Yesu ya ga ana hayaniya, mutane suna kuka da kururuwa.
39 便進去,給他們說:「你們為什麼喧噪哭泣呢﹖小女孩並沒有死, 祇是睡著了!」
Sai ya shiga ciki, ya ce musu, “Mene ne dalilin wannan hayaniya da kuka? Yarinyar ba mutuwa ne ta yi ba, barci take yi.”
40 他們都譏笑他。他卻把眾人趕出去,帶著小女孩的父親和母親,及同他在一起的人,進了小女孩所在的地方。
Sai suka yi masa dariya. Bayan ya fitar da su duk waje, sai ya ɗauki mahaifin da mahaifiyar yarinyar tare da almajiran da suke tare da shi, suka shiga inda yarinyar take.
41 他拿起小女孩的手,對她說:「塔里塔,古木!」意思是:「女孩子,我命妳起來!」
Sai ya kama hannunta ya ce mata, “Talita kum!” (Wato, “Ƙaramar yarinya, na ce miki, tashi!”).
42 那女孩子就立刻起來行走,原來她已十二歲了;他們都驚訝得目瞪口呆。
Nan da nan, sai yarinyar ta tashi ta yi tafiya (shekarunta goma sha biyu ne). Saboda wannan, suka yi mamaki ƙwarai.
43 耶穌卻嚴厲命令他們,不要叫任何人知道這件事;又吩咐給女孩子吃的。
Sai ya ba da umarni mai tsanani, kada kowa yă san kome game da wannan. Sai ya ce musu, su ba ta wani abu tă ci.