< 馬可福音 3 >

1 耶穌又進了會堂,在那裏有一個人,他的一隻手枯乾了。
Wani lokaci, da ya sāke shiga majami’a, sai ga wani mutum mai shanyayyen hannu.
2 他們窺察耶穌是否在安息日治好那人,好去控告他。
Waɗansu daga cikin mutane suna neman dalilin zargin Yesu, sai suka zuba masa ido, su ga ko zai warkar da shi a ranar Asabbaci.
3 耶穌對那有一隻手枯了的人說:「起來,站在中間! 」
Yesu ya ce wa mutumin mai shanyayyen hannun, “Tashi ka tsaya a gaban kowa.”
4 遂對他們說:「安息日許行善呢,或作惡呢﹖許救命呢,或害命呢﹖」他們一聲不響。
Sai Yesu ya tambaye su ya ce, “Me ya kamata a yi bisa ga doka, a ranar Asabbaci, a aikata alheri, ko a aikata mugunta, a ceci rai, ko a yi kisa?” Amma suka yi shiru.
5 耶穌遂含怒環視他們,見他們的心硬而悲傷,就對那人說:「伸出手來! 」他一伸,他的手就復了原。
Sai ya kalle su da fushi, don taurin zuciyarsu ya ɓata masa rai sosai. Sai ya ce wa mutumin, “Miƙo hannunka.” Sai ya miƙa, hannunsa kuwa ya koma lafiyayye.
6 法利賽人一出去,立刻便與黑落德黨人作陷害耶穌的商討,為除滅他。
Sai Farisiyawa suka fita, suka fara ƙulla shawara da mutanen Hiridus yadda za su kashe Yesu.
7 那時,耶穌同自己的門徒退到海邊去,有許多民眾從加里肋亞跟隨了來,並有從猶太、
Yesu da almajiransa suka janye zuwa tafkin, taro mai yawa kuwa daga Galili ya bi shi.
8 耶路撒冷、依杜默雅、約旦河彼岸、提洛和漆冬一帶地方的許多群眾,聽說他所做的一切事,都來到他跟前。
Mutane da yawa daga Yahudiya, da Urushalima, da Edom, da kuma yankunan da suke ƙetaren Urdun, da kewayen Taya, da Sidon suka zo wurinsa, don sun ji dukan abubuwan da yake yi.
9 因為人多,他遂吩咐他的門徒,為自己備好一隻小船,免得人擁擠他。
Saboda taron, sai ya ce wa almajiransa su shirya masa ƙaramin jirgin ruwa, don kada mutane su matse shi.
10 因為他治好了許多人,所以,凡有病的人都向他湧來,要觸摸他。
Gama ya warkar da mutane da yawa, masu cututtuka suka yi ta ƙoƙarin zuwa gaba, don su taɓa shi.
11 邪魔一見了他,就俯伏在他面前,喊說:「你是天主子。」
Duk sa’ad da mugayen ruhohi suka gan shi, sai fāɗi a gabansa, su ɗaga murya, su ce, “Kai Ɗan Allah ne.”
12 他卻嚴厲責斥他們,不要把他顯露出來。
Amma yakan tsawata musu, kada su shaida ko wane ne shi.
13 隨後,耶穌上了山,把自己所想要的人召來,他們便來到他面前。
Yesu ya hau gefen wani dutse, ya kira waɗanda yake so, suka kuma zo wurinsa.
14 他就選定了十二人,為同他常在一起,並為派遣他們去宣講,
Ya naɗa sha biyu, ya kira su manzanni don su kasance tare da shi, domin kuma yă aike su yin wa’azi,
15 且具有驅魔的權柄。
don kuma su sami ikon fitar da aljanu.
16 他選定了這十二人:西滿給他取名叫伯多祿,
Ga sha biyun da ya naɗa. Siman (wanda ya ba shi suna Bitrus);
17 載伯德的兒子雅各伯和雅各伯的弟弟若望,並為他們起名叫「波納爾革」,就是「雷霆之子」,
Yaƙub ɗan Zebedi da kuma ɗan’uwansa Yohanna (ga waɗannan kuwa ya sa musu suna Buwarnajis, wato, “’ya’yan tsawa”);
18 安德肋、斐理伯、巴爾多祿茂、瑪竇、多默、阿爾斐的兒子雅各伯,達陡和熱誠者西滿,
Andarawus, Filibus, Bartolomeyu, Mattiyu, Toma, Yaƙub ɗan Alfayus, Taddayus, Siman wanda ake kira Zilot,
19 並猶達斯依斯加略,他是負責耶穌者。
da kuma Yahuda Iskariyot, wanda ya bashe Yesu.
20 耶穌到了家,群眾又聚集了來,以致他們連飯都不能吃。
Sai Yesu ya shiga wani gida, taro kuma ya sāke haɗuwa, har shi da almajiransa ma ba su sami damar cin abinci ba.
21 他的人聽說了,便出來要抓住他,因為他們說:「他瘋了!」
Da’yan’uwansa suka sami wannan labari, sai suka tafi don su dawo da shi, suna cewa, “Ai, ya haukace.”
22 從耶路撒冷下來的經師們說:「他賴魔王驅魔。」
Malaman dokokin da suka zo daga Urushalima suka ce, “Ai, yana da Be’elzebub! Da ikon sarkin aljanu yake fitar da aljanu.”
23 耶穌遂把他們叫來,用比喻向他們說:「撒殫怎能驅逐撒殫呢﹖」
Sai Yesu ya kira su, ya yi musu magana da misalai ya ce, “Yaya Shaiɗan zai fitar da Shaiɗan?
24 一國若自相紛爭,那國就不能存立;
In mulki yana gāba da kansa, wannan mulki ba zai tsaya ba.
25 一家若自相紛爭,那家也將不能存立。
In gida yana gāba da kansa, wannan gida ba zai tsaya ba.
26 撒殫若起來自相攻擊紛爭,也就不能存立,必要滅亡。
In kuwa Shaiɗan yana gāba da kansa, ya kuma rabu biyu, ba zai tsaya ba, ƙarshensa ya zo ke nan.
27 決沒有人能進入壯士的家,搶劫他的家俱的,除非先把那壯士捆起來,然後搶劫他的家。
Tabbatacce, ba mai shiga gidan mai ƙarfi yă kwashe dukiyarsa, sai bayan ya daure mai ƙarfin, sa’an nan zai iya yin fashin gidansa.
28 我實在告訴你們:世人的一切罪惡,連所說的任何褻瀆的話,都可得赦免;
Gaskiya nake gaya muku, za a gafarta duk zunubai da kuma saɓon mutane suka yi.
29 但誰若褻瀆了聖神,永遠不得赦免,而是永久罪惡的犯人。」 (aiōn g165, aiōnios g166)
Amma duk wanda ya saɓi Ruhu Mai Tsarki, ba za a taɓa gafara masa ba. Ya aikata madawwamin zunubi ke nan.” (aiōn g165, aiōnios g166)
30 耶穌說這話,是因為他們說:「他附有邪魔。」
Ya faɗi haka domin suna cewa, “Yana da mugun ruhu.”
31 耶穌的母親和他的兄弟們來了,站在外邊,派人到他跟前去叫他。
Sai mahaifiyar Yesu tare da’yan’uwansa suka iso. Suna tsaye a waje, sai suka aiki wani ciki yă kira shi.
32 那時,群眾正圍著他坐著,有人給他說:「看,你的母親和你的兄弟在外邊找你。」
Taron yana zaune kewaye da shi, sai suka ce masa, “Mahaifiyarka da’yan’uwanka suna waje, suna nemanka.”
33 耶穌回答他們說:「誰是我的母親和我的兄弟﹖」
Ya yi tambaya ya ce, “Su wane ne mahaifiyata, da’yan’uwana?”
34 遂環視他週圍坐著的人說:「看,我的母親和我的兄弟!
Sai ya dubi waɗanda suke zaune kewaye da shi ya ce, “Ga mahaifiyata da’yan’uwana!
35 因為誰奉行天主的旨意,他就是我的兄弟、姊妹和母親。」
Duk wanda yake aikata nufin Allah, shi ne ɗan’uwana, da’yar’uwata, da kuma mahaifiyata.”

< 馬可福音 3 >