< 路加福音 8 >
1 以後,耶穌走遍各城各村講道,宣傳天主國的喜訊,同祂在一起的有那十二們徒,
Bayan haka, Yesu da almajiransa goma sha biyu, su ka zagaya cikin birane da kauyuka dabam dabam, suna wa'azi da shelar labari mai dadi game da mulkin Allah,
2 還有幾個曾附過惡魔或患病而得治好的婦女,有號稱瑪達肋納的瑪利亞,從她身上趕出了七個魔鬼;
mata da yawa wadanda Yesu ya warkar daga aljanu da cututtuka iri iri suna tafiya tare da su. A cikinsu akwai Maryamu wadda a ke ce da ita Magadaliya, wadda ya fitar da aljanu bakwai daga cikinta,
3 還有約安納,即黑落德的家宰雇撒的妻子,又有蘇撒納;還有別的許多婦女,她們都用自己的財產資助他們。
da Yuwana matar Kuza wakilin Hirudus, da Suzanatu da kuma wasu mata da yawa. Daga abin hannunsu suka tanada masu.
4 那時,有大夥群眾聚集了來,並有從各城來到耶穌跟前的,祂就用比喻說:
Wata rana aka tara taron mutane da yawa, saboda mutane su na zuwa daga birane da yawa domin su ga Yesu. Ya yi magana dasu cikin misali.
5 「有一個撒種子的,出去撒種子;他撒的時候,有的落在路在路旁,就被踐踏了,並有天的飛鳥把它吃了。
“Wani mai shuka ya tafi domin ya shuka iri. Sa'adda ya ke yafa iri, wadansu iri suka fada a kan hanya. Sai mutane suka tattake su, tsuntsaye kuma suka tsince wadansu suka cinye.
6 有的落在路在石頭上,一長起來,就乾枯了,因為沒有濕氣。
Wadansu kuma suka fada a kan duwatsu inda babu kasa da yawa. Da suka tsaro suka fara girma, sai nan da nan suka bushe saboda babu laima a wurin.
7 有的落在荊棘中,荊棘同它一起畏起來,把它窒息了。
Wadansu irin kuma suka fada inda yake da kayayuwa. Tsiretsiren kayayuwan suka fito tare da irin da aka shuka, suka shake su yadda basu iya yin girma ba.
8 又有的落在好地裏,長起來,結了百倍的果實。」祂說完這些話,就高呼說:「有耳聽的,就聽吧! 」
Amma wadansu irin suka fada a kan kasa mai kyau, suka yi girma sosai suka ba da anfani da yawa, har rubi dari.” Bayan da Yesu ya fadi wadannan abubuwan, sai ya yi kira gare su, “Duk mai kunnen ji, bari ya ji.”
Sai almajiran Yesu suka tambaye shi ya gaya ma su ma'anar labarin.
10 祂說:「天主國的奧秘,是給你們知道;對於其餘的人,就用比喻,使那看的,卻看不見,聽的,卻聽不懂。
ya ce da su, “Ku aka ba dama ku gane boyayyun abubuwa, na mulkin Allah. Amma ga sauran mutane ina yi masu magana cikin misalai, 'Domin ko da sun gani ba za su gane ba, kuma ko da sun ji ba za su fahimta ba.”
To ga ma'anar misalin. Irin shi ne maganar Allah.
12 那些在路旁的,是指那人聽了,隨後就有鬼來到,從他們心中把那話奪去,使他們不致信從而得救。
Irin da ya fada a kan hanya sune mutanen da suka ji maganar Allah amma daga baya sai shedan ya zo ya dauke maganar daga cikin hankulansu, domin kada su bada gaskiya su tsira.
13 那在石頭上的,是指那些人,他們聽的時候,高興的接受那話,但這些人沒有根,暫時相信,一到試探的時候,就退避了。
Sa'annan, wadanda suka fada kan duwatsu sune mutanen da, da zarar sun ji maganar, sukan karbe ta da murna, amma ba su da sauyu; su kan bada gaskiya na dan lokaci kadan kawai, da zaran gwaji ya same su sai su ridda.
14 那落在荊棘中的,是指那些聽了的人,還在中途就被掛慮、錢財及生活的逸樂所蒙蔽,沒有結出成熟的果實。
Irin da suka fada cikin kayayuwa, sune mutanen da suka ji maganar, amma da suka ci gaba da rayuwa, sai suka bari matsalolin rayuwa kamar dukiya da jin dadin rayuwa suka fi karfinsu, sai ya zama ba su iya bada 'ya'yan da suka yi girma ba.
15 那在好地裏的,是指那些以善良和誠實的心傾聽的人,他們把這話保存起來,以堅忍結出果實。
Amma irin da suka fada a kan kasa mai kyau, wadannan sune mutanen da suka ji maganar, suka karbe ta da gaskiya da zuciya daya, sun rike ta kam-kam, suna jimrewa wurin ba da 'ya'ya.
16 沒有人點上燈,用器皿遮蓋住,或放在床底下的,而是放在燈台上,為叫進來的人看見光明。
Ba mai kunna fitila, ya rufe ta da kasko, ko su sa ta a karkashin gado. Amma sai a sa ta a wurin zaman ta domin duk wanda ya shigo ya iya ganin hasken ta.
17 因為沒有隱藏的事,不成為顯露的;沒有秘密的事,不被知道而公開出來的。
Babu abin da yake a boye wanda ba za a tone shi ba, ko wani asiri da ba za ya fito fili a san shi ba.
18 所以,你們要留心要怎樣聽;因為凡有的,還要給他,凡沒有的,連他自以為有的,也要從他奪去。」
Ku yi hankali da yadda kuke ji, domin duk mai abu, shi za a kara wa, kuma duk mara abu, dan kadan da yake tunani yana da shi ma, za a dauke.”
19 耶穌的母親和兄弟到祂這裏來了,因為人多,不能與祂相會。
Sai mahafiyar Yesu da 'yan'uwansa, su ka zo wurinsa, amma ba su iya zuwa ko kusa da shi ba saboda taron jama'a.
20 有人告訴祂說:「你的母親和你的兄弟站在在外邊,願意見你。」
Sai wani ya gaya masa, “Ga mahaifiyarka da 'yan'uwanka, su na tsayuwa a waje, su na son ganin ka.”
21 祂卻回答說:「聽了天主的話而實行的,才是我的母親和兄弟。」
Amma Yesu ya amsa ya ce ma su, “Mahaifiyata da 'yan'uwana sune wadanda suke jin maganar Allah, suke yin biyayya da ita.”
22 有一天,耶穌和們徒上了船,對他們說:「我們渡到湖那去。」他們便開了船。
Wata rana kuma Yesu ya shiga cikin jirgin ruwa, shi da almajiransa. Ya ce masu, “Ina so mu je dayan ketaren tafkin.” Sai su ka fara tafiya domin su ketare tafkin.
23 正在航行時,他睡著了。忽然有狂風降到湖上,進入船中的水,使他們處於危險中。
Amma sa'adda su ke tafiya sai Yesu ya yi barci, sai wata iska mai karfi ta taso cikin tafkin, nan da nan sai jirgin ya fara cika da ruwa, kuma su na cikin hatsari.
24 們徒們前來叫醒耶穌,說:「老師! 老師! 我們要喪亡了! 」祂醒起來,叱責了狂風和波浪,風浪就止息平靜了。
Sai almajiran Yesu su ka zo su ka tashe shi daga barci. Suka ce da shi, “Ya Shugaba! Ya Shugaba! Za mu mutu!” Sai ya tashi ya umarci iskar, sai iskar mai hauka da tumbatsar ruwan sun tsaya tsit.
25 遂對他們說:「你們的信德在那裏? 」他們又害怕又驚奇,彼此說:「這人到底是誰? 因為祂一出命,風和水也都服從祂。」
Daga nan sai ya ce da su, “Ina bangaskiyar ku?” Almajiran suka tsorata suka yi mamakin abin da ya faru nan take. Suka ce wa junansu, “Wanene wannan wanda har zai ba iska da ruwa umarni kuma su yi masa biyayya?”
26 他們航行到革辣撒人的地方,就是加利肋亞的對面。
Suka zo yankin Garasinawa, wanda ke kusa da Gallili.
27 耶穌一上了岸,迎面來了一個那城中附魔的人,他很久不穿衣服,也不住在家裏,而住在墳墓中。
Sa'adda Yesu ya sauka kasa, sai wani mutum daga wannan yankin ya tarbe shi. Wannan mutum kuwa yana da aljanu. Mutumin ya dade ba ya sa tufafi, kuma ba ya zama a gida. Maimakon haka, sai a cikin kabarbura ya ke zama.
28 他一看見耶穌,就喊叫起來,跪伏在祂在面前大聲說:「至高天主之子耶穌,我與你有什麼相干? 我求你不要磨難我! 」
Sa'adda ya ga Yesu, mutumin ya yi ihu da karfi, ya rusuna a gabansa da babban murya ya ce, “Me zan yi da kai, Yesu, Dan Allah Madaukaki? Ina rokonka, kada ka ba ni azaba!”
29 因為祂曾命令邪魔從那人身上出去,原來邪魔已多次抓住他,他曾被鐵鏈和腳鐐捆縳起來,被看管著;他卻掙斷鐵鏈,被魔鬼趕到荒野中。
Domin Yesu ya umarci aljanun su fita daga cikinsa, domin sau da dama aljanun sukan kama shi. Ko an daure mutumin da sarkoki an kuma tsare shi, yakan tsuttsunke su, kazaman ruhohin sukan kora shi cikin jeji.
30 耶穌問他說:「你叫什麼名字? 」他說:「軍旅。」因為有許多魔鬼進入了他身內。
Sa'annan Yesu ya tambaye shi, “Yaya sunanka?” Sai ya ba da amsa, “Suna na dubbai.” Ya ce haka ne domin aljanu da yawa sun shiga wannan mutum.
31 魔鬼求耶穌,不要命他們到深淵中去。 (Abyssos )
Aljanun suka yi ta rokon Yesu kada ya ummarce su su shiga cikin rami mai zurfi. (Abyssos )
32 在那裡有一大群豬在山上牧放著,魔鬼就請求耶穌許他們進入那些豬內;耶穌准許了他們。
Akwai babban garken aladu su na kiwo a kan tsauni kusa da wurin. Aljanun suka roki Yesu da ya barsu su shiga cikin aladun, shi kuwa ya yarda masu.
33 於是,從那人身上出去,進入豬內,那群豬就從山崖上直衝到湖裏淹死了。
Aljanun suka bar mutumin suka shiga cikin aladun, sai garken aladun suka gangara kwari suka fada cikin tafkin, suka nutse.
34 放豬的看見發生的事,就逃去,到城裏和鄉間傳報開了。
Lokacin da mutanen da su ke kiwon aladun suka ga abin da ya faru, sai suka gudu! Suka ba da rahoton abin da ya faru ga mutanen cikin gari da na wannan kewayen.
35 人就出來看那發生的事,來到耶穌前,發現脫離魔鬼的那人,穿著衣服,神智清醒,坐在耶穌跟前前;他們就害怕起來,
Don haka, mutanen da suka ji haka suka tafi domin su ga abin da ya faru, suka zo wurin da Yesu yake, suka ga mutumin wanda aljanu suka fita daga cikinsa. Suka ga ya na sanye da tufafi, kuma ya na cikin hankalinsa, sai tsoro ya kama su.
36 那些見過這事的人就對他們述說:那附魔的人怎樣被治好了。
Mutanen da suka ga abin da ya faru, suka gaya wa wadansu yadda aka warkar da mutumin da aljanu suke iko da shi.
37 革辣撒所有的人民要尸離開他們,因為他們十分恐懼。祂便上船回去。
Sai dukan mutane wadanda suke cikin yankin Garasinawa da wadanda suke kewaye, suka roki Yesu da ya fita daga cikin yankin kasarsu domin sun ji tsoro kwarai da gaske. Daga nan Yesu da almajiransa suka shiga cikin jirgin ruwa suka koma.
38 脫離魔鬼的那人祈求耶穌:要同耶穌在一起;但耶穌打發他回去,說:
Mutumin wanda aljanu suka fita daga cikinsa, ya roki Yesu cewa, “Ka barni in tafi tare da kai!” Amma Yesu ya sallame shi cewa,
“Ka koma gida ka gaya wa mutanen ka abubuwa masu girma wadanda Allah ya yi maka.” Daga nan sai mutumin ya tafi yana ta gayawa dukan mutanen birnin game da abubuwan da Yesu ya yi masa.
40 耶穌回來時,群眾都迎接祂,因為眾人都在等候祂。
Sa'adda Yesu ya dawo, mutanen suka marabce shi, gama, dukansu suna jiransa.
41 來弓一個人,名叫雅依洛,這人是一個會堂長,跪伏在尸腳前,求祂到自己家中去,
Sai ga wani mutum mai suna Yayirus, daya daga cikin shugabannin majami'a, ya zo kusa da Yesu ya rusuna da kansa a kasa. Ya roke shi domin ya zo gidansa,
42 因為他有一個獨生女,約十二歲,快要死了。當耶穌去的時候,眾人都擁擠祂。
saboda diyarsa mai kimanin shekara goma sha biyu ta na bakin mutuwa, kuma ita kadai ce diya a gare shi. Amma sa'adda yake tafiya, taron mutane da yawa suna matsa shi.
43 有一個婦人,十二年來患血漏病,把全部家產都花在醫生身上,卻沒有一個能治好她。
Akwai wata mace a nan wadda take zubar jini har shekara goma sha biyu. Ta kashe kudinta duka a wurin likitoci, domin su warkar da ita amma ba wanda ya iya warkar da ita.
44 她來到耶穌後邊摸了摸祂衣服的繸頭,她的血漏立刻就止住了。
Sai ta biyo ta bayan Yesu ta taba habar rigarsa. Nan take sai zubar jinin ya tsaya.
45 耶穌說:「誰摸了我? 」人都否認,伯多祿說:「老師,眾人都在擁擠著你! 」
Yesu ya ce, “Wanene ya taba ni?” Wadanda suke kewaye da shi, kowa ya ce bai taba shi ba, Bitrus ya ce, “Shugaba, mutane da yawa suna ta taruwa kewaye da kai suna ta matsowa kusa da kai.”
46 耶穌卻說:「有人摸了我,因為我覺得有能力從我身上出去了。」
Amma Yesu ya ce, “Na sani, wani ya taba ni, domin iko ya fita daga wurina.”
47 那婦人看不能隱瞞,就戰戰競競地來跪伏在耶穌跟前,把自己摸祂的緣故和如何立刻病好的事,在眾百姓面前說了出來。
Sa'adda matar ta gane cewa ba za ta iya boyewa ba, sai ta zo wurinsa cikin tsoro. Ta durkusa a gaban Yesu, ta fada a gaban dukan jama'a dalilin da ya sa ta taba shi kuma nan da nan ta warke.
48 耶穌遂對她說:「女兒,妳的信德救了妳,平安去吧! 」
Sai ya ce da ita, “Diya, bangaskiyarki ta warkar da ke. Tafi cikin salama.”
49 祂還在話話時,有人從會堂長家裏來說:「你的女兒死了,不必煩勞師傅了。」
Yana cikin yin magana, wani daga cikin gidan shugaban majami'ar ya zo, ya ce, “Diyarka ta riga ta mutu, kada ka dami malam.”
50 耶穌聽了,就對他說:「不要害怕,只管信,她必得救。」
Amma sa'adda Yesu ya ji haka, sai ya ce da shi, “Kada ka ji tsoro. Ka bada gaskiya za ta rayu.”
51 耶穌到了那家裏,除了伯多祿、若望、雅各伯和女孩子的父母外,不讓任何人同祂進去。
Sa'adda ya zo gidan, bai bar kowa ya shiga gidan tare da shi ba sai Bitrus da Yahaya da Yakubu, da mahaifiyar yarinyar da babanta.
52 眾人都在痛哭哀弔女孩子。祂卻說:「不要哭泣,她並沒有死,只是睡著了。」
Dukan mutane a wurin, suna ta kuka da karfi saboda sun damu da yarinyar ta mutu. Amma Yesu ya ce da su, “Ku dena kuka! Ba mutuwa ta yi ba! Barci ta ke yi kawai!”
Mutanen suka yi ma sa dariyan reni, saboda sun sani yarinyar ta mutu.
Amma ya kama hannun ta yayi kira cewa, “Yarinya, na ce ki tashi!”
55 她的靈魂回來了,她就立起來了。耶穌吩咐給她吃的。
Nan da nan ruhun ta ya dawo jikin ta sai ta tashi. Ya ce masu su ba ta wani abu ta ci.
56 她的父母驚訝的出神。耶穌卻警告他們不要傳揚這事。
Iyayenta suka yi mamaki, amma Yesu ya ce da iyayen kada su gaya wa kowa abin da ya faru.