< 路加福音 7 >

1 耶穌向民眾講完了道一切話以後,就進了葛法翁。
Bayan da Yesu ya gama fadar dukan abubuwan da zai fadi a jin kunnen dukan mutanen, sai ya shiga Kafarnahum.
2 有一個百夫長,他所喜愛的僕人害病要死。
Bawan wani jarumi, wanda yake kauna, ba shi da lafiya har ma ya kusa mutuwa.
3 他聽說過耶穌的事,就打發猶太人的幾個長老祂那裏去,求祂來治好自己的僕人。
Amma da ya ji labarin Yesu, jarumin ya aiki wadansu dattawan Yahudawa, ya ce a roki Yesu ya zo ya ceci bawansa daga mutuwa.
4 他們到了耶穌那裏,懇切求祂說:「他堪當你給他做這事,
Sa'adda su ka zo kusa da Yesu, su ka roke shi da gaske, cewa, “Wannan ya isa ka yi masa haka,
5 因為祂愛護我們的民族,又給我們建築了會堂。」
saboda shi mai kaunar kasar mu ne, kuma shi ne ya gina mana majami'a.
6 耶穌就同他們去了。當祂離那家不遠時,百夫長打發僕人向祂說:「主啊! 不必勞駕了! 因為我當不起你到舍下來。
Sai Yesu ya tafi tare da su. Amma sa'adda ya zo kusa da gidan mutumin, jarumin ya aiki abokansa su ka ce da shi, “Ubangiji kada ka damu domin ni ban isa ka zo gida na ba.
7 為此我認為我不堪當親自到你跟前來,只請你說一句話,我的僕人就必好了。
Shi ya sa na ga ban isa in zo wurinka ba, ka yi magana kadai bawa na kuwa zai warke.
8 因為我雖是受派在人權下的,但是在我下也有士兵;,我對這個說:你去! 他就去;對那個說:你來! 他就來;對我的奴僕說:你作這個! 他就做。」
Gama ni ma mutum ne mai iko, ina da sojoji karkashina. Ina iya cewa da wannan, 'Ka je' sai ya tafi, in kuma ce da wani 'ka zo' sai ya zo, in kuma ce da bawa na, 'Yi kaza,' sai ya yi.”
9 耶穌一聽這些話,就佩服他,遂轉身對跟髓祂的人說:「我告訴你們:連在以色列,我也沒有見過這樣大的信德。
Sa'adda Yesu ya ji haka, ya yi mamakin mutumin, ya juya wajen taron da su ke biye da shi, ya ce, “Na gaya maku, ko a cikin Isra'ila ban sami wani mai bangaskiya irin wannan ba”
10 被派去的人回到家中,見那僕人已痊癒了。
Daga nan wadanda a ka aika, suka dawo gida suka tarar da bawan cikin koshin lafiya.
11 以後,耶穌往一座名叫納因的城去,祂的們徒和許多群眾與祂同行。
Wani lokaci bayan wannan, ya zama Yesu yana tafiya wani gari da ake kira Na'im. Almajiransa su na tare da shi, da kuma taron mutane masu yawa.
12 臨近城門時,看,正抬出一個死人來,他是母親的獨生子,母親又是寡婦;且有本城的一大夥人陪她。
Sa'adda ya kusa da kofar garin, sai ga wani matacce ana dauke da shi. Kuma shi kadai ne da a wurin mahaifiyarsa. Ita kuwa gwauruwa ce, mutane da dama daga cikin gari suna tare da ita.
13 主一看見她,就對她動了憐憫的心,向她說:「不要哭了! 」
Da ganin ta, sai Ubangiji ya cika da tausayi a game da ita ya ce da ita, “Kada ki yi kuka.”
14 遂上前按往棺材,抬棺材的人就站往了。祂說:「青年人,我對你說:起來吧! 」
Sai ya zo ya taba makarar, sai masu dauke da shi su ka tsaya. Ya ce 'Saurayi na ce ma ka ka tashi.”
15 那死者便坐起來,並開口說話;耶穌便把他交給了他的母親。
Sai mataccen ya tashi ya fara yin magana. Sai Yesu ya ba mahaifiyar danta.
16 眾人都害怕起來,光榮天主說:「在失們當中興起了一位大先知,天主眷顧了祂自己的百姓。」
Sai tsoro ya kama su duka. Su ka kama yabon Allah, su na cewa, “An ta da wani annabi mai girma a cikinmu” kuma “Allah ya dubi mutanensa.”
17 於是,稱述耶穌的這番話,傳遍了猶太和附近各地。
Wannan labari na Yesu, ya ba zu a cikin dukan Yahudiya da yankuna da su ke kewaye.
18 若翰的門徒把這一切報告給若翰,若翰便叫了自己的兩個門徒來,
Almajiran Yahaya suka gaya masa dukan wadannan abubuwa.
19 打發他們到主那裡去說:「你就是要來那位或者我們還要等待另一位?」
Sai Yahaya ya kira biyu daga cikin almajiransa, ya aike su wurin Ubangiji, suka ce da shi, “Kai ne mai zuwan nan, ko akwai wani wanda za mu saurari zuwansa?”
20 二人來到耶穌跟前說:「洗者若翰派我們來問你:你就是要來那位或者我們還要等候另一位?」
Sa'adda suka zo kusa da Yesu, sai mutanen suka ce, “Yahaya Mai Baftisma, ya aiko mu, mu tambaya, “Kai ne mai zuwan nan, ko akwai wani wanda za mu saurari zuwansa?”
21 正在那時刻,祂治好了許多患有病痛和疾苦的,並附有惡魔的人,又恩賜許多瞎子看見。
A cikin wannan lokaci, ya warkar da mutane da yawa daga cututtuka da matsaloli da miyagun ruhohi. Makafi da yawa sun sami ganin gari.
22 祂便回答說:「你們去吧! 把你們所見所聞的報告給若翰:瞎子看見,瘸子行走,癩病人潔淨,聾子聽見,死人復活,貧窮人聽到喜訊。
Yesu, ya amsa ya ce masu, “Bayan kun tafi, ku ba Yohanna rahoton abin da ku ka ji da abin da ku ka gani. Makafi suna ganin gari, guragu suna tafiya, ana kuma tsarkake kutare. Kurame suna ji, ana tayar da matattu, ana gaya wa matalauta labari mai dadi.
23 凡不因我而絆倒的,是有福的。」
Mai albarka ne mutumin da ya tsaya a kan ba da gaskiya gare ni saboda ayukan da na ke yi.”
24 若翰的使者走了以後,就對群眾論若翰說:「你們出去到荒野裏是為看什麼呢? 是看一枝被風搖曳的蘆葦嗎?
Bayan da mutanen da Yahaya ya aiko suka tafi, Yesu ya fara yi wa taron magana game da Yahaya. “Me ku ka tafi ku gani a cikin hamada, ciyawa wadda iska ta ke girgizawa?
25 你們出去到底是為看什麼? 為看一位穿細軟衣服的人嗎? 啊! 那衣服華麗和生活奢侈的人是在王宮裏。
Amma me ku ka tafi domin ku gani, mutum mai saye da tufafi masu taushi? Duba mutanen da su ke saye da tufafi masu daraja, kuma suna rayuwa cikin jin dadi suna fadar sarakuna.
26 你們出去究竟是為看什麼? 為看一位先知嗎? 是的,我告訴你們:而且他比先知還大。
Amma me ku ka tafi domin ku gani, annabi ne? I, ina gaya ma ku, ya ma fi annabi.
27 關於這人經上記載說:『看,我派遺我的使者在你在面前,他要在你的在前面預備你的道路。』
Wannan shine wanda aka rubuta a kansa, “Duba, ina aika manzo na a gabanka, wanda za ya shirya maka hanya a gabanka.
28 我告訴你們:婦女所生的,沒有一個比若翰更大的;但在天主的國最小的,也比他大。
Ina gaya maku, a cikin wadanda mata suka haifa, ba wanda ya fi Yahaya girma. Duk da haka, wanda ya fi kankanta a mulkin Allah, ya fi shi girma.
29 聽教的眾百姓和稅吏,都承認天主正義的要求而領受了若翰的洗禮。
Sa'anda dukan mutane suka ji haka, har da ma su karbar haraji, suka shaida Allah mai adalci ne. Su na cikin wadanda Yahaya ya yi wa baftisma.
30 但法利賽人和法學士卻沒有受他的洗,在自己的身上使天主的計劃作廢。
Amma Farisawa da wadanda su ke kwararru a cikin shari'ar Yahudawa, wadanda ba shi ne ya yi masu baftisma ba, suka yi watsi da hikimar Allah don kansu.
31 我可把這一時代的人比作什麼呢? 他們相似什麼人呢?
Sa'annan Yesu ya ce, “Da me zan kamanta mutanen wannan zamani? Da me suka yi kama?
32 他們相似坐在街上的兒童,彼此呼喚說:我們給你們吹笛,你們卻不跳舞;我們唱哀歌,你們卻不悲哭。
Suna kama da yaran da suke wasa a kasuwa, wadanda suke magana da junansu suna cewa, “Mun yi maku busa, ba ku yi rawa ba. Mun yi makoki, ba ku yi kuka ba.”
33 因為洗者若翰來了,他不吃餅,也不喝酒,們便說:他附了魔。
Haka, Yahaya ya zo, bai ci gurasa ba, bai sha ruwan inabi ba, amma ku ka ce, 'Aljani ne yake mulkinsa.
34 人子來了,也吃也喝,你們又說:這是個貪吃嗜酒的人,是個稅吏和罪人的朋友。
Dan Mutum, ya zo, yana ci, yana sha, amma, kuka ki shi, kuna cewa dubi mutum mai hadama, mai shan ruwan inabi da yawa, abokin masu karbar haraji da masu zunubi!
35 但一切智慧之子,必彰顯智慧的正義。
Amma hikimar Allah tana shaidar dukan 'yayanta.”
36 有個法利賽人請耶穌同他吃飯,祂便進了那法利賽人的家中坐席
Wata rana wani Bafarise, ya roki Yesu ya je ya ci abinci tare da shi. Bayan da Yesu ya shiga gidan Bafarisen, ya zauna a teburi domin ya ci abinci.
37 那時,有個婦人,是城中的罪人,她一聽說耶穌在法利賽人家中坐席,就帶著一玉瓶香液,
Sai ga wata mace mai zunubi, ta fito daga cikin birni. Sa'anda ta ji labari Yesu yana gidan Bafarisen, domin ya ci abinci. Ta dauki tandun mai na alabastar mai kamshi.
38 來站在祂背後,靠近祂的腳哭開了,用眼淚滴濕了祂的腳,用自己的頭髮擦乾,又熱切地口親祂的腳,以後抹上香液。
Ta tsaya kusa da Yesu tana kuka. Ta fara jika kafafunsa da hawayenta, tana shafe kafafunsa da gashin kanta. Tana yi wa kafafunsa sumba, tana shafe su da turare.
39 那請耶穌的法利賽人見了,就心裏想:「這人若是先知,必定知道這個摸他的人是誰,是怎樣的女人:是一個罪婦。」
Sa'anda Bafarisen da ya gaiyaci Yesu, ya ga haka, sai ya yi tunani a cikin ransa, da cewa, “In da wannan mutum annabi ne, da ya gane ko wacce irin mace ce, wannan da take taba shi, ita mai zunubi ce.”
40 耶穌發言對他說:「西滿,我有一件事要向你說。」西滿說:「師傅,請說吧!
Yesu ya amsa ya ce masa, “Siman, ina so in gaya maka wani abu.” Ya ce, “malam sai ka fadi!”
41 一個債主有兩個債戶:一個欠五百德納,另一個欠五十。
Yesu ya ce, “wani mutum mai ba da bashi yana bin wadansu mutane su biyu kudi, yana bin dayan sule dari, dayan kuma yana bin sa sule hamsin.
42 因為他們都無力償還,債主就開恩,赦免了他們二人。那麼他們中誰更愛他呢? 」
Da yake ba su da kudin da za su iya biyan sa, sai ya yafe masu, su duka biyu. A cikin su biyu, wanne ne zai fi nuna kauna ga wannan mutum?”
43 西滿答說:「我想是那多得恩赦的。」耶穌對他說:「你判斷得正對。」
Siman ya amsa ya ce, “Ina tsammani wanda ya yafe wa kudi da yawa.” Yesu ya amsa ya ce masa, “Ka shari'anta dai dai.”
44 祂遂轉身向那婦人,對西滿說:「你看見這個婦人嗎? 我進了你的家,你沒有給我水洗腳,她卻用眼淚滴濕了我的腳,並用頭髮擦乾。
Yesu ya juya wajen matar, ya ce da Siman, “Ka ga matan nan. Na shiga gidanka. Ba ka ba ni ruwa domin kafafuna ba, amma ita ta ba ni, da hawayenta ta wanke kafafuna, ta kuma shafe su da gashin kanta.
45 你沒有給我行口親禮,她卻自從我進來,就不斷地口親我的腳
Kai ba ka yi ma ni sumba ba, amma ita ta yi, tun sa'adda na shigo nan ba ta dena sumbatar kafafuna ba.
46 你沒有用油抹我的頭,她卻用香液抹了我的腳。
Kai ba ka shafe kai na da mai ba, amma ita ta shafe kafafuna da turare.
47 故此,我告訴你:她的那許多罪得了赦免,因為她愛得多;但那少得赦免的,是愛的少。」
Saboda haka, ita wadda ta ke da zunubi da yawa ta bayar da mai yawa, ta kuma nuna kauna mai yawa. Amma shi wanda aka gafarta wa kadan, ya kuma nuna kauna kadan.”
48 耶穌遂對婦人說:「妳的罪得了赦免。」
Daga nan sai ya ce mata, “An gafarta zunubanki.”
49 同席的人心中想道:「這人是誰? 他竟然赦免罪過! 」
Wadanda su ke a nan zaune tare da shi suka fara magana da junansu, “Wanene wannan wanda har yake gafarta zunubai?
50 耶穌對婦人說:「的信德救了妳,平安回去吧! 」
Sai Yesu ya ce da matar, “Bangaskiyarki ta cece ki. Ki tafi da salama.”

< 路加福音 7 >