< 猶大書 1 >

1 耶穌基督的僕人,雅各伯的弟兄猶達,致書給在天主父內蒙愛,為耶穌基督而保存的蒙召者。
Yahuda, bawan Yesu Kiristi, ɗan’uwan Yaƙub, Zuwa ga waɗanda aka kira, waɗanda Allah Uba yake ƙauna, waɗanda kuma Yesu Kiristi ya kiyaye.
2 願仁慈、平安、愛情豐富地賜予你們。
Jinƙai, salama da kuma ƙauna, su kasance tare da ku a yalwace.
3 親愛的,我早已切望給你們寫信,討論我們共享的就恩;但現在不得不給你們寫信,勸勉你們應奮鬥,維護從前一次而永遠傳與聖徒的信仰。
Abokaina ƙaunatattu, ko da yake na yi marmari ƙwarai in rubuta muku game da ceton nan namu, sai na ga ya dace in rubuta, in gargaɗe ku ku tsaya da ƙarfi cikin bangaskiya wadda aka danƙa wa mutane masu tsarki na Allah sau ɗaya tak.
4 因為有些早已被注定要受這審判的人,潛入你們中間;他們是邪惡的人,竟把我們天主的恩寵,變為放縱情慾的機會,並否認我們獨一的主宰和主耶穌基督。
Na faɗa haka ne domin waɗansu mutanen da aka rubuta hukuncinsu tun dā sun shiga cikinku a ɓoye. Su fa marasa tsoron Allah ne. Su ne waɗanda suka mai da alherin Allahnmu ya zama dalilin yin fasikanci, suna kuma mūsun Yesu Kiristi wanda shi ne Makaɗaici Mai Iko Duka da kuma Ubangijinmu.
5 雖然你們一次而永遠知道這一切,但我仍願提醒你們:主固然由埃及地救出了百姓,隨後卻把那些不信的人消滅了;
Ko da yake kun riga kun san duk wannan, ina so in tuna muku cewa Ubangiji ya ceci mutanensa daga Masar, duk da haka daga baya ya hallaka waɗanda ba su ba da gaskiya ba.
6 至於那些沒有保持自己尊位,而離棄自己居所的天使,主也用永遠的鎖鏈,把他們拘留在幽暗中,以等候那偉大日子的審判; (aïdios g126)
Haka ma mala’ikun da ba su riƙe matsayinsu na iko ba, waɗanda suka bar ainihin mazauninsu, su ne ya tsare a duhu daure da dawwammamun sarƙoƙi don hukunci ta babbar Ranan nan. (aïdios g126)
7 同樣,索多瑪和哈摩辣及其附近的城市,因為也和他們一樣恣意行淫,隨從逆性的肉慾,至今受著永火的刑罰,作為鑑戒。 (aiōnios g166)
Haka ma Sodom da Gomorra da garuruwan da suke kewaye da su, waɗanda su ma suka ba da kansu ga fasikanci da muguwar sha’awar jiki, sun zama misalin waɗanda suke shan hukuncin madawwamiyar wuta. (aiōnios g166)
8 可是這些作夢的人照樣玷污肉身,拒絕主權者,褻瀆眾尊榮者。
Haka yake da masu mafarke-mafarken nan, gama sun ƙazantar da jikunansu, suka ƙi bin masu mulki, suna ɓata sunan talikan sararin sama.
9 當總領天使彌額爾,為了梅瑟的屍體和魔鬼激烈爭辯時,尚且不敢以侮辱的言詞下判決,而只說:「願主叱責你!」
Kai, ko Mika’ilu babban shugaban mala’iku ma, sa’ad da yake mūsu da Iblis game da gawar Musa, bai yi garajen ɗora masa laifi da baƙar magana ba, sai dai ya ce, “Ubangiji yă tsawata maka!”
10 這些人卻不然,凡他們所不明白的事就褻瀆,而他們按本性所體驗的事,卻像無理性的牲畜一樣,就在這些事上敗壞自己。
Duk da haka mutanen nan suna maganar banza a kan kome da ba su gane ba; kuma abubuwan da suka fahimta bisa ga jiki, kamar dabbobi marasa hankali, waɗannan abubuwa ne suke hallaka su.
11 這些人是有禍的!因為他們走了加音的路,為圖利而自陷於巴郎的錯誤,並因科辣黑一樣的判逆,而自取滅亡。
Kaitonsu! Gama sun kama hanyar Kayinu; sun ruga a guje garin neman riba cikin kuskure kamar Bala’am; aka kuma hallaka su cikin tawayen Kora.
12 這些人是你們愛宴上的污點,他們同人宴樂,毫無廉恥,只顧自肥;他們像無水的浮雲,隨風飄盪;又像晚秋不結果實,死了又死,該連根拔出來的樹木;
Waɗannan mutane sun zama kamar ƙazanta a taronku na soyayya, suna ta ciye-ciye a cikinku, ba kunya ba tsoro. Su masu kiwo ne da suke ciyar da kansu kawai. Su kamar hadari ne da babu ruwa da iska take kori. Su kamar itatuwa ne, marasa’ya’ya da rani, waɗanda aka tumɓuke, ko kamar itatuwan da aka tumɓuke suka kuma mutu ƙurmus.
13 像海裏的怒濤,四下飛濺他們無恥的白沫;又像出軌的行星;為他們所存留的,乃是直到永遠的黑暗的幽冥。 (aiōn g165)
Su kamar raƙuman ruwan teku ne masu hauka, suna taƙama da tumbatsan kumfar kunyarsu. Su kamar taurari ne masu yawo barkatai, waɗanda aka ajiye mugun duhu saboda su har abada. (aiōn g165)
14 針對這些人,亞當後第七代聖祖哈諾客也曾預言說:「看,主帶著他千萬的聖者降來,
Enok ma, wanda yake na bakwai daga Adamu, ya yi annabci game da waɗannan mutane cewa, “Duba, Ubangiji yana zuwa da dubu dubban tsarkakansa
15 要審判眾人,指證一切惡人所行的一切的惡事,和邪辟的人所說的一切褻瀆他的言語。」
don yă yi wa kowa shari’a, yă kuma hukunta duk marasa tsoron Allah game da dukan ayyukansu na rashin tsoron Allah da suka aikata ta hanyar rashin tsoron Allah, da kuma dukan baƙaƙen kalmomin da masu zunubi marasa tsoron Allah suka faɗa game da shi.”
16 這些人好出怨言,不滿命運;按照自己的私慾行事,他們的口好說大話,為了利益而奉承他人。
Waɗannan mutane dai, gunaguni gare su, kullum ganin laifin waɗansu suke yi. Muguwar sha’awa ce kaɗai tunaninsu. Sun cika da banzar magana ta yabon kansu. Suna ruɗin mutane da zaƙin baki don samun ribar kansu.
17 但是,你們,親愛的,你們要記得我們的主耶穌基督的宗徒所預言過的話,
Amma ku abokaina ƙaunatattu, ku tuna da abin da manzannin Ubangijinmu Yesu Kiristi suka faɗa a dā.
18 他們曾向你們說過:「到末期,必有一些好嘲弄人的人,按照他們個人邪惡的私慾行事。」
Sun ce muku, “A kwanakin ƙarshe za a kasance da masu ba’a waɗanda za su bi sha’awace-sha’awacensu na rashin tsoron Allah.”
19 這就是那些好分黨分派,屬於血肉,沒有聖神的人。
Waɗannan mutanen ne, suke kawo rabe-rabe, masu bin abin da jiki yake so, marasa Ruhu.
20 可是,你們,親愛的,你們要把自己建築在你們至聖的信德上,在聖神內祈禱;
Amma ku, abokaina ƙaunatattu, ku gina kanku cikin bangaskiyarku mafi tsarki, ku kuma yi addu’a cikin Ruhu Mai Tsarki.
21 這樣保存你們自己常在天主的愛內,期望賴我們的主耶穌基督的仁慈,入於永生。 (aiōnios g166)
Ku zauna cikin ƙaunar Allah yayinda kuke jira jinƙan Ubangijinmu Yesu Kiristi don yă kawo ku ga rai madawwami. (aiōnios g166)
22 對那些懷疑不信的人,你們要說服;
Ku ji tausayin waɗanda suke shakka;
23 對另一些人,你們要拯救,把他們從火裏拉出來;但對另一些人,你們固然要憐憫,可是應存戒懼的心,甚至連他們肉身所玷污了的內衣,也要憎惡。
ku cece waɗansu ta wurin fizge su daga wuta. Ga waɗansu kuma ku ji tausayinsu, amma tare da tsoro, har ma ku yi ƙyamar tufafin da suka ɓata da ayyukansu na jiki.
24 願那能保護你們不失足,並能叫你們無瑕地,在歡躍中立在他光榮面前的,
To, yabo yă tabbata a gare shi, shi wanda yake da iko yă tsare ku daga fāɗuwa, yă kuma miƙa ku marasa laifi a gaban ɗaukakarsa da matuƙar farin ciki.
25 惟一的天主,我們的救主,藉我們的主耶穌基督,獲享光榮、尊威、主權和能力,於萬世之前,現在,至於無窮之世。阿們。 (aiōn g165)
Gare shi kuma, shi da yake kaɗai Allah Mai Cetonmu, ta wurin Yesu Kiristi Ubangijinmu, bari ɗaukaka, daraja, iko da mulki, su tabbata a gare shi, tun farkon zamanai, yanzu, da har abada abadin! Amin. (aiōn g165)

< 猶大書 1 >