< 約書亞記 10 >
1 當耶路撒冷王阿多尼責德克聽說若蘇厄攻佔了哈依,完全予以毀滅,對待哈依和哈依王如對待耶利哥和耶利哥王一樣;又聽說基貝紅居民已與以色列媾和,可住在他們中間,
Adoni-Zedek sarkin Urushalima ya ji cewa Yoshuwa ya ci Ai da yaƙi ya kuma hallaka ta sarai, ya yi wa Ai da sarkinta abin da ya yi wa Yeriko da sarkinta, mutanen Gibeyon kuwa sun yi yarjejjeniya ta salama da Isra’ilawa, suna kuma zama kusa da su.
2 大為震驚,因為基貝紅是座大城,像座京城,比哈依還大,中的人又都勇敢。
Shi da mutanensa suka ji tsoron wannan sosai, gama Gibeyon muhimmiyar birni ce, har ma kamar ɗaya daga cikin biranen sarauta, ya ma fi Ai girma, mazanta duka kuwa mayaƙa ne na ƙwarai.
3 耶路撒冷王阿多尼責德克打發使者去見赫貝龍王曷罕、雅爾慕特王丕蘭、拉基士王雅非雅和厄革隆王德彼爾說:
Saboda haka sai Adoni-Zedek sarkin Urushalima ya roƙi Hoham sarkin Hebron, Firam sarkin Yarmut, Yafiya sarkin Lakish da Debir sarki Eglon ya ce,
4 「請你們前來援助我,攻打基貝紅,因為這城已與若蘇厄和以色列人媾和。」
“Ku zo ku taimake ni in kai wa Gibeyon hari. Domin sun yi yarjejjeniya ta salama da Yoshuwa da Isra’ilawa.”
5 那五個阿摩黎王,即耶路撒冷王、赫貝龍王、雅爾慕特王、拉基士王和厄革隆王聯合起來,率領他們所有的軍隊上去包圍了基貝紅,合力進攻。
Sai sarakunan nan biyar na Amoriyawa, sarakunan Urushalima, Hebron, Yarmut, Lakish da Eglon suka haɗa sojojinsu. Suka je dukansu suka yi shirin kai wa Gibeyon hari.
6 基貝紅人即派人到基耳加耳營中見若蘇厄說:「你不要袖手不顧你的僕人,請快上來援助,扶助我們,因為住在山地的眾阿摩黎王都聯合起來攻擊我們。」
Sai mutanen Gibeyon suka aika zuwa wurin Yoshuwa a sansani a Gilgal, “Kada ka juya wa bayinka baya, ka zo da sauri ka cece mu! Ka taimake mu domin sarakunan Amoriyawa duka daga kan tudu sun haɗa ƙarfinsu tare za su tasar mana.”
7 若蘇厄遂親率他的一切軍民,和所有的精兵,從耳加耳上去了。
Saboda haka Yoshuwa ya tashi da rundunarsa duka, tare da dukan jarumawansa.
8 上主對若蘇厄說:「你不要怕他們,因為我已將他們交在你手中,沒有一人能抵抗你。」
Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Kada ka ji tsoronsu; na ba ka su a hannunka. Ba waninsu da zai iya tsayayya da kai.”
9 若蘇厄由基耳加耳出發,整夜行軍,出其不意,突然向他們進攻。
Bayan sun yi tafiya dukan dare daga Gilgal, Yoshuwa ya auko musu ba labari.
10 上主使他們以色列人前大為混亂,以色列人在基貝紅將他們完全擊敗,隨後在往貝特曷龍的上坡路上追趕他們,擊殺他們直到阿則卡,直到瑪刻達。
Ubangiji ya sa suka ruɗe a gaban Isra’ilawa, Isra’ilawa kuwa suka yi babbar nasara a kansu a Gibeyon. Isra’ilawa suka fafare su a kan hanyar zuwa Bet-Horon suka karkashe su duka har zuwa Azeka da Makkeda.
11 當他們逃避以色列人,來到貝特曷龍下坡時,上主從天上降下冰雹,落在他們身上,直落到阿則卡,死傷無數;為冰雹砸死的人,教宗以色列用刀死的還多。
Suna guje wa Isra’ilawa suna gangarawa a kan hanyar Bet-Horon har zuwa Azeka, sai Ubangiji ya turo manyan duwatsu daga sararin sama suka karkashe su, waɗanda manyan duwatsun suka kashe sun fi waɗanda Isra’ilawa suka kashe da takobi.
12 上主將阿摩黎人交於以色列子民的那一天,若蘇厄當以色列人的面對上主說:「太陽! 停在基貝紅! 月亮! 停在阿雅隆谷! 」
A ranar da Ubangiji ya ba da Amoriyawa a hannun Isra’ilawa, Yoshuwa ya ce wa Ubangiji a gaban Isra’ilawa, “Ke rana, ki tsaya cik a Gibeyon Kai wata, ka je Kwarin Aiyalon.”
13 太陽果然停住,月亮站住不動,直到百姓報復了自己的仇敵。這事豈不是記載在「義士書」上了嗎﹖太陽停在空中,未急速下落,約有一整天。
Sai rana ta tsaya cik, wata kuma ya tsaya, har sai da al’ummar ta ɗauki fansa a kan abokan gābanta, kamar yadda aka rubuta a cikin littafin Yashar. Rana ta tsaya a sararin sama, ba tă fāɗi ba har kusan yini guda.
14 以前或以後,從來沒有一天像這天一樣。上主這樣俯聽了人的呼聲,因為是上主在為以色列人作戰。
Ba a taɓa ganin abu haka ba ko dā can, ranar da Ubangiji ya saurari mutum. Ba shakka Ubangiji yana yaƙi domin Isra’ilawa.
15 此後,若蘇厄和所有跟隨他的以色列人,回了基耳加耳營。
Sai Yoshuwa ya koma sansanin Gilgal tare da dukan Isra’ilawa.
Sarakunan guda biyar suka gudu, suka ɓuya a cikin kogo a Makkeda.
17 有人來通知若蘇厄說:「那五個王子已被發現,藏在瑪刻達山洞裏。」
Lokacin da aka gaya wa Yoshuwa cewa an sami sarakunan nan biyar a ɓoye a cikin kogo a Makkeda.
18 若蘇厄吩咐說:「你們把幾塊大石滾到洞口,派人看守。
Sai ya ce, “Ku mirgina manyan duwatsu ku rufe bakin kogon, sai ku sa waɗannan mutane su yi tsaron kogon.
19 你們不可停下來,要去追趕敵人,切斷他們的後路,不容他們逃入城中,因為上主你們的天主,已將他們交在你們手中。」
Amma kada ku tsaya a can! Ku fafari abokan gābanku, ku kai musu hari ta baya, kada ku bari su kai biranensu, gama Ubangiji Allahnku ya ba da su a hannunku.”
20 以色列子民將他們殺得慘敗,幾乎將他們全部消滅,只剩下一些逃脫的人進入了堅城。
Saboda haka Yoshuwa da Isra’ilawa suka hallaka su da yawa ƙwarai, amma’yan kaɗan ɗin da suka rage suka tsere zuwa cikin biranensu masu kāriya.
21 軍民都平安無恙地回到瑪克達見若蘇厄。以後沒有人再敢侮辱以色列子民。
Dukan rundunar kuma suka dawo sansanin Makkeda tare da Yoshuwa, ba abin da ya same su. Ba wanda ya sāke tsokanar Isra’ilawa.
22 那時若蘇厄說:「你們去打開洞口,把五個王子從洞裏拉出來,帶到我這裏來。」
Yoshuwa ya ce, “Ku buɗe bakin kogon ku kawo mini sarakunan nan guda biyar.”
23 人就去,將那五個王子,是耶路撒冷王、赫貝龍王、雅爾慕特王、拉基斯王和厄格隆王,從洞裏拉出,帶到他面前,
Sai suka kawo sarakunan biyar daga cikin kogo; sarakunan Urushalima, Hebron, Yarmut, Lakish da Eglon.
24 當人們把那五個王子帶到若蘇厄面前時,若蘇厄將所有的以色列人召來,對那些與他同去作戰的軍長說:「你們前來,將腳踏在這些王子的脖子上! 」他們就前來,將腳踏在那些王子的脖子上。
Sa’ad da aka kawo sarakunan nan wurin Yoshuwa, ya kira dukan Isra’ilawa ya ce wa shugabannin rundunoni waɗanda suke tare da shi, “Ku zo nan ku taka wuyan sarakunan nan.” Sai suka zo suka taka wuyansu.
25 若蘇厄對他們說:「你們不要害怕,不要沮喪,只要勇敢果斷,因為上主必要這樣對待你們所征服的一切仇人。」
Yoshuwa ya ce musu, “Kada ku ji tsoro, ko kuwa ku razana, amma ku ƙarfafa, ku yi ƙarfin hali. Haka Ubangiji zai yi da duk abokan gāban da za ku yi yaƙi da su.”
26 隨後,若蘇厄將那五個王子殺死,將他們懸在五棵樹上,直懸到晚上。
Sai Yoshuwa ya karkashe waɗannan sarakuna guda biyar, ya kuma rataye kowannensu a bisa itace inda jikunansu suka kasance har yamma.
27 到太陽快落時候,o命人將他們由樹上放下來,丟在他們藏過的山洞裏,用大石頭塞住洞口;那些大石至今尚在。
Da yamma Yoshuwa ya ba da umarni a sauko da su daga itatuwan a jefa su cikin kogon da suka ɓuya. Aka sa manyan duwatsu aka rufe bakin kogon, suna a can har wa yau.
28 若蘇厄當天就佔領了瑪克達,並用利劍擊殺了那城和城中的王子,並將城中的一切生靈完全毀滅,一個也沒有留下;他對待瑪刻達王如對耶利哥王一樣。
A ranan nan Yoshuwa ya ci Makkeda da yaƙi. Ya karkashe mutanen tare da sarkinta. Bai bar wani da rai ba. Ya yi wa sarkin Makkeda yadda ya yi wa sarkin Yeriko.
29 若蘇厄和跟隨他的眾以色列人,由瑪刻達往里貝納進攻,攻打里貝納。
Sai Yoshuwa da dukan Isra’ilawa suka tashi daga Makkeda zuwa Libna, suka kai mata hari.
30 上主也將這城和城中的王子交在以色列人手中;他們用利劍擊殺了城和城中的一切生靈,一個也沒有留下;他對待這城中的王子,如對待耶利哥王一樣。
Ubangiji kuma ya ba da ƙasar da sarkinta a hannun Yoshuwa. Yoshuwa ya karkashe kowa ya hallaka birnin, bai bar wani da rai ba. Ya kuma yi wa sarkin yadda ya yi wa sarkin Yeriko.
31 若蘇厄和跟隨他的眾以色列人,又從里貝納往拉基士推進,圍攻拉基士,
Sai Yoshuwa da dukan Isra’ilawa suka tashi daga Libna zuwa Lakish; suka yi shiri suka kai mata hari.
32 上主將拉基士也交在以色列人手中。第二天若蘇厄攻取了拉基士,用利劍擊殺了那城和城中的一切生靈,全如對待里貝納一樣。
Ubangiji ya ba da Lakish a hannun Isra’ilawa, a rana ta biyu kuwa Yoshuwa ya ci nasara a kansu. Ya karkashe duk mutanen birnin ya kuma hallaka birnin, kamar yadda ya yi a Libna.
33 那時曷爾曷蘭上來援救拉基士,若蘇厄也將他和他的人民殺盡,一個也沒有留下。
Horam sarkin Gezer kuwa ya zo don yă taimaki Lakish, amma Yoshuwa ya haɗa duk da shi da rundunarsa ya ci su da yaƙi, har bai bar waninsu da rai ba.
34 此後,若蘇厄和跟隨他的眾以色列人,由拉基士往厄革隆推進,圍攻厄革隆。
Yoshuwa kuwa da dukan Isra’ilawa suka tashi daga Lakish zuwa Eglon; suka yi shiri suka kai mata hari.
35 當夜攻下了那城,並在那天用利劍殺盡了那城和城中的一切生靈,全如對待拉基士一樣。
A ranan nan suka ci ƙasar da yaƙi, suka buge ta, suka karkashe kowa da takobi kamar dai yadda suka yi a Lakish.
36 上後,若蘇厄和跟隨他的眾以色列人,從厄革隆上到赫貝龍,攻打那城;
Sai Yoshuwa da dukan Isra’ilawa suka tashi daga Eglon zuwa Hebron suka kai hari a can.
37 佔領後,用利劍擊殺了那城和城中的王子,以及屬於他的一切生靈,一個也沒有留下;將那城和城中一切生靈完全消滅,全如對待厄革隆一樣。
Suka ci birnin da yaƙi, suka karkashe mazaunanta, da sarkin, har da ƙauyukan, ba wanda ya tsira kamar yadda ya yi wa Eglon. Ya hallakar da ita sarai duk da kowane mutum da yake cikinta.
38 此後,若蘇厄和跟隨他的眾以色列人,轉身向德彼爾推進,攻打那城,
Yoshuwa da Isra’ilawa duka suka juya suka kai wa Debir hari,
39 獲得了那城和那城的王子,以及屬德彼爾的一切城邑後,用利劍擊殺了他們,將這些城內的一切生靈完全毀滅,一個也沒有留下;對待德彼爾城和城中的王子,有如對待赫貝龍和赫貝龍的王子一樣又如對待里貝納和里貝納王子一樣。
suka hallaka birnin, da sarkinta da ƙauyukanta, suka karkashe dukan mazaunan wurin, ba su bar wani da rai ba. Suka yi wa Debir da sarkinta yadda suka yi wa Libna da sarkinta da kuma Hebron.
40 若蘇厄征服了那一帶地方包括山地、乃革布、平原、山坡和那些地方的不子;並照上主以色列的天主的命令,消滅了所有的生靈,一個也沒有留下,
Yoshuwa ya cinye yankin duka da yaƙi, haɗe da na kan tudu, da Negeb, da kwarin yamma, da filayen cikin duwatsu tare da sarakunansu duka. Bai bar wani da rai ba, ya kashe duk wani mai numfashi, yadda Ubangiji, Allah na Isra’ilawa ya umarta.
41 由卡德士巴爾乃亞起,直到迦薩,以及哥笙全境,直到基貝紅。
Yoshuwa ya ci su da yaƙi daga Kadesh Barneya zuwa Gaza, da kuma daga dukan yankin Goshen zuwa Gibeyon.
42 若蘇厄這次出征,能獲取所有的王子和他們的土地,是因為上主以色列的天主在為以色列人作戰。
Yoshuwa kuwa ya cinye sarakunan nan duka da ƙasashensu gaba ɗaya gama Ubangiji, Allah na Isra’ila ne ya yi yaƙi domin Isra’ilawa.
43 以後,若蘇厄和所有跟隨他的以色列人,回到基耳加耳營。
Yoshuwa kuwa ya dawo da dukan Isra’ilawa zuwa sansani a Gilgal.