< 約翰福音 7 >

1 這些事以後,耶穌週遊於加里肋亞,而不願週遊於猶太,因為猶太人要圖謀殺害他。
Bayan wadannan abubuwa Yesu ya zagaya cikin Gallili, saboda baya so ya shiga cikin Yahudiya domin Yahudawa suna shirin su kashe shi.
2 那時,猶太人的慶節,帳棚節近了,
To Idin Bukkoki na Yahudawa ya kusa.
3 他的弟兄於是對他說: 「你離開這裏,往猶太去罷!好叫你的門徒也看見你所行的事,
Sai 'yan'uwansa suka ce da shi, “ka tashi ka tafi Yahudiya, domin almajiranka su ga ayyukan da kake yi su ma.
4 因為沒有人願意顯揚自己,而在暗地裏行事的;你既然行這些事,就該將你自己顯示給世界。」
Ba wanda ya ke yin wani abu a boye idan dai yana so kowa da kowa ya san shi. Da yake ka na yin wadannan abubuwa sai ka nuna kan ka a fili ga duniya.
5 原來,連他的弟兄們也不願相信他。
Domin ko 'yan'uwansa ma basu bada gaskiya gare shi ba.
6 耶穌回答說:「我的時候還沒有到,你們的時候卻常是現成的。
Yesu ya ce dasu, “lokaci na bai yi ba tukuna, amma ku koyaushe lokacin ku ne.
7 世界不會恨你們,卻是恨我,因為我指證它的行為是邪惡的。
Duniya baza ta iya kin ku ba, amma ta ki ni saboda ina fadin cewa ayyukanta ba su da kyau.
8 你們上去過節罷! 我還不上去過這慶節,因為我的時候還沒有成熟。」
Ku ku je wurin idin, ni ba zan je wurin idin ba domin lokacina bai yi ba tukuna.
9 他說了這些話後,仍留在加里肋亞。
Bayan da ya gaya masu wadannan abubuwa, ya tsaya a cikin Gallili.
10 但他的弟兄們上去過節以後,他也去了,但不是明顯的,而是暗中去的。
Amma bayan da 'yan'uwansa su ka tafi wurin idin shi ma ya tafi, amma a asirce ba a fili ba.
11 在慶節中,猶太尋找他說: 「那人在那裡呢?」
Saboda Yahudawa suna neman sa a wurin idin, su na cewa “Ina yake?”
12 在群眾間對他發生了許多私議:有的說:「他是好人;」有的卻說: 「不,他在煽惑民眾。」
Akwai maganganu dayawa a kansa cikin taron. Wadansu suna cewa, “shi mutumin kirki ne.” Wadansu kuma suna cewa,”A'a yana karkatar da hankalin jama'a.”
13 但是,因為都怕猶太人,誰也不敢公開地講論他。
Amma duk da haka ba wanda ya yi magana a fili a kansa saboda suna jin tsoron Yahudawa.
14 慶節已過了一半,耶穌就上殿堂裏去施教教。
Sa'anda aka kai rabin idin, sai Yesu ya shiga cikin haikali ya fara koyarwa.
15 猶太人都驚訝說: 「這人沒有進過學,怎麼通曉經書呢?」
Yahudawa suna mamaki suna cewa,”Yaya aka yi wannan mutum ya sami ilimi dayawa haka? Shi kuwa bai je makaranta ba.”
16 耶穌回答他們說: 「我的教訓不是我的,而是派遣我來者的。
Yesu ya ba su amsa ya ce,”Koyarwata ba tawa ba ce, amma ta wanda ya aiko ni ce.”
17 誰若願意承行他的旨意,就會認出這教訓,是出於天主或由我自己而講的。
Idan wani yana so ya yi nufinsa, za ya gane koyarwannan ko daga wurin Allah ta zo, ko ko tawa ce ta kaina.
18 由自己而講的,是尋求自己的光榮;但誰若尋求派遣他來者的光榮,他便是誠實的,在他內沒有不義。
Ko wanene yake maganar kansa, yana neman darajar kansa kenan, amma ko wanene ya nemi darajar wanda ya aiko ni, wannan mutum mai gaskiya ne, babu rashin adalci a cikin sa.
19 梅瑟不是曾給你們頒布了法律嗎?但你們中卻沒有一人遵行法律;你們為什麼圖謀殺害我?」
Ba Musa ya baku dokoki ba? Amma duk da haka ba mai aikata dokokin. Me yasa ku ke so ku kashe ni?
20 群眾回答說: 「你附了魔;誰圖謀殺害你?」
Taron suka ba shi amsa, “Ka na da aljani. Wanene yake so ya kashe ka?”
21 耶穌回答說 :「我作了一件事,你們就都奇怪。
Yesu ya amsa ya ce masu, “Nayi aiki daya, dukan ku kuna mamaki da shi.
22 梅瑟曾給你們頒定了割損禮──其實並不是由梅瑟,而是由祖先開始的,因此,你們也在安息日給人行割損禮。
Musa ya baku kaciya, (ba kuwa daga Musa take ba, amma daga kakannin kakanni ta ke), kuma a ranar Asabar kukan yi wa mutum kaciya.
23 若是在安息日為滿全梅瑟的法律,人可受割損禮;那麼,為了我在安息日,使一個人完全恢復健康,你們就對我癹怒麼?
Idan mutum ya karbi kaciya ranar Asabar, domin kada a karya dokar Musa, don me kuka ji haushi na saboda na mai da mutum lafiyayye sarai ranar Asabar?
24 你們不要按照外表判斷,但要按照公義判斷。」
Kada ku yi shari'a ta ganin ido, amma ku yi shari'a mai adalci.”
25 於是有幾個耶路撒冷人說: 「這不是人們要圖謀殺害的人嗎?
Wadansun su daga Urushalima suka ce, “wannan ba shine wannan da suke nema su kashe ba?”
26 看,他放膽地講論,而沒有人對他說什麼,難道首長們也確認這人就是默西亞嗎?
Kuma duba, yana magana a fili, sannan ba wanda ya ce da shi komai. Ba zai yiwu ba mahukunta su sani cewa wannan Kristi ne, ko ba haka ba?
27 可是我們知道這人是那裡的;然而,當默西亞來時,卻沒有人知道他是那裏的。」
da haka, mun san inda wannan mutum ya fito. Amma sa'anda Kristi za ya zo, ba wanda zai san inda ya fito.”
28 於是耶穌在聖殿施教時大聲喊說: 「你們認識我也知道我是那裏的;但我不是由我自己而來,而是那真實者派遣我來的,你們卻不認識他;
Yesu yayi magana da karfi a haikali, yana koyarwa ya na cewa, “Kun san ni kuma kun san inda na fito. Ban zo domin kaina ba, amma wanda ya aiko ni mai gaskiya ne, ku kuwa baku san shi ba.
29 我認識他,因為我是出於他,是他派遣了我。」
Ni na san shi domin daga wurinsa na fito, kuma shine ya aiko ni.”
30 他們想捉住他,但沒有人向他下手,因為他的時辰還沒有到。
Suna kokari su kama shi, amma ba wanda ya iya sa masa hannu domin sa'arsa ba ta yi ba tukuna.
31 群眾中有許多人信了他,且說: 「默西亞來時,難道會行比這人更多的奇跡嗎?」
Duk da haka wadansu dayawa a cikin taron suka bada gaskiya gare shi suka ce,”Sa'anda Kristi ya zo, zai yi alamu fiye da wadanda wannan mutum ya yi?”
32 法利賽人聽見群眾對耶穌這樣議論紛紛,司祭長和法利賽人便派遣差役去捉拿他。
Farisawa suka ji tattarmukan suna yin rada a kan wadannan abubuwa game da Yesu, Sai manyan malamai da Farisawa su ka aika jami'ai su kama shi.
33 於是耶穌說: 「我和你們同在的時候不多了,我要回到派遣我來的那裡去。
Sa'annan Yesu yace ma su,” jimawa kadan ina tare ku, sa'annan in tafi wurin wanda ya aiko ni.
34 你們要找我卻找不著;而我所在的地,方你們也不能去。」
Za ku neme ni ba za ku same ni ba; inda na tafi, ba za ku iya zuwa ba.”
35 猶太便彼此說: 「這人要往那裏去,我們找不著他呢?難道他要往散居在希臘民中的猶太人那裡去,教訓希臘人麼?
Yahudawa fa su ka cewa junan su, “Ina wannan mutum zai je inda ba za mu iya samun sa ba? Ko za ya tafi wurin Helinawa na warwatsuwa ya koyawa Helinawa?
36 他所說: 『你們要找我,卻找不著;我的地方,你們也不能去』的這話是什麼意思?」
Wace kalma ya ke fadi haka, 'za ku neme ni amma ba za ku same ni ba; inda na tafi, ba za ku iya zuwa ba'?”
37 在慶節末日最隆重的那一天,耶穌站著大聲喊說: 「誰若渴,到我這裏來喝罷!
To a rana ta karshe, babbar rana ta idin, Yesu ya mike ya yi magana da karfi cewa, “Idan kowa yana jin kishi, ya zo wuri na ya sha.
38 凡信從我的,就如經上說: 從他的心中要流出活水的江河。」
Shi wanda ya bada gaskiya gare ni kamar yadda nassi ya fadi, daga cikin sa rafukan ruwa na rai za su bulbulo.”
39 他說這話,是指那信仰他的人將要領受的神;聖神還沒有賜下,因為耶穌還沒有受到光榮。
Amma ya fadi haka a kan Ruhu, wanda wadanda suka bada gaskiya gare shi za su karba; ba a ba da Ruhun ba tukuna, saboda ba a rigaya an daukaka Yesu ba.
40 群眾中有些人聽到了這些話,便說: 「這人真是那位先知。」
Wadansu a cikin taron, sa'anda suka ji wadannan kalmomi, suka ce, “Wannan lallai annabi ne.”
41 另有人說: 「這人是默西亞。」但也有人說: 「難道默西亞能來自加利肋亞嗎?
Wadansu suka ce, “Wannan Almasihu ne.” Amma wadansu suka ce, “Almasihu zai fito daga Gallili ne?
42 經上不是說:默西亞要出自達味的後裔,來自達味出生的村莊白冷嗎?」
Ba nassi ya ce Almasihu zai fito daga cikin dangin Dauda daga Baitalami ba, daga kauyen da Dauda ya fito?”
43 因此,為了耶穌的緣故,在群眾中起了紛爭。
Sai aka sami rabuwa a cikin taron saboda shi.
44 他們中有些人願捉拿他,但誰也沒有向他下手。
Da wadansun su sun kama shi, amma ba wanda ya sa masa hannu.
45 差役回到司祭長和法利賽人那裡;司祭長法利賽人問他們說: 「為什麼你們沒有把他帶來?」
Sa'annan jami'an suka dawo wurin manyan Fristoci da Farisawa, wadanda suka ce,” me yasa ba ku kawo shi ba?”
46 差役回答說: 「從來沒有一個人如此講話,像這人講話一樣。」
Jami'an su ka amsa, “Ba mutumin da ya taba yin magana kamar haka.”
47 法利賽人遂向他們說: 「難道你們也受了煽惑嗎?
Farisawa suka amsa masu, “kuma an karkatar da ku?
48 首長中或法利賽人中,難道有人信仰了他嗎?
Ko wani daga cikin mahukunta ya bada gaskiya gare shi, ko kuwa daga cikin Farisawa?
49 但是,這些不明白法律的群眾,是可詛咒的! 」
Amma wannan taro da basu san shari'a ba, la'anannu ne.”
50 他們中有一個,即先前曾來到耶穌那裏的尼苛德摩,遂向他們說: 「
Nikodimus ya ce masu, (shi wanda ya zo wurin Yesu da, daya daga cikin Farisawa),
51 如果不先聽取人的口供,和查明他所做的事,難道我們的法律就許定他的罪麼?」
“Ko shari'armu bata hana hukunta mutum ba, sai ta ji daga gare shi ta kuma san abin da ya aikata ba?”
52 他們回答他說:「難道你也是出自加利肋亞麼?你去查考,你就能知道:從加利肋亞不會出先知的。」
Suka amsa masa suka ce,”kai ma daga Galili ka fito? Ka yi bincike ka gani ba annanbin da zai fito daga Galili.”
53 然後,他們就各自回家去了。
Daga nan sai kowa ya tafi gidansa.

< 約翰福音 7 >