< 約翰福音 5 >

1 這些事後,正是猶太人的慶節,耶穌便上了耶路撒冷。
Bayan an ɗan jima, sai Yesu ya haura zuwa Urushalima don wani bikin Yahudawa.
2 在耶路撒冷靠近羊門有一個水池,希伯來語叫作貝特匝達,周圍有五個走廊。
To, a Urushalima akwai wani tafki kusa da Ƙofar Tumaki, wanda a yaren Arameyik ake kira Betesda an kuma kewaye shi da shirayi biyar.
3 在這些走廊內,躺著許多患病的,瞎眼的,瘸腿的,痳痺的,都在等候水動,
A nan naƙasassu da yawa sukan kwanta, makafi, guragu, shanyayyu.
4 因為有天使按時下到水池中,攪動池水;水動後,第一個下去的,無論他患什麼病,必會痊癒。
5 在那裏有一個人,患病已三十八年。
Akwai wani da yake nan ba shi da amfani shekara talatin da takwas.
6 耶穌看見這人躺在那裏,知道他已病了多時,就向他說: 「你願意痊癒嗎?」
Da Yesu ya gan shi kwance a can ya kuma sami labari cewa ya daɗe a wannan hali, sai ya tambaye shi, “Kana so ka warke?”
7 那人回答說:「主,我沒有人在水動的時候,把我放到水池中;我正到的時候,別人在我以前已經下去了。」
Marar amfanin nan ya ce, “Ranka yă daɗe, ba ni da wanda zai taimaka yă sa ni a cikin tafkin sa’ad da aka motsa ruwan. Yayinda nake ƙoƙarin shiga, sai wani yă riga ni.”
8 耶穌向他說: 「起來,拿起你的床,行走罷!」
Sai Yesu ya ce masa, “Tashi! Ɗauki tabarmarka ka yi tafiya.”
9 那人便立刻痊癒了,拿起自己的床,行走起來;那一天正是安息日。
Nan take mutumin ya warke; ya ɗauki tabarmarsa ya yi tafiya. A ranar da wannan ya faru ranar Asabbaci ce,
10 於是猶太人對那痊癒的人說: 「今天是安息日,不許你拿床。」
saboda haka kuwa Yahudawa suka ce wa mutumin da aka warkar, “Yau Asabbaci ne; doka ta hana ka ɗauki tabarmarka.”
11 他回答他們說: 「叫我痊癒了的那一位給我說: 拿起你的床,行走罷!」
Amma ya amsa ya ce, “Mutumin da ya warkar da ni shi ya ce mini, ‘Ɗauki tabarmarka ka yi tafiya.’”
12 他們就問他:「給你說拿起床來,而行走的那人是誰?」
Sai suka tambaye shi suka ce, “Wane ne wannan da ya ce maka ka ɗauke ta ka yi tafiya?”
13 那痊癒的人卻不知道他是誰,因為那地方人多,耶穌已躲開了。
Mutumin da aka warkar kuwa bai ma san ko wane ne ba ne, gama Yesu ya ɓace cikin taron da yake can.
14 事後耶鮓在聖殿裏遇見了,他便向他說: 「看,你已痊癒了,不要再犯罪,免得你遭遇更不幸的事。」
Daga baya Yesu ya same shi a haikali ya ce masa, “Ga shi, ka warke. Ka daina yin zunubi, in ba haka ba wani abin da ya fi wannan muni zai iya samunka.”
15 那人就去告訴猶太人: 使他痊癒的就是耶穌。
Sai mutumin ya je ya gaya wa Yahudawa cewa Yesu ne ya warkar da shi.
16 為此猶太人便開始迫害耶穌,因為他在安息日做這樣的事。
To, domin Yesu yana yin waɗannan abubuwa a ranar Asabbaci, sai Yahudawa suka tsananta masa.
17 耶穌遂向他們說: 「我父到現在一直工作,我也應該工作。」
Yesu ya ce musu, “Ubana yana cikin aikinsa kullum har yă zuwa wannan rana, haka ni ma, ina kan aiki.”
18 為此猶太人越發想要殺害他,因為他不但犯了安息日,而且又稱天主是自己的父,使自己與天主平等。
Don haka Yahudawa suka ƙara nema su kashe shi; ba don yă karya Asabbaci kawai ba, har ma yana ce Allah Ubansa ne, yana mai da kansa daidai da Allah.
19 耶穌於是回答他們說: 「我實實在在告訴你們: 子不能由自己作什麼,他看見父作什麼,才能作什麼;凡父所作的,子也照樣作,
Sai Yesu ya ba su wannan amsa cewa, “Gaskiya nake gaya muku, Ɗan ba ya iya yin kome da kansa; yana yin abin da ya ga Ubansa yake yi ne kawai, gama duk abin da Uban yake yi shi ne Ɗan ma yake yi.
20 因為父愛子,凡自己所作的都指示給他;並且還要把這些更大的工程指示給他,為叫你們驚奇。
Gama Uban yana ƙaunar Ɗan yana kuma nuna masa duk abin da yake yi. I, za ku kuwa yi mamaki, gama zai nuna masa abubuwan da suka fi waɗannan girma.
21 就如父喚起死者,使他們復生,照樣子也使他所願意的人復生。
Gama kamar yadda Uban yake tā da matattu yake kuma ba su rai, haka ma Ɗan yake ba da rai ga wanda ya ga dama.
22 父不審判任何人,但他把審判的全權交給了子,
Bugu da ƙari, Uban ba ya hukunta kowa, sai dai ya danƙa dukan hukunci a hannun Ɗan,
23 為叫眾人尊敬子如同尊敬父;不尊敬子的,就是不尊敬派遣他來的父。
don kowa yă girmama Ɗan kamar yadda yake girmama Uban. Wanda ba ya girmama Ɗan ba ya girmama Uban, da ya aiko shi ke nan.
24 我實實在在告訴你們: 聽我的話,相信派遣我來者的,便有永生,不受審判,而已出死入生。 (aiōnios g166)
“Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ya ji maganata ya kuma gaskata da wanda ya aiko ni yana da rai madawwami ba za a kuma hukunta shi ba; ya riga ya ƙetare daga mutuwa zuwa rai. (aiōnios g166)
25 我實實在在告訴你們: 時候要到,且現在就是,死者要聽見天主子的聲音,凡聽從的,就必生存。
Gaskiya nake gaya muku, lokaci yana zuwa har ma ya riga ya zo sa’ad da matattu za su ji muryar Ɗan Allah waɗanda kuwa suka ji za su rayu.
26 就如父是生命之源,照樣他也使子成為生命之源;
Gama kamar yadda Uban yana da rai a cikinsa, haka ya sa Ɗan yă kasance da rai a cikin kansa.
27 並且賜給他行審判的權柄,因為他是人子。
Ya kuma ba shi iko yă hukunta domin shi Ɗan Mutum ne.
28 你們不要驚奇這事,因為時候要到,那時,凡在墳墓裏的,都要聽見他的聲音,
“Kada ku yi mamakin wannan, gama lokaci yana zuwa da duk waɗanda suke cikin kaburbura za su ji muryarsa
29 而出來: 行過善的,復活進入生命;作過惡的,復活而受審判。
su kuma fito, waɗanda suka aikata nagarta za su tashi zuwa ga rai, waɗanda kuma suka aikata mugunta za su tashi zuwa ga hukunci.
30 我由我自己什麼也不能作;父怎樣告訴我,我就怎樣審判,所以我的審判是正義的,因為我不尋求我的旨意,而尋求那派遣我來者的旨意。」
Ni kaɗai dai ba na iya yin kome, ina shari’a ne bisa ga abin da na ji. Shari’ata kuwa mai adalci ce. Gama ba na neman gamsar da kaina, sai dai in gamshi shi wanda ya aiko ni.
31 「如果我為我自己作證,我的證據不足憑信;
“In na ba da shaida a kaina, shaidata ba gaskiya ba ce.
32 但另有一位為我作證,我知道他為我作的證足以憑信。
Akwai wani mai ba da shaida mai kyau a kaina, na kuma san cewa shaidarsa game da ni gaskiya ce.
33 你們曾派人到若翰那裏去,他就為真理作過證。
“Kun aika wajen Yohanna ya kuma yi shaida a kan gaskiya.
34 其實我並不需要人的證據,我提及這事,只是為叫你們得救。
Ba cewa ina neman shaidar mutum ba ne; sai dai na faɗi haka ne domin ku sami ceto.
35 若翰好比是一盞點著而發亮的燈,你們只一時高興享受了他的光明。
Yohanna fitila ne da ya ci ya kuma ba da haske, kun kuwa zaɓa ku ji daɗin haskensa na ɗan lokaci.
36 但我有比若翰更大的證據,即父所託付我要我完成的工程,就是我所行的這些工程,為我作證:證明是父派遣了我。
“Ina da shaidar da ta fi ta Yohanna ƙarfi. Gama aikin nan da Uba ya ba ni in kammala, wanda kuwa nake yi, yana ba da shaida cewa Uba ne ya aiko ni.
37 派遣我來的父,親自為我作證;你們重未聽見過他的聲音,也從未看見過他的儀容,
Uba da ya aiko ni kuwa kansa ya yi shaida game da ni. Ba ku taɓa jin muryarsa ko ganin siffarsa ba,
38 並且你們也沒有把他的話存留在心中,因為你們不相信他所派遣的那位。
maganarsa kuwa ba ta zama a cikinku, gama ba ku gaskata da wanda ya aiko ni ba.
39 你們查考經典,因為仔們認為其中有永生,正是這些經典為我作證; (aiōnios g166)
Kuna ta nazarin Nassosi da himma don kuna tsammani ta wurinsu ne kuna samun rai madawwami. Nassosin nan ne suke ba da shaida a kaina, (aiōnios g166)
40 但你們不願意到我這裏來,為獲得生命。」
duk da haka kun ƙi zuwa wurina domin ku sami rai.
41 我不求人的光榮;
“Ni ba na neman yabon mutane,
42 而且我認得你們,知道在你們內沒有天主的愛情。
na fa san ku. Na san cewa ba ku da ƙaunar Allah a cikin zukatanku.
43 我因父的名而來,你們卻不接納我;如果有人因自己的名而來,你們反而接納他。
Na zo a cikin sunan Ubana, ba ku kuwa karɓe ni ba; amma a ce wani dabam ya zo a cikin sunan kansa, za ku karɓe shi.
44 你們既然彼此尋求光榮,而不尋求出於惟一天主的光榮,你們怎麼能相信我呢?
Ta yaya za ku gaskata in kuna neman yabon junanku, ba kwa kuwa yin ƙoƙarin neman yabon da yake zuwa daga Allah Makaɗaici?
45 不要想我要在父面前控告你們;有一位控告你們的,就是你們所寄望的梅瑟。
“Kada fa ku yi tsammani zan yi ƙararku wurin Uba. Akwai mai yin ƙararku, shi ne Musa, wanda kuke dogara da shi.
46 若是你們相梅瑟,必會相信我,因為他是指著我而寫的。
Da a ce kun gaskata da Musa, da kun gaskata ni, domin ya rubuta game da ni.
47 如果你們不相信他所寫的,怎會相信我的話呢?」
Amma da yake ba ku gaskata abin da ya rubuta ba, yaya za ku gaskata maganata?”

< 約翰福音 5 >