< 約伯記 4 >
Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
“In wani ya yi maka magana, za ka ji haushi? Amma wa zai iya yin shiru?
Ka tuna yadda ka yi wa mutane da yawa magana, yadda ka ƙarfafa hannuwa marasa ƙarfi.
Maganarka ta ƙarfafa waɗanda suka yi tuntuɓe; ka ƙarfafa gwiwoyin da suka rasa ƙarfinsu.
5 但是現今災禍一臨於你,你就萎靡不振;一接觸你,你就沮喪失意。
Amma yanzu wahala ta zo maka, sai ka karaya; wahala ta sa ka rikice.
6 你敬畏天主之情,豈不是你的依靠﹖你完善的行為,豈不是你的希望﹖
Ashe bai kamata ka dogara ga Allahnka ba, amincinka kuma yă zama begenka?
“Ka duba ka gani yanzu. Wane marar laifi ne ya taɓa hallaka? Ko an taɓa hallaka masu adalci?
8 照我所見:那播種邪惡的,必收邪惡;散佈毒害的,必收毒害。
Na kula cewa waɗanda suke huɗa gonar mugunta, da waɗanda suke shuka mugunta, su ne suke girbe mugunta.
9 天主一噓氣,他們即滅亡;一發怒氣,他們即消失。
A sa’a ɗaya Allah yake hallaka su, cikin fushinsa yakan hallaka su.
Zakoki suna ruri suna gurnani; duk da haka an karya haƙoran manyan zakoki.
Zakoki suna mutuwa domin ba dabbar da za su kashe su ci,’ya’yan zakanya kuma sun watse.
“Asirce aka gaya mini maganan nan, da ƙyar kunnuwana suka iya ji.
Cikin mafarki da tsakar dare, lokacin kowa yana zurfin barci, na sami saƙon nan.
Tsoro da fargaba suka kama ni har duk ƙasusuwan jikina suka yi ta rawa.
Wani iska ya taɓa mini fuska, sai tsigar jikina ta tashi.
16 他停立不動,但我不能辨其形狀;我面前出現形影,我聽見細微的聲音:
Ya tsaya cik, amma ban iya sani ko mene ne ba. Wani abu ya tsaya a gabana, na kuma ji murya.
17 人豈能在天主前自以為義﹖在造他者前,自以為潔﹖
‘Ko zai yiwu mutum yă fi Allah adalci, ko kuma mutum yă fi wanda ya halicce shi tsarki?
18 看,他的僕役,他還不信;他的使者,他還歸罪,
In Allah bai yarda da bayinsa ba, in ya sami mala’ikunsa da laifi,
19 何況那以泥屋為居所,以塵土為基礎的人! 他們為人踐踏,有如蠹蟲;
to, su wane ne mutane masu zama a gidan da aka yi da laka, waɗanda da ƙura aka yi harsashensu, waɗanda za a iya murƙushe su kamar asu!
Tsakanin safe da yamma mai yiwuwa ne ragargaza su; farat ɗaya, su mutu har abada.
Ba a tuge igiyar tentinsu, don su mutu ba tare da hikima ba?’