< 約伯記 15 >

1 特曼人厄里法次又發言說:
Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
2 智者豈能以虛言作答﹖豈能以東風果腹﹖
“Mutum mai hikima zai amsa da surutai marasa kan gado ko yă cika cikinsa da iskar gabas?
3 豈能以無益的廢話,無濟於事的言詞來辯護﹖
Ko zai yi gardama da maganganun wofi maganganu marasa amfani?
4 不但如此,而且你還廢除了敬畏天主之情,斷絕了在他面前的默禱。
Amma ka ma rena Allah ka hana a yi addu’a gare shi.
5 其實,是你的罪惡教導你說話,叫你的口舌詭辯。
Zunubanka ne suke gaya maka abin da za ka ce; kana magana kamar mai wayo.
6 定你罪的,是你的口而不是我,是你的口唇作證控告你。
Bakinka zai kai ka yă baro, ba nawa ba; maganar bakinka za tă juya a kanka.
7 你豈是第一個出生的人﹖在山嶽未有之前,你豈已誕生﹖
“Kai ne mutum na farko da aka fara haihuwa? Ko kai ne aka fara halitta kafin tuddai?
8 難道你聽見了天主的秘旨,把持著智慧﹖
Kana sauraron shawarar Allah? Ko kana gani kai kaɗai ne mai hikima?
9 有什麼事,只有你知,而我們不知;只有你明瞭,而我們不明瞭﹖
Me ka sani da ba mu sani ba? Wane fahimi kake da shi da ba mu da shi?
10 我們之中也有白頭老人,年紀比你父親還大。
Masu furfura da tsofaffi suna gefenmu mutanen da sun girme babanka.
11 天主的安慰,和向你說的溫和的話,你以為還太少嗎﹖
Ta’aziyyar Allah ba tă ishe ka ba. Maganarsa mai laushi ba tă ishe ka ba?
12 你為何讓你的感情控制著你﹖你的眼為何冒火,
Don me ka bar zuciyarka ta kwashe ka, kuma don me idanunka suke haske,
13 竟向天主發怒,開口說出這樣的話﹖
har kake fushi da Allah kake kuma faɗar waɗannan maganganu daga bakinka?
14 人算什麼而敢自稱潔淨,婦女所生的敢自稱正直﹖
“Mene ne mutum, har da zai zama da tsarki, ko kuma mace ta haife shi, har yă iya zama mai adalci?
15 他連自己的聖者,還不信賴;在他眼中,連蒼天也不純潔,
In Allah bai nuna amincewa ga tsarkakansa ba, in har sammai ba su da tsarki a idonsa,
16 何況一個墮落可憎,飲惡如水的人。
mutum fa, wanda yake da mugunta da lalacewa, wanda yake shan mugunta kamar ruwa!
17 我要告訴你,你且聽我說;我要說明我的經驗,
“Ka saurare ni, zan kuma yi maka bayani; bari in gaya maka abin da na gani,
18 即賢哲所傳授,和祖先未曾隱瞞的事:──
abin da masu hikima suka ce, ba tare da sun ɓoye wani abu da suka samu daga wurin iyayensu ba
19 這地方原只賜給了他們,尚無一個外方人從他們中間經過。──
(waɗanda su ne masu ƙasar kafin baƙi su shigo ƙasar).
20 惡人一生飽受苦惱,壽數已給暴君限定;
Dukan kwanakin ransa mugu yana shan wahala, wahala kaɗai zai yi ta sha.
21 恐怖之聲常在他耳中,平靜時匪徒也來侵擾。
Ƙara mai bantsoro za tă cika kunnuwansa’yan fashi za su kai masa hari.
22 他不相信還能脫離黑暗,只等待遭受刀劍之害,
Yana jin tsoron duhu domin za a kashe shi da takobi.
23 注定作為鷹鳥的食物,自知大難業已臨頭。
Yana ta yawo, abinci don ungulaye; ya san ranar duhu tana kusa.
24 黑暗的日子使他恐怖,困苦艱難跟隨著他,好像準備廝殺的君王。
Ɓacin rai da baƙin ciki sun cika shi, kamar sarkin da yake shirin yaƙi,
25 因為他曾伸手反抗過天主,向全能者傲慢逞強過;
domin ya nuna wa Allah yatsa ya rena Allah Maɗaukaki,
26 以伸直的頸項,以堅厚的盾背攻擊過天主。
ya tasar masa da faɗa da garkuwa mai kauri da kuma ƙarfi.
27 他的臉蓋滿了脂油,他的腰積滿了肥肉。
“Ko da yake fuskarsa ta cika da kumatu kuma yana da tsoka ko’ina,
28 他住在荒涼的城內,住在無人居留,行將化為廢墟的屋中。
zai yi gādon garuruwan da suka lalace, da kuma gidajen da ba wanda yake zama a ciki, gidajen da sun zama tarkace.
29 他不能富有,所有的財富也不能久存,也決不能向地下生根。
Ba zai sāke zama mai arziki ba, dukiyarsa ba za tă dawwama ba, abin da ya mallaka kuma ba zai bazu a ƙasar ba.
30 他脫離不了黑暗,火燄要灼乾他的嫩芽,暴風要吹去他的花朵。
Ba zai tsere wa duhu ba; wuta za tă ƙona rassansa, kuma numfashi daga bakin Allah zai hallaka shi.
31 別依恃枝椏已長大,應知這都是空虛;
Kada yă ruɗi kansa ta wurin dogara ga abin da ba shi da amfani domin ba zai samu wani abu ba daga ciki.
32 未到時日,已經凋謝,枝葉再不發綠。
Kafin lokacinsa yă cika, za a gama biyansa duka, kuma rassansa ba za su ba da amfani ba.
33 有如葡萄未熟即被打下,橄欖開花即被搖落,
Zai zama kamar itacen inabi wanda’ya’yansa suka kakkaɓe kafin su nuna, kamar itacen zaitun zai zubar da furensa.
34 因為惡人的家室必要絕嗣,火要燒盡受賄者的帳幕。
Gama marasa tsoron Allah za su zama marasa ba da’ya’ya, wuta kuma za tă ƙona tenti na masu son cin hanci.
35 他們所懷的是邪惡,所生的是罪孽;心胸懷念的,無非是欺詐。
Suna yin cikin rikici su kuma haifi mugunta; cikinsu yana cike da ruɗami.”

< 約伯記 15 >