< 耶利米書 44 >

1 以下是關於住在埃及地,住在米革多耳,塔黑培乃斯、諾夫和帕特洛斯地的一切猶太人,傳給耶肋米亞的話:「
Wannan maganata zo wa Irmiya game da dukan Yahudawa masu zama a Masar ta Ƙasa, a Migdol, Tafanes da Memfis, da kuma a Masar ta Bisa.
2 萬軍的上主,以色列的天主這樣說:你們看見了我對耶路撒冷和猶大各城召來的一切災禍,看,今日已成為無人居住的曠野。
“Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa kun ga masifa mai girmar da na kawo a kan Urushalima da kuma a kan dukan garuruwan Yahuda. A yau sun zama hamada da kuma kango
3 這是因為他們做了惹我動怒的惡事,向他們、你們和你們的祖先從不認識的外方神祇焚香敬拜;
saboda muguntar da suka aikata. Sun tsokane ni na yi fushi ta wurin ƙone turare da kuma ta wurin bauta wa waɗansu allolin da su ko ku ko kakanninku ba su taɓa sani ba.
4 雖然我早就不斷洽你們派遣我所有的先知僕人們說:你們切不可做我所憎恨的可惡之事!
Sau da sau na aiki bayina annabawa, waɗanda suka ce, ‘Kada ku yi wannan abin ƙyama da na ƙi!’
5 他們卻沒有側耳聽從,沒有放棄他們向外方神祇焚香的惡習。
Amma ba su saurara ko su kasa kunne ba; ba su juye daga muguntarsu ko su daina ƙone turare wa waɗansu alloli ba.
6 於是我的憤恨如火發作,焚毀了猶大城市和耶路撒冷的街市,使她成為荒涼的曠野,有如今日。
Saboda haka, fushina mai ƙuna ya fāɗo a kan garuruwan Yahuda da kuma titunan Urushalima na kuma mai da su kufai da suke a yau.
7 現在,上主萬軍的天主以色列的天主這樣說:為什麼你們招來這樣大的災禍,加害自己,使你們中的男人、婦女、幼童、嬰兒,全由猶大滅絕,不給你們留下遺民﹖
“To, ga abin da Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa don me kuka kawo irin masifa mai girma haka a kanku ta wurin warewa daga Yahuda maza da mata, yara da jarirai, kun kuma bar kanku babu raguwa?
8 為什麼你們做惹我動怒的事,向你們來寄居的埃及地的外方神祇獻香,使你們自遭滅亡,成為普世萬民詛咒和恥笑的對象﹖
Me ya sa kuka tsokane ni in yi fushi saboda abin da hannuwanku suka yi, kuna ƙone turare wa waɗansu alloli a Masar, inda kuka zo don ku zauna? Za ku hallakar da kanku ku kuma mai da kanku abin la’ana da abin zargi da abin ba’a a cikin dukan al’umman duniya.
9 難道你們忘了你們的祖先、猶大君王和他們的妻妾、你們自己和你們的女人,在猶大地和耶路撒冷街上犯的種種罪惡﹖
Kun manta mugayen ayyukan kakanninku, da na sarakuna da sarauniyoyin Yahuda da mugayen ayyukanku, da na matanku a cikin Yahuda da kan titunan Urushalima?
10 他們直到今日尚不後悔,也不畏懼,更不履行我給你們和你們的祖先頒布的法律和誡命。
Har yă zuwa yau ba su ƙasƙantar da kansu ko su nuna bangirma, ko su kiyaye dokata da ƙa’idodin da na sa a gabanku da kakanninku ba.
11 為此,萬軍的上主,以色列的天主這樣說:看,我面向你們,是為降災,消滅整個猶大。
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa na ƙudura in aukar muku da masifa in kuma hallaka dukan Yahuda.
12 凡決意往埃及地去,要六那裏寄居的猶大遺民,我必要剷除,叫他們全死在埃及地,喪身刀下,饑餓而死;不分老幼都死於刀劍、饑荒,飽受憎恨、厭惡、詛咒和侮辱。
Zan ɗauke raguwar Yahuda waɗanda suka ƙudurta su je Masar su zauna a can. Duk za su hallaka a Masar; za su mutu ta wurin takobi ko su mutu da yunwa. Daga ƙarami zuwa babba, za su mutu ta wurin takobi ko yunwa. Za su zama abin zarge da abin tsoro, abin la’ana da abin ba’a.
13 我必以刀劍、饑荒和瘟疫懲罰住在埃及地的人,如懲罰耶路撒冷一樣,
Zan hukunta waɗanda suke zama a Masar da takobi, yunwa da annoba, yadda na hukunta Urushalima.
14 使前往寄居埃及的猶大遺民,無一能幸免逃脫,返回他們所渴望回去居住的猶大地;除少數脫身者外,他們不會回來了。」
Babu wani daga raguwar Yahuda wanda ya tafi Masar da zai kuɓuta ko ya tsira har ya komo zuwa ƙasar Yahuda, wadda za su yi marmari su komo su zauna; babu wani da zai komo sai dai’yan gudun hijira.”
15 於是凡知道自己的女人曾向外方神祇燒香的人,和一大群環立在旁的婦女,以及住在埃及地和帕特洛斯的全體人民,就答覆耶肋米亞說:「
Sai dukan mazan da suka san cewa matansu suna ƙone turare wa waɗansu alloli, tare da dukan matan da suke a nan babban taro, da kuma dukan mutanen da suke zama a Masar ta Ƙasa da ta Bisa, suka ce wa Irmiya,
16 你奉上主的名對我們說的話,我們不願聽從;
“Ba za mu saurari saƙon da ka yi mana magana a sunan Ubangiji ba!
17 至於凡出自我們口中的話,我們必定實行,給天后焚香奠酒,如同我們、我們的祖先、君王及首領,在猶大城和耶路撒冷街上所做的一樣;那時我們都豐衣足食,安享太平,不見災禍。
Lalle za mu aikata duk abin da muka ce za mu yi. Za mu ƙone turare ga Sarauniyar Sama za mu kuma miƙa hadayun sha gare ta kamar dai yadda mu da kakanninmu, sarakunanmu da fadawanmu muka yi a garuruwan Yahuda da kuma kan titunan Urushalima. A lokacin muna da abinci a yalwace muna kuma da arziki ba mu kuma da wata damuwa.
18 可是,自從我們斷絕向天后獻香,不給她奠酒以來,我們就什麼也缺乏,死於刀劍和饑荒。
Amma tun da muka daina ƙone turare ga Sarauniyar Sama da kuma miƙa mata hadayun sha, muka rasa kome muna ta mutuwa ta wurin takobi da yunwa.”
19 至於我們的女人向天后焚香奠酒,又那能沒有我們男人的同意,依照她的形狀,給她備製祭餅,向她奠酒呢﹖」
Matan suka ƙara da cewa, “Sa’ad da muka ƙone turare ga Sarauniyar Sama muka kuma miƙa mata hadayun sha, mazanmu ba su san muna yin waina kamar siffarta muna kuma miƙa mata hadayun sha ba?”
20 耶肋米亞便對全體人民,對答覆他的男人和婦女以及所有的人說:「
Sai Irmiya ya ce wa dukan mutanen, maza da mata, waɗanda suke ba shi amsa,
21 難道你們、你們的祖先、君王、首領和地方上的人民,在猶大城和耶路冷街上燒香的事,上主就不記得了,再也不懷念在心了嗎﹖
“Ubangiji bai tuna ya kuma yi tunani game da turaren da aka ƙone a garuruwan Yahuda da kan titunan Urushalima wanda ku da kakanninku, sarakunanku da fadawanku da mutanen ƙasar ba ne?
22 上主再也不能容忍你們邪惡的行為,和你們做的可惡的事,為此你們的土地變成了荒野,成了驚愕和詛咒的對象,無人居住,有如今日:
Sa’ad da Ubangiji bai iya jurewa da mugayen ayyukanku da kuma abubuwa banƙyama da kuka aikata ba, sai ƙasarku ta zama abin la’ana da kufai babu mazauna yadda yake a yau.
23 就因為你們燒香得罪了上主,不聽上主的勸告,不覆行他的法律、誡命和法令,纔給你們招來了像今日這樣的災禍。」
Domin kun ƙone turare kuka kuma yi wa Ubangiji zunubi ba ku kuma yi masa biyayya ko ku kiyaye dokarsa ko ƙa’idodinsa ko farillansa ba, wannan masifa ta aukar muku, yadda yanzu kuka gani.”
24 以後,耶肋米亞又對全體人民和全體婦女說:「凡在埃及境內的猶大人,請聽上主的話!
Sai Irmiya ya ce wa dukan mutane, har da mata, “Ku saurari maganar Ubangiji, dukanku mutanen Yahuda a Masar.
25 萬軍的上主,以色列的天主這樣說:你們和你們的女人都要親手做你們親口說的事;你們說:我們決意實踐我們許的誓願,向天后燒香奠酒。你們就實踐你們的誓願,舉行你們的奠祭罷!
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ku da matanku kun nuna ta wurin ayyukanku abin da kuka yi alkawari sa’ad da kuka ce, ‘Lalle za mu yi abin da muka yi alkawari na ƙone turare da kuma miƙa hadayun sha ga Sarauniyar Sama.’ “To, sai ku ci gaba, ku aikata abin da kuka yi alkawari! Ku cika alkawarinku!
26 但是,所有住在埃及地的猶大人,你們且聽上主的話:看,我以我偉大的名起誓──上主說:在埃及全地任何猶大人的口中,不會再呼號我名說:我主上主永在!
Amma ku ji maganar Ubangiji, dukan Yahudawan da suke zama a Masar, ‘Na rantse da sunana,’ in ji Ubangiji, ‘cewa babu wani daga Yahuda wanda yake zama a ko’ina a Masar zai ƙara kira bisa sunana ko ya rantse ya ce, “Muddin Ubangiji Mai Iko Duka yana raye.”
27 看,我注視他們,是為降災,不是為賜福,使在埃及地所有的猶大人,都死於刀劍饑荒,徹底消滅;
Gama ina lura da su don lahani, ba alheri ba; mutanen Yahuda da suke a Masar za su hallaka ta wurin takobi da yunwa sai dukansu sun hallaka.
28 即使有逃脫刀劍,從埃及地回到猶大的人,為數也寥寥無幾。到埃及地來寄居的全體猶大遺民,終於會知道:誰的話要應驗,是我的還是他們的。
Waɗanda suka kuɓuta wa takobi suka komo zuwa ƙasar Yahuda daga Masar za su zama kima kawai. Sa’an nan dukan raguwar Yahuda waɗanda suka zo don su yi zama a Masar za su san maganar wane ne za tă tabbata, tawa ko tasu.
29 這為你們是個徵兆──上主的斷語──就在這地方我要懲罰你們,叫你們知道:我對你們要降災的話,必要絕對應驗。
“‘Wannan zai zama alama a gare ku cewa zan hukunta ku a wannan wuri,’ in ji Ubangiji, ‘saboda ku san cewa barazanata ta lahani a kanku tabbatacce za tă cika.’
30 上主這樣說:看,我必將埃及王法郎曷斐辣交在他仇人和圖謀他性命的人手中,就如我曾將猶大王漆德克雅,交在他仇人和圖謀他性命的巴比倫王拿步高的手中一樣。」
Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Zan bayar da Fir’auna Hofra sarkin Masar ga abokan gābansa waɗanda suke neman ransa, kamar yadda na ba da Zedekiya sarkin Yahuda ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, abokin gāban da ya nemi ransa.’”

< 耶利米書 44 >