< 耶利米書 31 >

1 時候────將作以色列各宗族的天主,他們將作我的人民。
“A lokacin nan, zan zama Allah na dukan kabilan Isra’ila, za su kuma zama mutanena,” in ji Ubangiji.
2 上主這樣說:逃脫了刀劍的,在曠野中找到了聖寵遇;以色列前來自己巿身的地方。
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Mutanen da suka tsere wa takobi za su sami tagomashi a hamada; zan zo don in ba da hutu ga Isra’ila.”
3 上主自遠處顯示給她說:我愛妳,我永遠愛妳,因此我給妳留了我的仁慈;
Ubangiji ya bayyana mana a dā, yana cewa, “Na ƙaunace ku da madawwamiyar ƙauna; na janye ku da ƙauna marar iyaka.
4 我要再修建妳,而妳必建再建立起來;妳必再帶上妳的小鼓,出來歡樂哥舞;
Zan sāke gina ki za ki kuwa sāke ginuwa, ya Budurwar Isra’ila. Za ki kuma ɗauki ganganki ki fita don ki yi rawa da masu farin ciki.
5 再在撒馬黎雅山上栽種葡萄,栽種培埴,必有收穫;
Za ki sāke dasa gonakin inabi a kan tussan Samariya; manoma za su yi shuka a kansu su kuma ji daɗin amfaninsu.
6 因為終有一天,守望的人要在厄弗辣因山上嘁說:起來,讓我們上熙雍去,到上主我們的天主那裏去!
Za a yi ranar da matsara za su tā da murya a kan tuddan Efraim su ce, ‘Ku zo, bari mu haura Sihiyona, zuwa wurin Ubangiji Allahnmu.’”
7 因為上主這樣說:你們應為雅各伯歡呼,向為首的民族喝采,傳揚稱讚說:上主救了自己的百姓,以色列的遺民。
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ku rera don farin ciki wa Yaƙub; ku yi sowa don al’ummai da suke nesa. Ka sa a ji yabanku, ku kuma ce, ‘Ya Ubangiji ka ceci mutanenka, raguwar Isra’ila.’
8 看,我由北地引他們歸來,從大地的盡頭召集他們,其中有瞎子,有跛子,有懷孕的和正在生產的,形成一大隊回到這裏來。
Ga shi, zan kawo su daga ƙasar arewa in tattara su daga iyakar duniya. A cikinsu makafi da guragu za su kasance, mata masu ciki da matan da suke naƙuda; jama’a mai yawan gaske za su komo.
9 他們含淚前行,我卻撫引導,領他們踏上不會跌倒的坦途,來到溪流旁,因為我是以色列的慈父,厄弗辣因是我的長子。
Za su zo da kuka; za su yi addu’a yayinda nake komo da su. Zan bishe su kusa da rafuffukan ruwa a miƙaƙƙiyar hanya inda ba za su yi tuntuɓe ba, domin ni ne mahaifin Isra’ila, Efraim kuma ɗan farina ne.
10 萬民! 請聽上主的話,向遙遠的海島宣傳說:那
“Ku ji maganar Ubangiji, ya al’ummai; ku yi shelarta a gaban teku masu nesa cewa, ‘Shi wanda ya watsar da Isra’ila zai tattara su zai kuma lura da garkensa kamar makiyayi.’
11 那昔日驅散以色列的,再要來聚集他們,看守他們像牧童看守自己的羊群。11. 因為上主必拯救雅各伯,比他更強者的手中將他們贖回。
Gama Ubangiji zai fanshi Yaƙub zai cece su daga hannun waɗanda suka fi su ƙarfi.
12 他們將來前來,在熙雍山巔歡呼,湧向上主的美物,飽享穀、麥、酒、油,子牛小羊;他們的心靈好像受灌溉的田園,再也不感憔悴。
Za su zo su yi sowa don farin ciki a ƙwanƙolin Sihiyona; za su yi farin ciki cikin yalwar Ubangiji hatsi, sabon ruwan inabi da mai,’ya’yan garken tumaki da na shanu. Za su zama kamar gonar da aka yi wa banruwa, ba za su ƙara yin baƙin ciki ba.
13 那時,處女必歡欣鼓舞,老幼必相聚同樂,因為我將使的悲哀變成喜樂,仗他們由自己的憂苦中獲得安慰歡樂;
’Yan mata za su yi rawa su kuma yi murna, haka ma samari da tsofaffi. Zan mai da makokinsu farin ciki; zan ta’azantar da su in kuma sa su yi farin ciki a maimakon baƙin ciki.
14 我將以肥脂滋潤司祭的心靈,以美物飽飫我的人民──上主的斷語。
Zan ƙosar da firistoci da yalwa, mutanena kuma za su cika da yalwa,” in ji Ubangiji.
15 上主這樣說:「聽! 在辣瑪有嘆息聲,酸辛哭泣;辣黑耳悲悼自己的兒子,不願接受安慰,因為他們已不存在了! 」
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “An ji murya daga Rama, makoki da kuka mai zafi, Rahila tana kuka domin’ya’yanta ta kuma ƙi a ta’azantar da ita domin’ya’yanta ba su.”
16 上主這樣說:「要止往痛哭,不再流淚,因為你的苦終必有報──上主的斷語──他們必會由敵地歸來!
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Hana muryarki kuka da kuma idanunki hawaye, gama za a sāka wa aikinki,” in ji Ubangiji. “Za su komo daga ƙasar abokin gāba.
17 你們的前途大有希望──上主的斷語──你的子孫都要歸回自己的疆域。
Saboda haka akwai sa zuciya domin nan gaba,” in ji Ubangiji. “’Ya’yanki za su komo ƙasarsu.
18 我實在聽到厄弗辣因在悲歎說:你懲罰了我,我受了杖搫,有如一頭不馴服的公牛犢;你使我歸來,我必歸來,因為你是上主,我的天主x。
“Tabbatacce na ji gurnanin Efraim yana cewa, ‘Ka hore ni kamar ɗan maraƙi mai ƙin ji, na kuwa horu. Ka mayar da ni, zan kuwa dawo, domin kai ne Ubangiji Allahna.
19 的確,我離棄你以後,我已後悔;在覺悟以後,我拍腿自慚自愧,因為我又染上了我少年時的恥辱。
Bayan na kauce, sai na tuba; bayan na gane, sai na sunkuyar da kaina. Na ji kunya da ƙasƙanci domin ina ɗauke da kunyar ƙuruciyata.’
20 厄弗辣因豈? 是我的寵兒,我鍾愛嬌子﹖因為我幾時恐嚇他,反倒更顧念他;對他我五內感動,不得不大施愛憐──上主的斷語」。
Efraim ba ƙaunataccen ɗana ba ne, ɗan da nake jin daɗinsa? Ko da yake sau da dama ina maganar gāba a kansa, duk da haka nakan tuna da shi. Saboda haka zuciyata tana marmarinsa; ina da jinƙai mai girma dominsa,” in ji Ubangiji.
21 請你給自己樹立路程碑,設置指路牌,細心回想你走的路線,以往你走過的大道;以色列處女! 回到妳自己的城邑。
“Ki kafa alamun hanya; ki sa shaidun bishewa. Ki lura da babbar hanya da kyau, hanyar da kika bi. Ki komo, ya Budurwar Isra’ila, ki komo zuwa garuruwanki.
22 妳要流浪到幾時﹖叛逆的女兒! 因為上主在地上正在創造一件新事:女人包圍男人。
Har yaushe za ki yi ta yawo, Ya’ya marar aminci? Ubangiji zai ƙirƙiro sabon abu a duniya mace za tă kewaye namiji.”
23 萬軍的上主,以色列的天主這樣說:「當我轉變他們的命運時,在猶大地和她城市中的人,還要用這話祝賀說:正義的所在,神聖的山嶺! 願上主祝福你。
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa, “Sa’ad da na komo da su daga bauta mutane a ƙasar Yahuda da cikin garuruwanta za su sāke yi amfani da waɗannan kalmomi. ‘Ubangiji ya albarkace ka, ya mazauni mai adalci, ya tsarkakan dutse.’
24 猶大和她各城中的人,農夫和隨羊遷徒的人,將要同住在那裏,
Mutane za su zauna tare a Yahuda da dukan garuruwansa, manoma da waɗanda suke yawo da garkunansu.
25 因為我要振作困乏的心靈,飽飫一切苦悶的心靈。──
Zan wartsake waɗanda suka gaji in kuma ƙosar da waɗanda ransu ya yi yaushi.”
26 至此,我醒來了,我看見了,我的睡眠為我實在甘甜。
A kan wannan na farka na duba kewaye. Barcina ya yi mini daɗi.
27 ──上主的斷語──我要給以色列家和猶大家播散人種和獸種;
“Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan kafa gidan Isra’ila da gidan Yahuda da’ya’yan mutane da na dabbobi.
28 就如往昔我曾監視他們,為將他們拔除、破壞、推翻、毀滅、損害;同樣,日後我必要監視他們、為將他們建設、栽培──上主的斷語──
Kamar yadda na lura da su don su tumɓuke su kuma rusar, su lalatar, su hallaka su kuma kawo masifa, haka zan lura da su don su gina su kuma dasa,” in ji Ubangiji.
29 在那時裏,人必不再說:「祖先吃了酸葡萄,子孫的牙齒也要酸軟」。
“A waɗannan kwanaki mutane ba za su ƙara ce, “‘Ubanni suka ci’ya’yan inabi masu tsami, haƙoran’ya’ya suka mutu ba.’
30 不,各人只因自己的的罪惡而死;只有吃酸葡萄的人,自己的牙齒才酸軟。
A maimako, kowa zai mutu saboda zunubinsa; duk wanda ya ci’ya’yan inabi masu tsami, haƙoransa ne za su mutu.
31 看,時日將到──上主的斷語──我必要與叵家和猶大家訂立新約,
“Lokaci yana zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan yi sabon alkawari da gidan Isra’ila da kuma gidan Yahuda.
32 不像我昔日──握住他們的手,引他們出離埃及時──與他們的祖先訂立盟約;雖然我是他們的夫君,他們已自行破壞了我這盟約──上主的斷語──
Ba zai zama kamar alkawarin da na yi da kakanni kakanninsu ba sa’ad da na kama su da hannu na bishe su daga Masar, domin sun take alkawarina, ko da yake na zama miji a gare su,” in ji Ubangiji.
33 我願在那些時日,與叵家訂立的盟約──上主的斷語──就是:我要將我的法律放在他們的肺腑裏,寫在他們的心頭上;我要作他們的天主,他們要作我的人民。
“Ga alkawarin da zan yi da gidan Isra’ila bayan wannan lokaci,” in ji Ubangiji. “Zan sa dokata a tunaninsu in kuma rubuta ta a zukatansu. Zan zama Allahnsu, za su kuma zama mutanena.
34 那時,誰也不教訓自己的近人或弟兄說:「你們該認識上主」,因為不論大小,人人都必認識我──上主的斷語──因為我要寬恕他們的過犯,不再記憶他們的罪惡。
Mutum ba zai ƙara koya wa maƙwabci ba, ko ya koya wa ɗan’uwansa cewa, ‘Ka san Ubangiji,’ domin duk za su san ni, daga ƙaraminsu har zuwa babba,” in ji Ubangiji. “Gama zan gafarta muguntarsu ba zan kuwa ƙara tuna da zunubansu ba.”
35 那指定太陽照耀白日規定月亮星辰照耀黑夜,撥動海洋使波濤怒號,號稱「萬軍的上主」
Ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya kafa rana don tă yi haske a yini shi da ya sa wata da taurari su yi haske da dare, shi da yake dama teku don raƙuman ruwansa su yi ruri Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa.
36 假若這些規定已由我面前消失──上主的斷語──以色列種族在我面前也就永不再是一個民族。
“In dai wannan kafaffiyar ƙa’ida ta daina aiki a gabana,” in ji Ubangiji, “to, sai zuriyar Isra’ila ta daina zama al’umma a gabana.”
37 上主這樣說:假若能測量在上的諸天,能探察在下大地的基礎,我也就因他們所做的一切,拋棄整個以色列種族──上主的斷語」。
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “In a iya auna sammai a kuma bincike tushen duniya a ƙarƙas to, sai in ƙi dukan zuriyar Isra’ila ke nan saboda dukan abin da suka yi,” in ji Ubangiji.
38 看,時日將到──上主的斷語──上主的城市必要重建,不佰自哈納乃布堡直到角門,
“Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da za a sāke gina wannan birni domina daga Hasumiyar Hananel zuwa Ƙofar Kusurwa.
39 而且測量的繩墨還要向外伸展,直到加勒布丘,再轉向哥阿;
Ma’auni zai miƙe daga can ya nausa kai tsaye zuwa tudun Gareb sa’an nan ya juya zuwa Gowa.
40 滿了屍首和灰燼的整個山谷,以及直到克德隆溪流和東邊馬門角旁所有木田地,都將祝聖給上主,永不再遭受」。
Dukan kwarin da ake zubar da toka da kuma gawawwaki, da dukan lambatun da suke can har zuwa Kwarin Kidron a gabas zuwa kusurwar Ƙofar Doki, za su zama mai tsarki ga Ubangiji. Ba za a ƙara tumɓuke birnin ko a rushe shi ba.”

< 耶利米書 31 >