< 以賽亞書 15 >
1 有關摩阿布的神諭:實在,摩阿布的阿爾經過一夜的蹂躪,就滅亡了!實在,摩阿布的克爾經過一夜的摧殘,就滅亡了!
Abin da Allah ya yi magana a kan Mowab shi ne, An lalatar da Ar a Mowab, an hallaka ta da dare! An lalatar da Kir a Mowab, an hallaka ta da dare!
2 狄朋女兒走上高丘哭泣,摩阿布為乃波和默德巴悲號;眾人的頭都剃光了,眾人的鬍鬚都剪去了;
Dibon ya haura zuwa haikalinta, zuwa masujadan kan tudu don tă yi kuka; Mowab ta yi ihu a kan Nebo da Medeba. An aske kowane kai an kuma yanke kowane gemu.
3 有的在街道上穿著苦衣,有的在屋頂上痛哭;在廣場上的人,人人哀號,流淚痛哭。
A tituna sun sa tsummoki a jikunansu; a kan rufin ɗakuna da kuma dandalin taruwa dukansu sai makoki suke yi, sun kwanta suna kuka.
4 赫市朋和厄肋阿肋號啕,雅哈茲都可聽到他們的哭聲;因此摩阿布的兩腰為之顫動,她的心靈為之恐怖。
Heshbon da Eleyale sun yi kuka da ƙarfi, aka ji muryoyinsu ko’ina har zuwa Yahaz. Saboda haka mayaƙan Mowab suka yi kuka da ƙarfi, har zuciyarsu ta karai.
5 我的心為摩阿布發出哀號,她的難民已逃至左哈爾。他們哭著攀上了路希特的山坡,在曷洛納因的道上揚起了失望的哀聲。
Zuciyata ta yi kuka a kan Mowab; mutanenta sun gudu har zuwa Zowar, har zuwa Eglat Shelishiya. Sun haura zuwa Luhit, suna tafe suna kuka; a kan hanyar zuwa Horonayim suna makoki saboda hallakawarsu.
6 尼默陵的水地成了荒野,青草枯焦了,嫩芽萎縮了,再也見不到青綠。
Ruwayen Nimrim sun ƙafe ciyayin kuma sun bushe; tsire-tsire duk sun ɓace babu sauran ɗanyen abu.
7 為此,他們將所有的積蓄和財物,都帶過了「柳樹河。」
Saboda haka dukiyar da suka tara suka kuma ajiye sun ɗauka suka ƙetare Rafin Arabim da su.
8 因為哀叫聲傳遍了摩阿布四境,她的哭聲已傳到厄革拉因,她的哭聲已達到貝爾厄林。
Ƙugin kukansu ya kai ko’ina a iyakar Mowab; kururuwarsu ta kai har zuwa Eglayim, makokinsu ya kai har zuwa Beyer-Elim.
9 狄孟的水已滿了鮮血,我還要加禍於狄孟:為摩阿布的難民和當地的遺民將有一隻獅子。
Ruwayen Dimon sun cika da jini, amma zan yi ƙari a kan Dimon, zan kawo zaki a kan masu gudu na Mowab da kuma a kan waɗanda suka ragu a ƙasar.