< 何西阿書 8 >
1 你要把號角放你的口上,當作上主家的哨兵,因為百姓違背了我的盟約,,干犯了我的法律。
“Ka sa kakaki a leɓunanka! Gaggafa tana a bisan gidan Ubangiji domin mutane sun tā da alkawarina suka kuma tayar wa dokata.
Isra’ila ta yi mini kuka, ‘Ya Allahnmu, mun yarda da kai!’
Amma Isra’ila sun ƙi abin da yake mai kyau; abokin gāba zai fafare su.
4 他們自立了君王,卻沒有我的同意;他們自立了首領,卻沒有叫知道;他們用金錢為自己製造了偶像,給自己招來滅亡。
Suna naɗa sarakuna, ba da izinina ba; sun zaɓa shugabanni ba da yardanta ba. Da azurfa da zinariya sun ƙera gumaka wa kansu wanda zai kai zuwa ga hallakarsu.
5 撒馬黎雅! 我必要除掉你的牛犢,我的怒火必要對牠燃起;以色列子民不能自新要到幾時呢﹖
Ku zubar da gunkin maraƙinku, ya Samariya! Fushina yana ƙuna a kansu. Sai yaushe za su rabu da gumaka?
6 牛犢是工匠製造的,牠並不是天主;撒馬黎雅的牛犢必定被粉碎!
Su daga Isra’ila ne! Wannan maraƙi, mai aikin hannu ne ya yi shi; gunki ne ba Allah ba. Za a farfashe shi kucu-kucu, waccan maraƙin Samariya.
7 他們既播種了風,收的也必是風;麥子不抽穗,做不成麵粉;既使做出麵粉來,也必被外邦人吃掉。
“Gama sun shuka iska don haka za su girbe guguwa. Hatsin da yake tsaye ba shi da kai, ba zai yi tsaba ba. Ko da ya yi tsaba ma, baƙi ne za su ci.
8 以色列疲吞滅了,今後在列邦中必成為一個無用的廢物。
An haɗiye Isra’ila; yanzu tana cikin al’ummai kamar abin da ba shi da amfani.
9 他們去投奔亞述──一匹孤獨的野驢──同時又給埃及送愛情的禮物。
Gama sun haura zuwa Assuriya kamar jakin jejin da yake yawo shi kaɗai. Efraim ya sayar da kansa ga maza.
10 縱然他們在列邦中行賄,我現在就要分散他們,使他們暫時停止給君王和領袖傅油。
Ko da yake sun sayar da kansu a cikin al’ummai, yanzu zan tattara su wuri ɗaya. Za su fara lalacewa a ƙarƙashi danniyar babban sarki.
11 厄弗辣因建築了許多祭壇,但這些祭壇卻只有犯罪的用途。
“Ko da yake Efraim ya gina bagadai masu yawa don hadayun zunubi, waɗannan sun zama bagade don yin zunubi.
12 雖然我為他們寫了許多法律,卻被看作陌生人的廢話。
Na rubuta musu abubuwa masu yawa na dokata, amma suka ɗauke su tamƙar wani baƙon abu ne.
13 讓他們奉獻燔祭,讓他們取吃祭肉;這一切上主都不喜歡;今後衪必記住他們的邪惡,必懲罰他們的罪孽;他們必要回到埃及去。
Suna miƙa hadayun da aka ba ni su kuma ci nama, amma Ubangiji ba ya jin daɗinsu. Yanzu zai tuna da muguntarsu yă kuma hukunta zunubansu. Za su koma Masar.
14 以色列忘了自己的造主,建立了許多宮殿,猶大也增建了許多堅固的城池;但是,我必要把火投在你們的1城中,吞滅城中的宮室。
Isra’ila ya manta da Mahaliccinsa ya kuma gina fadodi; Yahuda ya gina katanga a yawancin garuruwansa. Amma zan aiko da wuta a bisa biranensu da zai cinye kagaransu.”