< 出埃及記 7 >
1 上主向梅瑟說:「看,我使你在法朗前像神一樣,你的哥哥亞郎將作你的代言人。
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Duba, na maishe ka kamar Allah ga Fir’auna, ɗan’uwanka Haruna kuma zai zama annabinka.
2 凡我吩咐你的一切,你要告訴你的哥哥亞郎,要他對法朗講話,叫他放以色列子民離開他的國境。
Za ka faɗi kome da na umarce ka, ɗan’uwanka Haruna kuwa zai faɗa wa Fir’auna, yă bar Isra’ilawa su fita daga ƙasarsa.
3 我卻要使法朗心硬,為此在埃及國要增多我的奇蹟和異事。
Amma zan taurare zuciyar Fir’auna, kuma ko da na ninka mu’ujizai da kuma alamu a Masar,
4 因法朗布聽從你們,我要向埃及伸手,藉嚴厲的懲罰,將我的軍隊,我的百姓以色列子民,從埃及國領出來。
ba zai saurare ku ba. Don haka zan miƙa hannuna a kan Masar, in murƙushe ta da bala’i iri-iri, bayan haka zan fitar da taron mutanen Isra’ila daga ƙasar Masar ta wurin hukuntaina masu girma.
5 當我向埃及人伸手,將以色列子民從埃及人中間領出來的時候,他們要承認我是上主。」
Masarawa kuwa za su san cewa ni ne Ubangiji sa’ad da na miƙa hannuna a kan Masar, na kuma fitar da Isra’ilawa daga gare ta.”
6 梅瑟和亞郎就受命行事;上主怎樣吩咐他們,他們就怎樣行了。
Musa da Haruna suka aikata yadda Ubangiji ya umarce su.
7 當他們去與法朗會談的時候,梅瑟八十歲,亞郎八十三歲。
Musa yana da shekara tamanin da haihuwa, Haruna kuma yana da shekara tamanin da uku, sa’ad da suka yi magana da Fir’auna.
Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
9 如果法朗要求你們說:你們顯個奇蹟,給你們作證罷! 你就吩咐亞郎說:將你的棍杖扔在法朗的面前,棍杖就會變成一條蛇。」
“Sa’ad da Fir’auna ya ce muku, ‘Aikata wani al’ajabi,’ sai ka ce wa Haruna, ‘Ɗauki sandanka ka jefa shi a ƙasa, a gaban Fir’auna,’ zai kuwa zama maciji.”
10 梅瑟和亞郎就去見法朗,照上主的吩咐做了:亞郎將棍杖扔在法朗和他的臣僕面前,棍杖就變成了一條蛇。
Sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir’auna, suka yi yadda Ubangiji ya umarce su. Haruna ya jefa sandansa ƙasa, a gaban Fir’auna da bayinsa, sai sandan ya zama maciji.
11 法朗將他的智者和術士召來,這些埃及的巫士也用他們的巫術作了同樣的事:
Fir’auna kuwa ya kira masu hikima da masu sihiri, sai bokayen Masarawa ma suka yi irin abubuwan nan da bokancinsu.
12 他們每人扔下自己的棍杖,也都變成了蛇,但亞郎的棍杖卻吞了他們的棍杖。
Kowannensu ya jefa sandansa ƙasa, ya kuwa zama maciji. Amma sandan Haruna ya haɗiye sandunansu.
13 法朗仍然心硬,不肯聽他們的話,正如上主所說。第一災、水變血
Duk da haka zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa saurare su ba, kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Zuciyar Fir’auna taurariya ce, ya ƙi yă bar mutanen su tafi.
15 明天早晨你去見法朗。他去水邊時候,你要站在尼羅河邊迎住他;手中拿著那根變過蛇的棍杖。
Ka je wurin Fir’auna da safe, yayinda za shi kogi. Ka jira a bakin Nilu don ka sadu da shi, ka ɗauki sandan nan da ya canja zuwa maciji a hannunka.
16 你對他說:上主,希伯來人的天主打發我來見你說:你應放我的百姓到曠野中去崇拜我;彈道現在你仍沒有聽從。
Sa’an nan ka ce masa, ‘Ubangiji, Allah na Ibraniyawa, ya aiko ni in faɗa maka, Ka bar mutanena su tafi domin su yi mini sujada a hamada. Amma har yanzu ba ka yi biyayya ba.
17 上主這樣說:看,我要用我手中拿的棍杖擊打河水,水就變成血,如此你必承認,我是上主。
Ga abin da Ubangiji ya ce, da wannan za ka san cewa ni ne Ubangiji. Da sandan da yake hannuna zan bugi ruwan Nilu, zai kuma zama jini.
18 河中的魚都要死,河水都要腥臭,埃及人不能再喝河中的水。」
Kifi a ciki Nilu za su mutu, ruwan kuma zai yi ɗoyi; Masarawa ba za su iya shan ruwansa ba.’”
19 上主對梅瑟說:「你向亞郎說:拿起你的棍杖,將手伸在埃及的水上,即伸在河、溝渠、池沼和一切水塘之上,水都要變成血;如此埃及全國,連木器石器中的水野都要變成血。」
Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ce wa Haruna, ‘Ka ɗauki sandanka, ka miƙa hannunka kan ruwan Masar, kan kogunansu da rafuffukansu da kududdufansu da kuma dukan tafkunansu, za su zama jini.’ Jini zai kasance ko’ina a Masar, har ma a cikin abubuwan ajiyar ruwansu da aka yi da itace da kuma dutse.”
20 梅瑟和亞郎就照了上主的吩咐作了:亞郎在法朗和他臣僕的面前,舉起棍杖一打河水,所有的河水變成了血;
Musa da Haruna suka yi yadda Ubangiji ya umarta. Ya ɗaga sandansa a gaban Fir’auna da bayinsa, ya bugi ruwan Nilu, dukan ruwan kuwa ya zama jini.
21 河中的魚都死了,河水都腥臭不堪,埃及人不能再喝河中的水;埃及遍地是血。
Kifin da suke cikin Nilu suka mutu, kogin kuwa ya yi wari sosai yadda Masarawa ba su iya shan ruwan ba. Jini ya bazu ko’ina a Masar.
22 埃及的巫士用他們的巫術也行了同樣的事,因此法朗仍舊心硬,不肯聽信梅瑟和亞郎,正像上主所說的。
Amma bokayen Masar ma suka yi abubuwan nan da sihirinsu, sai zuciyar Fir’auna ta taurare; bai saurari Musa da Haruna ba, kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
A maimakon yă saurara, sai ya juya ya koma fadarsa, bai ma damu da abin da aka yi ba.
24 因為全埃及的人不能喝河中的水,便在河的附近掘水喝。第二災、蝦蟆
Sai dukan Masarawa suka yi ta tonon gefen Nilu don su sami ruwan sha, domin ba su iya shan ruwan kogin ba.
Kwana bakwai suka wuce bayan da Ubangiji ya bugi kogin.