< 出埃及記 5 >
1 此後,梅瑟同亞郎去見法朗說:「以色列的天主雅威這樣說:「你應放我的百姓走,好叫他們在曠野裏過傑敬拜我。」
Daga bisani sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir’auna suka ce, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Bari mutanena su tafi domin su yi mini biki a hamada.’”
2 法朗問說:「誰是雅威,我該聽他的命,放以色列走﹖我不認識雅威,也不放以色列走。」
Fir’auna ya ce, “Wane ne Ubangiji da zan yi biyayya da shi, har in bar Isra’ila su tafi? Ban san Ubangiji ba, kuma ba zan bar Isra’ila su tafi ba.”
3 他們回答說:「希伯來人的天主遇見了我們。請讓我們走三天的路到曠野裏,向上主我們的天主獻祭,免得他用瘟疫刀兵擊殺我們。」
Sai suka ce, “Allah na Ibraniyawa ya sadu da mu. Yanzu bari mu ɗauki tafiyar kwana uku cikin hamada domin mu miƙa hadaya ga Ubangiji Allahnmu, don kada yă buga mu da annoba ko takobi.”
4 埃及王回答他們說:「梅瑟、亞郎啊! 你們為什麼妨礙百姓工作呢﹖去服你們的勞役罷! 」
Amma sarkin Masar ya ce wa, “Musa da Haruna, don me kuke hana mutane yin aikinsu? Ku koma wurin aikinku!”
5 法朗又說:「現在他們比本地的人民還多,你們竟然叫他們歇工﹖」
Sa’an nan Fir’auna ya ce, “Ga shi mutane sun yi yawa a ƙasar Masar, ku kuma yanzu kuna so ku hana su yin aiki.”
A wannan rana Fir’auna ya ba da wannan umarni wa shugabannin masu gandu,
7 你們以後不要再像往日一樣,給百姓做磚用的草楷,叫他們自己去拾草。
“Kada ku ƙara ba wa mutanen ciyawar tattaka domin su yi tubula, bari su tafi su tattara tattaka da kansu.
8 但你們仍向他們要往日所做的同樣磚數,一點也不可減少,因為他們懶惰,所以才吶喊說:我們要去向我們的天主獻祭。
Ku kuma bukace su su yi tubula daidai yawan tubalin da suka saba yi, kada ku rage. Ragwaye ne, shi ya sa suke kuka cewa, ‘Bari mu tafi mu yi hadaya ga Allahnmu.’
9 應給這些人加重工作,使他們只工作,而不聽謊言。」苦工加重
Ku sa waɗannan mutane su yi aiki mai tsanani sosai, don kada su sami zarafin kasa kunne ga maganganun ƙarya.”
10 百姓中的監工頭遂出去向百姓說:「法朗這樣吩咐:我不再給你們草楷。
Sai shugabannin masu aikin gandu suka fita suka gaya wa mutanen Isra’ila, “Ga abin da Fir’auna ya ce, ‘Ba zan ƙara ba ku tattaka ba.
11 你們看那裏能找到草楷,就到那裏去拾罷! 但應有的工作一點也不可減少。」
Ku tafi ku nemo wa kanku tattaka duk inda za ku samu, amma ba za a rage aikinku ba ko kaɗan.’”
Saboda haka mutane suka warwatsu ko’ina a Masar domin tattara bunnun da za su yi amfani da su, maimakon tattaka.
13 監工催迫說:「你們每天應該完成當天的工作,像從前有草楷時一樣。」
Shugabannin gandu suka dinga matsa musu suna cewa, “Ku cika aikin da aka bukace ku na kowace rana kamar yadda kuke yi sa’ad da kuke da tattaka.”
14 法朗的監工責打他們所派出的以色列子民的工頭說:「你們昨天今天為什麼沒有完成像前天所做的磚數呢﹖」
Manyan Isra’ilawa waɗanda shugabannin gandun Fir’auna suka naɗa, suka sha dūka, aka kuma yi musu tambayoyi ana cewa, “Don me ba ku cika yawan tubula na jiya da na yau kamar yadda kuka saba ba?”
15 以色列子民的工頭遂去向法朗訴苦說:「你為什麼這樣對待你的僕人們呢﹖
Sai manyan Isra’ila masu bi da aikin gandu suka tafi wurin Fir’auna suka yi roƙo suna cewa, “Don me kake yi wa bayinka haka?
16 不給你僕人們草楷,只對我們說:做磚罷! 原是你人民的錯,你卻來打你的僕人們。」
Ba a ba wa bayinka tattaka, duk da haka ana ce mana, ‘Ku yi tubula!’ Ana wa bayinka dūka, amma fa laifin na mutanenka ne.”
17 法朗回答說:「你們太懶惰了! 所以說:讓我們去祭獻上主!
Fir’auna ya ce, “Ku ragwaye ne! Shi ya sa kuke cewa, ‘Bari mu tafi mu yi hadaya wa Ubangiji.’
18 現在都快去作工! 決不供給你們草楷,但是磚卻該如數交上。
Ku ɓace yanzu daga nan, ku koma wurin aikinku. Ba za a ba ku tattaka ba, kuma dole ku fid da tubula kamar yadda kuka saba.”
19 以色列子民的工頭因所出的命令說:你們每天應做的磚數,不得減少,」便知自己更陷於困難中。梅瑟受責哀求天主
Manyan Isra’ilawa da suke bi da aikin gandu suka gane cewa sun shiga uku, sa’ad da aka gaya musu, “Ba za ku rage yawan tubulan da aka bukace ku ku yi na kowace rana ba.”
20 工頭們由法朗那裏出來,遇見梅瑟和亞郎正等候他們,
Da suka bar Fir’auna, sai suka sadu da Musa da Haruna suna jira su sadu da su,
21 就對他們說:「願上主鑑察懲罰你們! 你們使我們在法朗和他臣僕眼中成了可恨的,就好像把刀交在他們手中,宰殺我們。」
sai suka ce, “Bari Ubangiji yă duba, yă kuma hukunta ku! Kun maishe mu abin ƙyama ga Fir’auna da bayinsa, kuka kuma sa musu takobi a hannunsu don su kashe mu.”
22 梅瑟回到上主那裏說:「吾主,你為什麼折磨這百姓﹖為什麼偏偏打發我呢﹖
Musa ya koma wurin Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji, don me ka kawo wahala a kan mutanen nan? Abin da ya sa ka aiko ni ke nan?
23 自從我到法朗那裏,奉你的名講話以來,他更加折磨這百姓,而你也沒有整救你的百姓。」
Gama tun da na tafi wurin Fir’auna, na yi masa magana da sunanka, sai ya fara gasa wa mutanen nan azaba, ba ka kuma ceci mutanenka.”