< 列王紀下 2 >

1 上主要用旋風接厄里亞升天的時候,厄里亞和厄里叟正離開基耳加耳;
Da lokaci ya yi da Ubangiji zai ɗauki Iliya zuwa sama cikin guguwa, Iliya da Elisha kuwa suna kan hanyarsu daga Gilgal.
2 厄里亞對厄里叟說:「請你劉在這裏,因為上主派我到貝特耳去。」厄里叟卻回答說:「我指著永生的上主和你的性命起誓:我決不離開你。」於是二人到貝特耳。
Sai Iliya ya ce wa Elisha, “Ka dakata a nan; Ubangiji ya aike ni Betel.” Amma Elisha ya amsa ya ce, “Muddin Ubangiji yana a raye, kai kuma kana a raye, ba zan rabu da kai ba.” Saboda haka suka gangara zuwa Betel.
3 在貝特耳的先知弟子們出來見厄里叟說:「上主今天要接你的師傅離開你,你知道嗎﹖」他回答說:「是,我知道,你們不要作聲。」
Sai ƙungiyar annabawa a Betel suka fito zuwa wajen Elisha suka ce masa, “Ka san cewa Ubangiji zai ɗauki maigidanka daga wurinka yau?” Sai ya ce, “I, na sani, amma kada ku yi magana game da wannan.”
4 厄里亞對厄里叟說:「厄里叟,請你留在這裏,因為上主派我到耶里哥去。」他回答說:「我指著永生的上主和你的性命起誓:我決不離開你。」於是二人往耶里哥去了。
Sai Iliya ya ce masa, “Ka dakata a nan Elisha; Ubangiji ya aike ni Yeriko.” Sai ya ce masa, “Muddin Ubangiji yana a raye, kai ma kana a raye, ba zan rabu da kai ba.” Saboda haka sai suka tafi Yeriko.
5 在耶里哥的先知弟子們前來,對厄里叟說: 「上主今天要接你的師傅離開你,你知道嗎﹖」他回答說:「是的,我知道,你們不要作聲。」
Ƙungiyar annabawa a Yeriko suka haura zuwa wajen Elisha suka ce, “Ko ka san Ubangiji zai ɗauki maigidanka daga gare ka yau?” Sai ya ce, “I, na sani, amma ku bar zancen nan tukuna.”
6 厄里亞又對厄里叟說:「請你留在這裏,因為上主派我到約但河去。」厄里叟回答說:「我指著永生的上主和你的性命起誓:我決不離開你。」二人於是繼續前行。
Sai Iliya ya ce masa, “Ka dakata a nan, Ubangiji ya aike ni Urdun.” Sai Elisha ya ce masa, “Muddin Ubangiji yana a raye, kai kuma kana raye, ba zan rabu da kai ba.” Saboda haka suka ci gaba da tafiya tare.
7 先知弟子中有五十個人同去,遠遠站在他們對面,他們二人立在約旦河邊,
Mutum hamsin na ƙungiyar annabawa suka je suka tsaya da nisa, suna fuskantar inda Iliya da Elisha suka tsaya a Urdun.
8 厄里亞將自己的外衣捲起,擊打河水,即左右分開,他們二人從乾地上走了過去。
Sai Iliya ya tuɓe rigarsa, ya nannaɗe ya bugi ruwan Urdun da shi. Sai ruwan ya dāre gida biyu, suka haye a busasshiyar ƙasa.
9 過去以後,厄里亞對厄里叟說:「在我被接去離開你以前,我應該為你作什麼,你儘管求罷! 」厄里叟答說:「求你把你的精神給我兩分。」
Da suka haye, sai Iliya ya ce wa Elisha, “Faɗi mini, abin da kake so in yi maka kafin a ɗauke ni daga gare ka!” Elisha ya amsa ya ce, “Bari in gāji ninki biyu na ruhunka.”
10 厄里亞說:「你求了一件難事;不過當我被接去離開你的時候,你若能看見我,你就可以得到;否則,你就不能得到。」
Iliya ya ce, “Ka nemi abu mai wuya, amma in ka ga lokacin da aka ɗauke ni daga gare ka, zai zama naka, in ba haka ba, ba za ka samu ba ke nan.”
11 他們正邊走邊談的時候,忽然有一輛火馬拉的火車出現,把他們二人分開;厄里亞便乘著旋風升天去了。
Yayinda suke tafiya suna magana, sai kwatsam, keken yaƙin wuta da dawakan wuta suka ratse tsakaninsu, sai Iliya ya tafi sama a cikin guguwa.
12 厄里叟一見,就呼喊說:「我父,我父! 以色列的戰車,以色列的駿馬! 」隨後就再看不見他了;厄里叟遂抓住自己的衣服,撕成兩半,
Da Elisha ya ga haka sai ya yi ihu yana cewa, “Babana! Babana! Kekunan yaƙin da mahayan dawakan Isra’ila!” Elisha kuwa bai sāke ganinsa ba. Sai ya kama tufafinsa ya yayyage.
13 然後拾起厄里亞身上掉下來的外衣,回去站在約旦河邊,
Sai ya ɗauki rigar da ta fāɗo daga Iliya ya koma ya tsaya a gaɓar Kogin Urdun.
14 拿著從厄里亞身上掉下來的外衣擊打河水說:「上主,厄里亞的天主在那裏﹖」他一擊打河水,河水就左右分開,厄里叟走了過去。
Sa’an nan Elisha ya ɗauki rigar da ta fāɗo daga Iliya ya bugi ruwan da shi. Ya ce, “Yanzu ina Ubangiji Allah na Iliya?” Da ya bugi ruwan sai ruwan ya dāre gida biyu, sai ya haye.
15 耶里哥的先知弟子們從對面看見了他,就說:「厄里亞的精神已降在厄里叟的身上了。」他們便前來迎接,俯伏在地,叩拜他,
Ƙungiyar annabawa daga Yeriko, waɗanda suke kallo, suka ce, “Ruhun Iliya yana a kan Elisha.” Sai suka je su tarye shi, suka rusuna har ƙasa a gabansa.
16 對他說:「你僕人中有五十個強壯的人,請讓他們去尋找你的師傅,或者上主的神將他提去,丟在一座山上,或一個山谷裏。」他回答說:「不必派他們去。」
Suka ce, “Duba, mu bayinka muna da masu ji da ƙarfi hamsin. Bari su je su nemi maigidanka. Wataƙila, Ruhun Ubangiji ya ɗauke shi ya ajiye bisa wani dutse, ko wani kwari.” Elisha ya ce, “A’a, kada ku aike su.”
17 但是他們逼得他不好意思,他這纔說:「你們派人去罷! 」他們於是派了五十個人去,尋找了三天,始終沒有找到,
Amma suka matsa masa har ya ji ba ya iya hana su. Saboda haka ya ce, “Ku aike su.” Sai suka aiki mutane hamsin, suka yi ta nema har kwana uku amma ba su same Iliya ba.
18 便回來見厄里叟,那時厄里叟還在耶里哥。厄里叟對他們說:「我不是對你們早說了,你們不必去嗎﹖」
Da suka dawo wurin Elisha, wanda yake a Yeriko, sai ya ce musu, “Ban ce muku kada ku tafi ba?”
19 城中的人對厄里叟說:「請看,本城的地勢很好,師傅也看見了,只是水不好,以致土產不熟即落。」
Mutane garin suka ce wa Elisha, “Ranka yă daɗe, duba, garin yana da kyan gani, amma ruwan ba shi da kyau, ƙasar kuma ba ta ba da amfani.”
20 厄里叟說:「給我拿一隻新碗來,裏面放上些鹽。」他們就給他拿了來;
Sai ya ce, “Ku kawo mini sabuwar ƙwarya, ku kuma sa gishiri a ciki.” Sai suka kawo masa.
21 他遂出去到水泉旁,將鹽倒在水裏說:「上主這樣說:我已治好了這水,從此再也不會引起死亡和不熟早落的病。」
Sai ya tafi maɓulɓular ruwan yana watsa gishirin a ciki, yana cewa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Na warkar da ruwan nan. Ba zai ƙara jawo mutuwa, ko yă hana ƙasar ba da amfani ba.’”
22 果然,照厄里叟所說的,那水直到今日常是好水。
Ruwan ya tsabtacce har yă zuwa yau, bisa ga faɗin Elisha.
23 厄里叟從那裏上貝特耳去,當他沿路上去的時候,從城中出來一些小孩,譏笑他說:「光頭,上來! 光頭,上來! 」
Daga nan sai Elisha ya tafi Betel. Yayinda yake tafiya a hanya, sai waɗansu matasa suka fito daga cikin gari, suka yi masa dariya suna cewa, “Ka haura, ya kai mai kai marar gashi! Ka haura, kai mai kai marar gashi!”
24 厄里叟回過頭去看他們,因上主的名詛咒了他們;立即有兩隻狗熊從林中出來,咬死了其中四十二個孩子。
Sai ya juya ya dube su, ya la’anta su da sunan Ubangiji. Sai beyar guda biyu suka fito daga jeji suka hallaka matasa arba’in da biyu daga cikinsu.
25 厄里叟從那裏去了加爾默耳山,然後又從那裏回了撒瑪黎雅。
Sai ya ci gaba zuwa Dutsen Karmel, daga can kuma ya koma Samariya.

< 列王紀下 2 >