< 列王紀下 10 >

1 阿哈布在撒瑪黎雅尚有七十個孫子,為此,耶胡寫信給撒瑪黎雅城中的首領、長老和阿哈布子孫的師保,說:「
To, akwai’ya’ya maza saba’in na gidan Ahab a Samariya. Saboda haka Yehu ya rubuta wasiƙu, ya aika su Samariya, zuwa ga shugabannin Yezireyel, da kuma ga masu lura da’ya’yan Ahab. Ya ce,
2 你們主上的子孫,既然都同你們在一起,又有車馬、堅城和武器;那麼,這信一到你們手中,
“Da zarar wasiƙan nan ta sadu da ku, da yake’ya’yan maigidanku suna tare da ku, kuna kuma da kekunan yaƙi da dawakai, da birni mai katanga da makamai,
3 你們就在你們主上的子孫中,選出一位最好最能幹的,坐上他父親的寶座,來為你們主上的家作戰。」
sai ku zaɓi mafi cancanta a cikin’ya’yan maigidanku ku sa shi a kan kursiyin mahaifinsa. Sa’an nan ku yi yaƙi don gidan maigidanku.”
4 但是,他們都很害怕說:「哎! 兩位君王尚且不能抵抗他,我們又怎能抵抗﹖」
Amma suka razana suka ce, “Idan sarakuna biyu ba su iya yin tsayayya da shi ba, wane mu?”
5 因此,家臣、市長、長老和師保,便派人去見耶胡說:「我們是你的僕人,凡你吩咐的,我們都必照辦。我們不選立任何人作王;你看著怎樣好,就怎樣辦罷! 」
Saboda haka sarkin fada, da gwamnan birnin, da dattawa, da kuma masu lura da’ya’yan suka aika da saƙo ga Yehu, cewa, “Mu bayinka ne, za mu kuma yi duk abin da ka ce. Ba za mu naɗa kowa sarki ba; sai ka yi abin da ka ga ya fi kyau.”
6 耶胡又給他們寫了第二封信:「如果你們擁護我,願聽從我的號令;那麼,明天這個時候,你們就帶著你們主上的子孫的頭,到依次勒耳來見我。」君王的七十個子孫,其時都教養在城中的官紳家中。
Sai Yehu ya sāke rubuta musu wasiƙa ta biyu, ya ce, “In a gefena kuke, to, sai ku yi biyayya da ni, ku fille kawunan’ya’yan maigidanku, ku kawo mini a Yezireyel war haka gobe.” To,’ya’yan sarki, su saba’in, suna tare da manyan birni waɗanda suke lura da su.
7 這封信一到,他們便將君王的七十個子孫全都殺了,把他們的頭放在籃子裏,送到依次勒耳耶胡那裏。
Sa’ad da wasiƙar ta iso, sai mutanen nan suka ɗauki dukan’ya’yan sarkin nan saba’in, suka kashe su, suka sa kawunansu cikin kwanduna, suka aika wa Yehu a Yezireyel.
8 有使者來報告耶胡說:「他們將君王子孫的頭送來了。」耶胡即下令說:「將頭分成兩堆,放在城門口,直到明天早晨。」
Da ɗan saƙon ya iso, sai aka ce wa Yehu, “Sun kawo kawunan’ya’yan sarki.” Sai Yehu ya ce, “Ku ajiye su kashi biyu a ƙofar gari har safiya.”
9 第二天早晨,耶胡出來,站著對全民眾說:「你們都沒有罪。看,我背叛了我的主上,且殺了他,但是,這些人是誰殺的呢﹖
Da gari ya waye, sai Yehu ya fita ya tsaya a gaban dukan jama’a ya ce, “Ba ku da laifi. Ni ne na ƙulla wa maigidana maƙarƙashiya, na kuma kashe shi, amma wa ya karkashe dukan waɗannan?
10 你們也知道上主的話,即上主論及阿哈布家所說的話,一句也沒有落空;上主藉他僕人厄里亞所說的話,都實現了。」
Ku sani fa, ba kalmar da Ubangiji ya faɗa game da gidan Ahab da ba za tă cika ba. Ubangiji ya yi abin da ya alkawarta ta bakin bawansa Iliya.”
11 然後,耶胡把阿哈布家在依次勒耳所剩下的人,所有的親屬、友人和司祭,全都殺了,一個也沒有留下。
Saboda haka Yehu ya kashe duk waɗanda suka rage na iyalin Ahab a Yezireyel, tare da dukan fadawansa da aminansa da firistocinsa, ba a bar masa kowa ba.
12 以後,耶胡起程往撒瑪黎雅去了。途中經過牧人聚集地貝特厄刻得時,
Sa’an nan Yehu ya nufi Samariya. Da ya kai Bet-Eked na Makiyaya,
13 遇見猶大王阿哈齊雅的兄弟,就問他們說:「你們是誰﹖」他們回答說:「我們是阿哈齊雅的兄弟,現在下去向君王和太后的兒子請安。」
sai ya gamu da waɗansu daga dangin Ahaziya sarkin Yahuda, sai ya tambaye su, ya ce, “Ku, su wane ne?” Suka ce, “Mu dangin Ahaziya ne, mun kuma zo ne mu gai da iyalan sarki da kuma mahaifiyar sarauniya.”
14 耶胡遂下令說:「將他們活活捉住! 」隨從就將他們活活捉住,在貝特厄刻得井旁把他們殺了,共計四十二人,一個也沒有留下。
Sai ya umarta ya ce, “A kama su da rai!” Aka kuwa kama su aka yayyanka kusa da rijiyar Bet-Eked, su arba’in da biyu. Ba a bar wani da rai ba.
15 耶胡從那裏起身前行,又遇見勒加布的兒子約納達布前來迎接他;耶胡向他請安,問他說:「你對我的心是否同我對你的心,請你伸出手來。」他就向耶胡伸過手去;耶胡就拉他上車,坐在自己身旁,
Bayan ya bar wurin, sai ya gamu da Yehonadab ɗan Rekab wanda yake kan hanyarsa don yă sadu da shi. Sai Yehu ya gaishe shi, ya ce, “Ka amince da ni yadda na amince da kai?” Yehonadab ya ce, “I.” Yehu ya ce, “To, in haka ne ka ba ni hannunka.” Sai ya miƙa masa, Yehu kuwa ya ja shi cikin keken yaƙin.
16 對他說:「你跟我來,看看我對天主是怎樣的熱誠。」於是叫他坐上他自己的車。
Yehu ya ce, “Zo tare da ni ka ga himmata saboda Ubangiji.” Sa’an nan ya sa suka tafi tare cikin keken yaƙinsa.
17 到了撒瑪黎雅,就照上主對厄里亞所說的話,將阿哈布家在撒瑪黎雅剩下的人,全都殺了。
Da Yehu ya isa Samariya, sai ya karkashe dukan sauran iyalin Ahab, ya hallaka su, bisa ga maganar da Ubangiji ya faɗa ta bakin Iliya.
18 耶胡召集了全國人民,對他們說:「阿哈布事奉巴耳不夠熱心,我耶胡要更熱心事奉他。
Sa’an nan Yehu ya tattara dukan jama’a ya ce musu, “Ahab ya bauta wa Ba’al kaɗan ne kawai; amma Yehu zai bauta masa sosai.
19 所以現在,你們去召集所有巴耳的先知,所有敬拜巴耳的人,和所有的司祭,都到我這裏來,一個也不要缺席,因為我要向巴耳奉獻大祭;誰缺席,誰就不能生存。」這原是耶胡運用的詭計,想消滅所有敬拜巴耳的人。
Yanzu sai ku kira dukan annabawan Ba’al, dukan masu yin masa hidima da kuma dukan firistocinsa. Ku tabbata ba a manta da wani ba, gama zan yi wa Ba’al babbar hadaya. Duk wanda bai zo ba, a bakin ransa.” Amma Yehu yana wayo ne domin yă hallaka masu yi wa Ba’al sujada.
20 耶胡下令說:「你們要為巴耳召開一個聖會! 」他們就宣布召開。
Yehu ya ce, “Ku kira jama’a don a girmama Ba’al.” Saboda haka suka yi shela.
21 耶胡派人走遍全以色列;凡敬百拜巴耳的人都來了,沒有一個缺席不來的;他們都進了巴耳廟,巴耳廟內全擠滿了人。
Sa’an nan ya aika saƙo ko’ina a Isra’ila, dukan masu yi wa Ba’al hidima kuwa suka tattaru, ba mutumin da bai zo ba. Suka yi cincirindo a haikalin Ba’al har sai da ya cika makil.
22 耶胡對管祭衣的人說:「為所有敬拜巴耳的人,拿出衣服來! 」那人就給他們拿出衣服來。
Sai Yehu ya ce wa mai ajiyar tufafi, “Ka kawo riguna domin dukan masu yi wa Ba’al hidima.” Sai ya fito musu da riguna.
23 耶胡和勒加布的兒子約納達布進了巴耳廟,對敬拜巴耳的人說:「你們要搜查看看,這裏不要有事奉雅威的人同你們在一起,只准敬拜巴耳的人。」
Sa’an nan Yehu da Yehonadab ɗan Rekab, suka shiga haikalin Ba’al. Yehu ya ce wa masu yi wa Ba’al sujada, “Ku dudduba ku tabbatar cewa babu wani bawan Ubangiji a nan tare da ku, sai masu hidimar Ba’al kawai.”
24 他們於是進去奉獻犧牲和全燔祭。耶胡預先在外已派定八十人,對他們說:「誰若讓我交於你們手中的一個人逃走,就要他以命抵命。」
Saboda haka suka shiga don su miƙa hadayu da kuma hadaya ta ƙonawa. To, Yehu ya riga ya ba wa mutane takwas wannan kashedi a waje cewa, “In waninku ya bar ɗaya daga cikin mutanen nan da nake danƙa a hannunku ya tsere, to, a bakin ransa.”
25 全燔祭奉獻完畢,耶胡吩咐衛兵和軍官說:「你們進去擊殺,一個耶不可叫他逃走! 」衛兵和軍官便用刀擊殺了他們,把他們的屍體拋出,然後進入巴耳廟的內堂,
Nan da nan sa’ad da Yehu ya gama yin hadayar, sai ya umarci masu gadin da hafsoshi, “Ku shiga ku karkashe su; kada ku bar wani yă tsere.” Saboda haka suka karkashe su da takobi. Masu gadin da hafsoshin suka wuwwurga gawawwakinsu waje, suka kuma shiga ciki cikin haikalin Ba’al ɗin,
26 把巴耳廟內的神柱搬出來燒了,
suka fitar da dutsen tsafi daga haikalin Ba’al, suka kuma ƙone shi.
27 推倒了巴耳偶像,拆毀了巴耳廟,使之成為一個廁所,直到今日。
Suka farfasa dutsen tsafin Ba’al, suka kuma rushe haikalin, mutane suka mai da wurin salga har yă zuwa yau.
28 這樣,耶胡將巴耳從以色列中剷除了;
Ta haka Yehu ya hallaka butar Ba’al a Isra’ila.
29 但他仍沒有離棄乃巴特的兒子雅洛貝罕使以色列陷於罪惡的罪:即那兩頭設在貝特耳和丹的金牛。
Duk da haka, bai rabu da zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata ba, wato, yin sujada ga siffofin maruƙa na zinariya a Betel da kuma Dan.
30 上主對耶胡說:「由於你好好執行了我視為義的事,照我心中所想的一切對待了阿哈布家,你的子孫要坐以色列的王位,直到第四代。」
Ubangiji ya ce wa Yehu, “Tun da yake ka aikata abin da yake mai kyau a idanuna, ka kuma yi wa gidan Ahab dukan abin da yake a zuciyata, ina yin maka alkawari cewa zuriyarka za su yi mulkin Isra’ila har tsara ta huɗu.”
31 但耶胡並沒有全心謹守遵行上主以色列天主的法律,沒有放棄雅洛貝罕使以色列陷於罪惡的罪。
Duk da haka, Yehu bai mai da hankali ya kiyaye dokokin Ubangiji, Allah na Isra’ila da dukan zuciyarsa ba. Bai rabu da zunubin Yerobowam, wanda ya sa Isra’ila ta aikata ba.
32 那時,上主開始削弱以色列,哈匝耳也在四面邊境上攻擊以色列,
A kwanakin sai Ubangiji ya fara rage girman Isra’ila, Hazayel ya yi nasara a bisa Isra’ila a ko’ina a yankinsu
33 侵佔了約旦河東基肋阿得全地,即加得人,勒烏本和默納協人的地方,從阿爾農河附近的阿洛厄爾城,直到基肋阿得和巴商。
gabas da Urdun, cikin dukan ƙasar Gileyad (yankin Gad, da na Ruben, da na Manasse), daga Arower wajen Kwarin Arnon ya ratsa Gileyad zuwa Bashan.
34 耶胡其餘的事蹟,他的一切作為和武功,都記載在以色列列王實錄上。
Game da sauran ayyukan mulkin Yehu, da dukan abin da ya yi, a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
35 耶胡與列祖同眠,人將他葬在撒瑪黎雅;他的兒子約阿哈次繼位為王。
Yehu ya huta tare da kakanninsa, aka binne shi a Samariya. Yehoyahaz kuma ya ci sarauta bayansa.
36 耶胡在撒瑪黎雅作以色列王,凡二十八年。
Yehu ya yi sarautar Isra’ila a Samariya shekara ashirin da takwas.

< 列王紀下 10 >