< 撒母耳記上 30 >

1 當達味和他的人第三天來到漆刻拉格時,阿瑪肋克人已侵入乃革布和漆刻拉格,將漆刻拉格洗劫,放火燒了,
A rana ta uku, Dawuda da mutanensa suka isa Ziklag, sai suka tarar Amalekawa sun riga sun kawo wa Negeb da Ziklag hari. Suka cinye Ziklag, suka ƙone ta,
2 將城中的婦女,以及所有的老幼,都擄了去;但沒有殺人,只將他們擄走,回返原路。
suka kwashe mata, yara da tsofaffi da dukan abubuwan da suke cikin garin. Ba su kashe kowa ba, amma suka kwashe su, suka tafi.
3 達味和他的人來到城旁,見城已被火燒毀,他們的妻子兒女盡被據去,
Da Dawuda da mutanensa suka isa Ziklag suka tarar an ƙone garin, an kuma kwashe matansu, da’ya’yansu mata, da kuma’ya’yansu maza ganima,
4 遂放聲大哭,直哭得聲嘶力竭。
sai Dawuda da mutanensa suka yi kuka, suka yi ta kuka har sai da ƙarfinsu ya ƙare.
5 達味的兩個妻子:依次勒耳人阿希諾罕和曾作加爾默耳人納巴耳妻子的阿彼蓋耳也被據去了。
An kama matan Dawuda, wato, Ahinowam daga Yezireyel da Abigiyel matar Nabal mutumin Karmel wanda ya rasu.
6 達味陷入窘境,因為人民各為自己的兒女非常痛心,都說要用石頭打死他;但是達味更加堅固倚靠上主,他的天主。
Dawuda kuwa ya damu ƙwarai domin mutanensa suna niyyar su jajjefe shi da duwatsu, kowannensu ransa ya ɓace saboda’ya’yansa maza da mata, amma Dawuda ya sami ƙarfafawa a cikin Ubangiji Allahnsa.
7 達味對阿希默肋客的兒子厄貝雅塔爾司祭說:「請你將「厄弗得」給我拿來! 」厄貝雅塔爾就將厄弗得」給達味拿了來。
Sai Dawuda ya ce wa Abiyatar firist, ɗan Ahimelek, “Kawo mini efod.” Sai Abiyatar ya kawo masa.
8 達味求問上主說:「我該追趕這些土匪嗎﹖我追得上嗎﹖」上主答說:「你去追趕,必能追上,能救回一切」。
Dawuda kuwa ya nemi nufin Ubangiji ya ce, “In bi bayan’yan harin nan? Zan ci musu?” Ubangiji ya ce, “Bi su, gama za ka ci musu, ka ƙwato abin da suka kwashe.”
9 達味和隨從他的六百人於是立即出發,到了貝索爾河。
Dawuda da mutanensa ɗari shida suka kama hanya, da suka kai Kwarin Besor, waɗansunsu suka tsaya a can.
10 艮帶著四百人仍向追趕,其餘二百人因為過於疲倦,不能過貝索爾河,就住下了。
Dawuda ya ci gaba da mutane ɗari huɗu, don mutane ɗari biyu sun gaji sosai har sun kāsa ƙetare rafin Besor.
11 有人在田間遇見了一個埃及人,把他領到達味前,給他飯吃,給他水喝,
Suka sami wani mutumin Masar a fili suka kawo shi wurin Dawuda. Suka ba shi abinci ya ci, suka kuma ba shi ruwa ya sha.
12 又給他一個無花果餅,兩串乾葡萄;他吃了後,精神就恢復了,因為他已三天三夜沒有吃飯喝水了。
Suka ba shi saura wainan’ya’yan ɓaure da kuma wainan’ya’yan inabi, ya ci ya sami ƙarfi. Gama bai ci ba, bai sha ba, har yini uku da dare uku.
13 達味問他說:「你是誰的人,你是哪裏的﹖」他答說:「我是個埃及少年,為一個阿瑪肋克人做奴隸,因為我害病,我主人拋棄我已三天了。
Dawuda ya tambaye shi ya ce, “Wane ne ubangidanka, kuma daga ina ka fito?” Ya ce, “Ni mutumin Masar ne, bawan wani mutumin Amalek. Maigidana ya ƙyale ni sa’ad da na yi rashin lafiya kwanaki ukun da suka wuce.
14 我們侵擊了革肋提人的南部,猶太的南部和加肋布的南部,放火燒了漆刻拉格」。
Mun kai hari a Negeb ta Keretawa ta Yahuda, da Negeb ta Kaleb, muka kuma ƙone Ziklag.”
15 達味問他說:「你能領我下到這群土匪那裏去嗎﹖」他答說:「你要指著天主給我起誓:不殺我,也不將我交在我主人手裏,那麼我就領你下到這群土那裏去」。艮對他起了誓,
Dawuda ya ce masa, “Za ka iya kai ni wurin maharan nan?” Ya ce, “Idan ka rantse mini da Allah, ba za ka kashe ni ba, ba kuwa za ka mai da ni wurin ubangidana ba, sai in kai ka inda maharan suke.”
16 他便領他下去了。看,土匪都散在各處,正在吃喝,慶祝他們從培肋舍特和猶大地方搶來的大批勝利品。
Ya bi da Dawuda har zuwa can, sai ga su a baje ko’ina a ƙasa, suna ci, suna sha, suna annashuwa saboda yawan ganimar da suka kwashe daga ƙasar Filistiyawa da ƙasar Yahuda.
17 達味從天亮直到晚上,擊殺他們,消滅他們,除四百駱馲騎逃走的兵士外,一個也沒有逃脫。
Dawuda ya yaƙe su tun daga fāɗuwar rana har yammar kashegari. Ba ko ɗaya da ya tsira sai samari ɗari huɗu waɗanda suka tsere a kan raƙuma.
18 凡阿瑪肋克人所據去的,達味都救了回來,也救回了他的兩個妻子。
Dawuda ya ƙwato kome da Amalekawa suka kwashe tare da matarsa biyu.
19 凡被據去的,不論老幼,不論子女,不論什麼財物,一個也不缺,達味全都奪了回來。
Babu abin da ya ɓace, Dawuda ya dawo da kowa, manya da ƙanana,’yan maza da’yan mata duka, da dukan abubuwan da Amalekawa suka kwashe.
20 他們奪回了所有牛羊,牽到達味前說:「這的達味的戰利品」。
Ya kuma ƙwato garkunan tumaki, da na awaki, da na shanu. Mutanensa suka koro shanun, suka yi gaba, suka ce, “Wannan shi ne ganimar Dawuda.”
21 達味回到那二百人那裏,他們因為走路疲乏,不能跟著去,達味就叫他們留在貝索爾河旁,──這些人就前來歡迎跟隨他的軍人也上去向廿請安。
Da Dawuda ya zo wurin mutum ɗari biyu ɗin nan waɗanda suka tafke, suka kāsa binsa, waɗanda aka bari a bakin Kwarin Besor, sai suka taryi Dawuda da mutanensa da suka tafi tare da shi. Sa’ad da Dawuda ya zo kusa da su, sai ya gaishe su.
22 達味前去的人中,有些不良份子無賴之徒高聲嚷說:「他們既然沒有與我們同去,我們所救回來的財物,什麼也不要分給他們,只他們各自帶自己的妻子和兒女4 回去。
Sai dukan mugaye da marasa kirki daga cikin mutanen da suka tafi tare da Dawuda suka ce, “Tun da yake ba su tafi tare da mu ba, ba za mu ba su kome daga cikin ganimar da muka ƙwato ba, sai dai kowane mutum yă ɗauki matarsa da’ya’yansa yă tafi.”
23 達味就說:「兄弟們,上主既然這樣恩待我們,保護我們,把這群前來攻擊我們的土匪,父在我們手裏,你們決不能這樣做。
Dawuda ya ce, “A’a,’yan’uwana ba za ku yi haka da abin da Ubangiji ya ba mu ba. Ya tsare mu, ya kuma bashe sojojin da suka yi gāba da mu a hannuwanmu.
24 在這件事上,誰能依從你們呢﹖那下去打仗的得多少;大家應當平分! 」
Wa zai goyi bayanku a kan wannan al’amari? Wanda ya tafi wurin yaƙi da wanda ya zauna wurin kaya, rabonsu zai zama daidai.”
25 從那天起,達味給以色列立定了這項至今有效的規律和法律。
Dawuda ya sa wannan tă zama dawwammamiyar farilla ga Isra’ila tun daga wannan rana har yă zuwa yau.
26 達味回到漆刻拉格,照猶大所有的城邑,從勝利品中拿了些給他們的長說:「請看! 這是由上主敵人的財物中,給你們分送的禮物」。
Da Dawuda ya iso Ziklag, sai ya aika wa abokansa, dattawan Yahuda da rabo daga cikin ganimar ya ce, “Ga kyauta dominku, daga cikin ganimar maƙiyan Ubangiji.”
27 就是給了那些在貝突耳的,在辣瑪南方的,在雅提爾的,
Kyautar domin waɗanda suke a Betel, da Ramot ta Negeb, da Yattir,
28 在阿辣辣的,在息弗摩特的,在厄市特摩的,
da Arower, da Sifmot, da Eshtemowa,
29 在加爾默耳的,在耶辣默耳人城中的,在刻尼人城中的,
da Rakal, da garuruwan Yerameyelawa, da garuruwan Keniyawa,
30 在曷爾瑪的,在波爾阿商的,在阿塔客的,
da Horma, da Bor-Ashan, da Atak,
31 在赫貝龍的長老,也給了在達味和其他人民曾經漂流過的地方的人。
da Hebron, da dukan wuraren da Dawuda da mutanensa suka taɓa zagawa.

< 撒母耳記上 30 >