< 歷代志上 10 >
1 [撒烏耳陣亡]那時,培肋舍特攻打以色列,以色列人由培肋舍特人面前逃走,在基耳波亞山陣亡的人很多。
To, fa, Filistiyawa suka yi yaƙi da Isra’ilawa; Isra’ilawa kuwa suka gudu a gabansu, da yawa kuma suka mutu a kan Dutsen Gilbowa.
2 培肋舍特人追擊撒烏耳和他的兒子,殺了撒烏耳的兒子約納堂、阿彼納達布和瑪耳基叔亞;
Filistiyawa suka matsa sosai suna bin Shawulu da’ya’yansa maza, suka kuma kashe’ya’yansa maza Yonatan, Abinadab da Malki-Shuwa.
3 戰爭就集中攻打撒烏耳,弓箭手發現了他,他遂為弓箭手所射傷。
Yaƙin ya yi tsanani kewaye da Shawulu, kuma sa’ad da maharba suka rutsa shi, sai suka ji masa rauni.
4 當時撒烏耳對自己的執戟者說:「拔出你的劍來,將我刺死,免得那些為受割損的人來凌辱我。」但是,執戟者十分害怕,不肯作這事;於是撒烏耳拔出劍來,伏劍自刎。
Sai Shawulu ya ce wa mai riƙe masa kayan yaƙi, “Zare takobinka ka soke ni, in ba haka ba waɗannan marasa kaciya za su zo su yi mini ba’a.” Amma mai ɗaukar masa kayan yaƙi ya ji tsoro bai kuwa yi haka ba; saboda haka Shawulu ya zāre takobinsa ya fāɗi a kansa.
Da mai ɗaukar masa kayan yaƙi ya ga Shawulu ya mutu, sai shi ma ya fāɗi a kan takobinsa ya mutu.
6 這樣,撒烏耳和他的三個兒子,並他的全家一同陣亡了。
Ta haka Shawulu da’ya’yansa maza uku suka mutu, dukan gidansa kuwa suka mutu tare.
7 所有住在平原的以色列人見軍隊逃散,撒烏耳和他的三個兒子陣亡了,也都棄城逃走;培肋舍特人遂來住在那裏。
Sa’ad da dukan Isra’ilawa a cikin kwari suka ga cewa mayaƙansu suna gudu, kuma cewa Shawulu da’ya’yansa maza sun mutu, sai suka bar garuruwansu suka gudu. Filistiyawa kuwa suka zo suka zauna a cikinsu.
8 次日,培肋舍特人來剝去陣亡者的衣服時,發現撒烏耳和他的兒子橫臥在基耳波亞山上。
Kashegari, da Filistiyawa suka zo don su tuttuɓe waɗanda suka mutu, sai suka sami Shawulu da’ya’yansa maza sun mutu a Dutsen Gilbowa.
9 他們便剝去了他的衣服,取下他的首級和武器,送到培肋舍特地方,到處給他們的神和人民報喜信。
Suka tuttuɓe shi suka yanke kansa suka ɗauka duk da kayan yaƙinsa, suka kuma aika’yan aika ko’ina a ƙasar Filistiyawa, a yi shela labarin a cikin gumakansu da kuma mutanensu.
10 以後,將撒烏耳的武器放在他們的神廟裏;將他的首級釘在達貢廟內。
Suka sa kayan yaƙinsa a haikalin allahnsu suka kuma rataye kansa a haikalin Dagon.
11 基肋阿得雅貝士的居民,一聽說培肋舍特人對撒烏耳所行的一切,
Sa’ad da mazaunan Yabesh Gileyad suka ji dukan abin da Filistiyawa suka yi wa Shawulu,
12 所有的勇士便起身前去,收殮了撒烏耳和他兒子的屍體,帶回雅貝士,將他們的骨骸葬於雅貝士的篤耨香樹下,且禁食七天。
sai dukan jarumawa suka tafi suka ɗauki jikunan Shawulu da na’ya’yansa maza suka kawo Yabesh. Sa’an nan suka binne ƙasusuwan a ƙarƙashin babban itace oak a Yabesh, suka kuma yi azumi kwana bakwai.
13 撒烏耳之死,是由於他背叛上主,沒有遵守上主的話,並且還求問過招魂的女巫,
Shawulu ya mutu domin rashin aminci ga Ubangiji; bai kiyaye maganar Ubangiji ba, ya ma nemi shawarar mace mai duba,
14 而沒有求其問上主;因此上主使他死亡,將王位移交給葉瑟的兒子達味。
bai kuwa nemi nufin Ubangiji ba. Saboda haka Ubangiji ya kashe shi, ya miƙa mulkin ga Dawuda ɗan Yesse.