< 路加福音 7 >

1 耶稣向民众讲完这一切,就开始向迦百农走去。
Bayan da Yesu ya gama fadar dukan abubuwan da zai fadi a jin kunnen dukan mutanen, sai ya shiga Kafarnahum.
2 那里的一位百夫长有一名十分器重的仆人,但这仆人快要死了。
Bawan wani jarumi, wanda yake kauna, ba shi da lafiya har ma ya kusa mutuwa.
3 百夫长听见耶稣的事,就派来几位犹太人长老过来,求他去医治他的奴仆。
Amma da ya ji labarin Yesu, jarumin ya aiki wadansu dattawan Yahudawa, ya ce a roki Yesu ya zo ya ceci bawansa daga mutuwa.
4 长老们就来见耶稣,恳求他说:“请过来为他做这件事吧,因为他值得你的帮助。
Sa'adda su ka zo kusa da Yesu, su ka roke shi da gaske, cewa, “Wannan ya isa ka yi masa haka,
5 因为他爱我们的人民,给我们建造会堂。”
saboda shi mai kaunar kasar mu ne, kuma shi ne ya gina mana majami'a.
6 耶稣就和他们一同前去。在距离百夫长住宅不远的地方,百夫长派几个朋友来说:“主啊,有劳你大驾光临,实在不敢当,
Sai Yesu ya tafi tare da su. Amma sa'adda ya zo kusa da gidan mutumin, jarumin ya aiki abokansa su ka ce da shi, “Ubangiji kada ka damu domin ni ban isa ka zo gida na ba.
7 我觉得自己实在没有资格去见你,但只要你说一句话,我的仆人就能治愈了。
Shi ya sa na ga ban isa in zo wurinka ba, ka yi magana kadai bawa na kuwa zai warke.
8 我既听命于自己的长官,手下也有士兵。如果我对士兵说‘去吧!’他就会去;对另一个人说‘来吧!’他就会来;我对仆人说‘做这个吧!’他就会做。”
Gama ni ma mutum ne mai iko, ina da sojoji karkashina. Ina iya cewa da wannan, 'Ka je' sai ya tafi, in kuma ce da wani 'ka zo' sai ya zo, in kuma ce da bawa na, 'Yi kaza,' sai ya yi.”
9 耶稣听见这些话,很是惊讶,转身对跟随的众人说:“告诉你们,我在以色列从未见过如此坚定的信心。”
Sa'adda Yesu ya ji haka, ya yi mamakin mutumin, ya juya wajen taron da su ke biye da shi, ya ce, “Na gaya maku, ko a cikin Isra'ila ban sami wani mai bangaskiya irin wannan ba”
10 百夫长的朋友回到家里,发现那奴仆已经痊愈了。
Daga nan wadanda a ka aika, suka dawo gida suka tarar da bawan cikin koshin lafiya.
11 很快,耶稣开始向拿因城走去,身边跟着他的门徒和一大群民众。
Wani lokaci bayan wannan, ya zama Yesu yana tafiya wani gari da ake kira Na'im. Almajiransa su na tare da shi, da kuma taron mutane masu yawa.
12 他走近城门的时候,看到另一条路上有个送葬的队伍,那是一家的独子,母亲是个寡妇。城里有一大群人陪着她。
Sa'adda ya kusa da kofar garin, sai ga wani matacce ana dauke da shi. Kuma shi kadai ne da a wurin mahaifiyarsa. Ita kuwa gwauruwa ce, mutane da dama daga cikin gari suna tare da ita.
13 主看见她便心生怜悯,对她说:“不要哭!”
Da ganin ta, sai Ubangiji ya cika da tausayi a game da ita ya ce da ita, “Kada ki yi kuka.”
14 然后耶稣上前按着棺材,抬棺人站住。 耶稣说:“年轻人,我要对你说,起来吧!”
Sai ya zo ya taba makarar, sai masu dauke da shi su ka tsaya. Ya ce 'Saurayi na ce ma ka ka tashi.”
15 那死去之人就坐起来,开口说话,耶稣把他交给他母亲。
Sai mataccen ya tashi ya fara yin magana. Sai Yesu ya ba mahaifiyar danta.
16 众人都感到敬畏万分,纷纷颂赞上帝:“我们中间出现了伟大的先知!”又说:“上帝眷顾他的子民了!”
Sai tsoro ya kama su duka. Su ka kama yabon Allah, su na cewa, “An ta da wani annabi mai girma a cikinmu” kuma “Allah ya dubi mutanensa.”
17 关于耶稣的消息传遍了犹太和周围各地。
Wannan labari na Yesu, ya ba zu a cikin dukan Yahudiya da yankuna da su ke kewaye.
18 约翰的门徒把这一切都告诉约翰,约翰叫来他的两名门徒,
Almajiran Yahaya suka gaya masa dukan wadannan abubuwa.
19 派他们去主那里,说:“你就是我们一直期待的人?还是我们需要继续等待其他人?”
Sai Yahaya ya kira biyu daga cikin almajiransa, ya aike su wurin Ubangiji, suka ce da shi, “Kai ne mai zuwan nan, ko akwai wani wanda za mu saurari zuwansa?”
20 两人来到耶稣跟前,说:“施洗约翰派我们来问你,‘你就是我们一直期待的人?还是我们需要继续等待其他人?’”
Sa'adda suka zo kusa da Yesu, sai mutanen suka ce, “Yahaya Mai Baftisma, ya aiko mu, mu tambaya, “Kai ne mai zuwan nan, ko akwai wani wanda za mu saurari zuwansa?”
21 耶稣这时正在治愈众多患病、遭难、恶鬼附体之人,让盲人可以看到。
A cikin wannan lokaci, ya warkar da mutane da yawa daga cututtuka da matsaloli da miyagun ruhohi. Makafi da yawa sun sami ganin gari.
22 耶稣回答约翰的门徒:“你们回去把所见所闻都告诉约翰。盲人可以看见,跛人可以走路,麻风患者被治愈,聋人可以听见,死人复活,穷人听到了福音。
Yesu, ya amsa ya ce masu, “Bayan kun tafi, ku ba Yohanna rahoton abin da ku ka ji da abin da ku ka gani. Makafi suna ganin gari, guragu suna tafiya, ana kuma tsarkake kutare. Kurame suna ji, ana tayar da matattu, ana gaya wa matalauta labari mai dadi.
23 那些不会因我而感到冒犯的人,有福了。”
Mai albarka ne mutumin da ya tsaya a kan ba da gaskiya gare ni saboda ayukan da na ke yi.”
24 约翰派来的人走了以后,耶稣开始对众人说:“关于约翰,你们到荒野去寻找他时,希望看到什么?风吹动的芦苇吗?
Bayan da mutanen da Yahaya ya aiko suka tafi, Yesu ya fara yi wa taron magana game da Yahaya. “Me ku ka tafi ku gani a cikin hamada, ciyawa wadda iska ta ke girgizawa?
25 身穿华服之人吗?不,那些衣着华丽、生活奢侈的人都生活在宫殿中。
Amma me ku ka tafi domin ku gani, mutum mai saye da tufafi masu taushi? Duba mutanen da su ke saye da tufafi masu daraja, kuma suna rayuwa cikin jin dadi suna fadar sarakuna.
26 你们是在寻找先知吗?是的,约翰是先知。但我要说的是,他比先知重要得多了。
Amma me ku ka tafi domin ku gani, annabi ne? I, ina gaya ma ku, ya ma fi annabi.
27 经文中记着:‘看啊,我派遣使者先你一步,预备你的道路’,说的就是他。
Wannan shine wanda aka rubuta a kansa, “Duba, ina aika manzo na a gabanka, wanda za ya shirya maka hanya a gabanka.
28 我告诉你们,女人所诞下的人类中,没有谁比约翰更伟大,但他在上帝之国中却是最不重要的那一个!”
Ina gaya maku, a cikin wadanda mata suka haifa, ba wanda ya fi Yahaya girma. Duk da haka, wanda ya fi kankanta a mulkin Allah, ya fi shi girma.
29 经过约翰施洗的众人,甚至包括税吏,听到此言便纷纷决定追随上帝的善意正道。
Sa'anda dukan mutane suka ji haka, har da ma su karbar haraji, suka shaida Allah mai adalci ne. Su na cikin wadanda Yahaya ya yi wa baftisma.
30 但法利赛人和研究法律的专家未受过约翰的洗礼,便拒绝上帝对他们的美意。
Amma Farisawa da wadanda su ke kwararru a cikin shari'ar Yahudawa, wadanda ba shi ne ya yi masu baftisma ba, suka yi watsi da hikimar Allah don kansu.
31 耶稣又说:“这个世界的人可以比作什么呢?他们像什么呢?
Sa'annan Yesu ya ce, “Da me zan kamanta mutanen wannan zamani? Da me suka yi kama?
32 他们就像小孩子坐在巿中心,对彼此说:‘我们给你们吹笛子,你们却不跳舞,我们唱哀歌,你们也不痛哭。’
Suna kama da yaran da suke wasa a kasuwa, wadanda suke magana da junansu suna cewa, “Mun yi maku busa, ba ku yi rawa ba. Mun yi makoki, ba ku yi kuka ba.”
33 施洗约翰来了,不吃饭,不喝酒,你们就说他是恶魔附体。
Haka, Yahaya ya zo, bai ci gurasa ba, bai sha ruwan inabi ba, amma ku ka ce, 'Aljani ne yake mulkinsa.
34 现在人子来了,看他吃喝你们又说:‘你看,这人又贪吃,又贪杯,还与税吏和罪人为伍。’
Dan Mutum, ya zo, yana ci, yana sha, amma, kuka ki shi, kuna cewa dubi mutum mai hadama, mai shan ruwan inabi da yawa, abokin masu karbar haraji da masu zunubi!
35 但上帝的智慧之道,已被他的所有追随者所证实!”
Amma hikimar Allah tana shaidar dukan 'yayanta.”
36 有一个法利赛人请耶稣同他一起用餐,于是他就到那位法利赛人家中赴宴。
Wata rana wani Bafarise, ya roki Yesu ya je ya ci abinci tare da shi. Bayan da Yesu ya shiga gidan Bafarisen, ya zauna a teburi domin ya ci abinci.
37 城里有一个女人,是个罪人。得知他在法利赛人家里吃饭,就拿着一瓶香膏来到这里。
Sai ga wata mace mai zunubi, ta fito daga cikin birni. Sa'anda ta ji labari Yesu yana gidan Bafarisen, domin ya ci abinci. Ta dauki tandun mai na alabastar mai kamshi.
38 她跪在耶稣身边,眼泪沾湿了他的脚。于是她用自己的头发把泪水擦干,然后亲吻他的脚,抹上香膏。
Ta tsaya kusa da Yesu tana kuka. Ta fara jika kafafunsa da hawayenta, tana shafe kafafunsa da gashin kanta. Tana yi wa kafafunsa sumba, tana shafe su da turare.
39 请耶稣吃饭的法利赛人看见她,心想:“这人若真的是先知,必定知道是谁在触摸他。这是怎样的女人,她是个罪人!”
Sa'anda Bafarisen da ya gaiyaci Yesu, ya ga haka, sai ya yi tunani a cikin ransa, da cewa, “In da wannan mutum annabi ne, da ya gane ko wacce irin mace ce, wannan da take taba shi, ita mai zunubi ce.”
40 于是耶稣开口说:“西门,我有话要对你说。”他说:“老师,请讲。”
Yesu ya amsa ya ce masa, “Siman, ina so in gaya maka wani abu.” Ya ce, “malam sai ka fadi!”
41 耶稣说:“有两个人欠了一个债主的钱,一人欠 500 银币,一人欠 50 银币。
Yesu ya ce, “wani mutum mai ba da bashi yana bin wadansu mutane su biyu kudi, yana bin dayan sule dari, dayan kuma yana bin sa sule hamsin.
42 他们都无力偿还,于是债主就免了两人的债务。这两个人哪一个人会更爱他?”
Da yake ba su da kudin da za su iya biyan sa, sai ya yafe masu, su duka biyu. A cikin su biyu, wanne ne zai fi nuna kauna ga wannan mutum?”
43 西门回答:“我想是那个欠债多的人会更爱他。”耶稣说:“你说对了。”
Siman ya amsa ya ce, “Ina tsammani wanda ya yafe wa kudi da yawa.” Yesu ya amsa ya ce masa, “Ka shari'anta dai dai.”
44 于是他转身向着那女人,对西门说:“你看到这女人吗?我走进你家,你没有给我水洗脚,但她却用眼泪湿了我的脚,用头发擦干。
Yesu ya juya wajen matar, ya ce da Siman, “Ka ga matan nan. Na shiga gidanka. Ba ka ba ni ruwa domin kafafuna ba, amma ita ta ba ni, da hawayenta ta wanke kafafuna, ta kuma shafe su da gashin kanta.
45 你没有亲吻我,但这女人自我进来,就一直在亲吻我的脚。
Kai ba ka yi ma ni sumba ba, amma ita ta yi, tun sa'adda na shigo nan ba ta dena sumbatar kafafuna ba.
46 你没有在我的头上涂抹香膏,但这女人却用香膏抹我的脚。
Kai ba ka shafe kai na da mai ba, amma ita ta shafe kafafuna da turare.
47 所以我告诉你,因为她的很多罪都被赦免了,所以她心中的爱多。如果被赦免的少,心中爱的也少。”
Saboda haka, ita wadda ta ke da zunubi da yawa ta bayar da mai yawa, ta kuma nuna kauna mai yawa. Amma shi wanda aka gafarta wa kadan, ya kuma nuna kauna kadan.”
48 然后耶稣对女人说:“你的罪被赦免了。”
Daga nan sai ya ce mata, “An gafarta zunubanki.”
49 一同进餐之人心里说:“这是谁啊?竟然可以宽恕罪过?”
Wadanda su ke a nan zaune tare da shi suka fara magana da junansu, “Wanene wannan wanda har yake gafarta zunubai?
50 耶稣对那女人说:“你的信任已经拯救了你,安心地去吧。”
Sai Yesu ya ce da matar, “Bangaskiyarki ta cece ki. Ki tafi da salama.”

< 路加福音 7 >