< 使徒行传 22 >
1 他说:“各位父老兄弟,请听我在你们面前的申辩。”
“’Yan’uwa da iyaye, ku saurari kāriyata yanzu.”
2 众人听到保罗用阿拉姆语说话,立刻变得非常安静。
Da suka ji ya yi musu magana da Arameyik, sai suka yi tsit. Sai Bulus ya ce,
3 他开始讲述:“我是犹太人,生在基利家的大数。但其实我是在这座城里长大,在迦玛列门下接受教育。老师教育我要严格遵守祖先的律法,我满腔热情地对待上帝,就像今天这里的所有人一样。
“Ni mutumin Yahuda ne haifaffen Tarshish na Silisiya, amma a nan birnin ne aka rene ni. Aka horar da ni sosai cikin dokokin kakanninmu a ƙarƙashin Gamaliyel ni ma dā mai himma ne cikin bauta wa Allah kamar yadda kowannenku yake a yau.
4 我也曾经迫害信奉此道之人,将他们处死,把男女信徒投入监狱。
Na tsananta wa masu bin wannan Hanyar har ga mutuwarsu, ina kama maza da mata ina kuma jefa su cikin kurkuku,
5 大祭司和公议会的长老都可以为我作证。我曾收到他们的授意信,要求处理在大马士革的犹太人信徒。于是我去了那里捉拿那些人,把他们带到耶路撒冷接受惩罚。
kamar yadda babban firist da dukan Majalisa za su iya shaida. Na ma karɓi wasiƙu daga gare su zuwa ga’yan’uwansu a Damaskus, na kuma tafi can don in kawo waɗannan mutane a daure zuwa Urushalima don a hukunta su.
6 那天大约中午时分,我正在去往大马士革的路上,即将抵达目的地时,忽然一束耀眼的光芒从天而降,环绕着我。
“Wajen tsakar rana da na yi kusa da Damaskus, ba zato ba tsammani sai wani babban haske daga sama ya haskaka kewaye da ni.
7 我仆倒在地,只听见一个声音对我说:‘扫罗啊,扫罗,你为什么迫害我?’
Sai na fāɗi a ƙasa na kuma ji wata murya ta ce mini, ‘Shawulu! Shawulu! Don me kake tsananta mini?’
8 我答道:‘主啊,你是谁?’ 他说:‘我就是你迫害的拿撒勒人耶稣。’
“Sai na yi tambaya na ce, ‘Wane ne kai, ya Ubangiji?’ “Ya amsa ya ce, ‘Ni ne Yesu Banazare, wanda kake tsanantawa.’
9 与我同行之人只看见那束光,却听不到与我说话的声音。
Abokan tafiyata suka ga hasken, amma ba su fahimci muryar mai magana da ni ba.
10 我说:‘主啊,我该怎么做?’ 主告诉我:‘站起来,进到大马士革城里,那里会有人告知安排你做的事情。’
“Sai na yi tambaya, na ce, ‘Me zan yi, ya Ubangiji?’ “Ubangiji ya ce, ‘Tashi, ka tafi cikin Damaskus. A can za a faɗa maka duk abin da aka shirya za ka yi.’
11 那束光如此强烈,我的双眼便看不到了,我的同伴们牵着我的手走进了大马士革。
Abokan tafiyata suka ja ni a hannu zuwa cikin Damaskus, saboda ƙarfin hasken ya makanta ni.
12 有一个人名叫亚拿尼亚,是一名遵守律法的虔诚之人,当地所有犹太人都很敬重他。
“Wani mutumin da ake kira Ananiyas ya zo ya gan ni. Shi mai ibada ne wajen kiyaye dokoki wanda dukan Yahudawan da suke zama a can suna girmama shi ƙwarai.
13 他站在我旁边对我说:‘扫罗兄弟,你现在可以看见了。’就在那一刻,我又能看到了。我看到了他。
Ya tsaya kusa da ni ya ce, ‘Ɗan’uwa Shawulu, ka sami ganin garinka!’ A daidai lokacin kuwa na iya ganinsa.
14 他对我说:‘我们祖先的上帝指认你来理解他的旨意,去见真正良善的正义之人,去听见他要对你所说的一切。
“Sa’an nan ya ce, ‘Allah na kakanninmu ya zaɓe ka ka san nufinsa ka kuma ga Mai Adalcin nan ka kuma ji kalmomi daga bakinsa.
15 对于你的所见所闻,你将向所有人作证。所以你还在等什么呢?
Za ka zama mai shaidarsa ga dukan mutane game da abin da ka gani ka kuma ji.
Yanzu me kake jira? Ka tashi, a yi maka baftisma, a wanke zunubanka, ta wurin kira bisa ga sunansa.’
17 我回到耶路撒冷后,有一次在殿里祷告时,忽然在恍惚间看到了异象。
“Sa’ad da na dawo Urushalima ina cikin addu’a a haikali, sai na ga wahayi
18 主在异象中对我说:‘快!你必须尽快离开耶路撒冷,因为他们无法接受你所讲述关于我的一切。’
na ga Ubangiji yana magana. Ya ce mini, ‘Maza! Ka bar Urushalima, gama ba za su yarda da shaidarka game da ni ba.’
19 我回答:‘主啊,他们肯定知道,我曾在很多会堂中拷打信你之人,将它们送进监牢,
“Na amsa na ce, ‘Ubangiji, waɗannan mutane sun san cewa na bi majami’a-majami’a na jefa waɗanda suka gaskata da kai a cikin kurkuku, in kuma yin musu dūka.
20 司提芬因为为你作证而被杀害的时候,我就站在那里,而且完全支持那些杀死他的人,还为他们拿着衣服。’
Sa’ad da kuma aka zub da jinin Istifanus mashaidinka, na tsaya can ina ba da goyon bayana ina kuma tsaron tufafin masu kisansa.’
21 主对我说:‘现在就离开吧,我要派你到远方异教徒那里去。’”
“Sa’an nan Ubangiji ya ce mini, ‘Je ka; zan aike ka can nesa a wurin Al’ummai.’”
22 众人一直都在听他说的话,但听到这里,他们就高喊:“应该把这种人从世间除掉,他不配活着!”
Taron suka saurari Bulus sai da ya yi wannan magana. Sa’an nan suka ɗaga muryoyinsu suka yi ihu suka ce, “A raba duniya da wannan mutum! Bai cancanci yă rayu ba!”
Da suna ihu suna kaɗa mayafansu suna da tā da ƙura sama,
24 就在这时,千夫长下令把保罗带到军营,命人用鞭刑拷问他,想要找出高声喊叫的民众反对他的原因。
sai shugaban ƙungiyar sojan ya umarta a kai Bulus a barikin soja. Ya ba da umarni a yi masa bulala a kuma tambaye shi abin da ya sa mutane suke masa ihu haka.
25 士兵将他四肢伸开,用皮带将其捆住,准备施以鞭刑。这时保罗对站在旁边的百夫长说:“你们鞭打一个还没有定罪的罗马公民,这合法吗?”
Suna kwantar da shi ke nan domin a yi masa bulala, sai Bulus ya ce wa jarumin da yake tsaye a nan, “Ashe, daidai ne bisa ga doka a yi wa ɗan ƙasar Roma bulala wanda ba a ma tabbatar da laifi a kansa ba?”
26 百夫长听言就去报告千夫长,说:“这个人是罗马公民,该怎么办?”
Da jarumin ya ji haka sai ya je wurin shugaban ƙungiyar sojan ya ce masa, “Me kake so yi ne? Wannan mutum ɗan ƙasar Roma ne.”
27 千夫长就过来问保罗:“告诉我,你真是罗马公民吗?”他说:“是的。”
Sai shugaban ƙungiyar sojan ya je ya tambayi Bulus ya ce, “Faɗa mini, kai ɗan ƙasar Roma ne?” Bulus ya ce, “I.”
28 千夫长说:“为了获得罗马公民的身份,我可是花了一大笔钱。”保罗说:“我生下来就是罗马公民。”
Sai shugaban ƙungiyar sojan ya ce, “Sai da na biya kuɗi mai yawa kafin in zama ɗan ƙasa.” Bulus ya ce, “Ni kuwa an haife ni ɗan ƙasa.”
29 于是那些想要拷问他的人立刻走开了。得知他是罗马公民,又曾被捆绑起来,千夫长感到很害怕。
Waɗanda dā suke shirin yin masa tambayoyi suka ja da baya nan da nan. Shugaban ƙungiyar sojan kansa ya tsorata da ya fahimci cewa ya sa wa Bulus, ɗan ƙasar Roma sarƙa.
30 第二天,千夫长想要了解为什么犹太人要控告保罗,于是就解开他身上的锁链,随后召集祭司长和公议会全体成员,将保罗带到众人面前。
Kashegari da yake shugaban ƙungiyar sojan ya so yă tabbatar da ainihin abin da ya sa Yahudawa suke zargin Bulus, sai ya sake shi ya kuwa umarci manyan firistoci da dukan Majalisar su taru. Sa’an nan ya kawo Bulus ya sa ya tsaya a gabansu.