< Milu Pareinae 36 >
1 Joseph imthung dawk hoi Manasseh capa Makhir capa Gilead catoun imthung kahrawikungnaw hmalah lawk a dei awh.
Sai shugabannin gidajen iyalan Gileyad ɗan Makir, ɗan Manasse, waɗanda suka fito daga kabilar zuriyar Yusuf, suka zo, suka yi magana a gaban Musa da shugabanni, shugabannin iyalan Isra’ilawa.
2 Ahnimouh ni, BAWIPA ni Isarel catounnaw hah cungpam rayu hoi a coe awh hane ram poe hanlah, ka bawipa Mosi hah kâ a poe teh, hmaunawngha Zelophehad canunaw a coe hane râw hah BAWIPA ni ka bawipa koe kâ a poe toe.
Suka ce, “Sa’ad da Ubangiji ya umarce ranka yă daɗe, yă raba ƙasar gādo ga Isra’ilawa ta wurin ƙuri’a, ya umarce ka, ka ba wa’ya’ya matan nan na Zelofehad ɗan’uwanmu gādonsa.
3 Hatei, ahnimouh ni Isarel catoun thung dawk hoi miphun alouke capa koe vâ sak pawiteh, na mintoenaw e ram a coe awh e hah la pouh vaiteh, a vâ koelae ram miphun koe lah a kâthap han. Hottelah coe tangcoung e ram dawk hoi tâcokhai han.
To, a ce sun auri mutane daga waɗansu kabilan Isra’ilawa fa; ka ga, za a ɗebe gādonsu daga gādon kakanninmu a ƙara wa gādon kabilan mutanen da suka aura ke nan. Ta haka za a ɗebe sashe daga gādon da aka ba mu ke nan.
4 Hahoi Isarel catounnaw e Jubili a pha toteh, a ram hah a vanaw e miphunnaw ni coe e ram lah thapsin lah ao han. Hottelah mintoenaw e miphun ram thung dawk hoi let na lawp pouh awh han telah ati.
Sa’ad da Shekara ta Murnar Isra’ilawa ta kewayo, za a haɗa gādonsu da na kabilan mutanen da suka aura, a kuma ba su mallakar gādon da aka ɗebe daga kabilar kakanninmu.”
5 Hatdawkvah, Mosi ni BAWIPA lawk patetlah Isarel catounnaw hah kâ a poe teh, Joseph capa hoi miphunnaw ni a dei e a thuem.
Ta wurin umarnin Ubangiji, Musa ya ba Isra’ilawa wannan umarni, “Abin da kabilar zuriyar Yusuf suke faɗi, daidai ne.
6 Zelophehad canunaw kong dawkvah BAWIPA ni kâ a poe e teh hettelah doeh. Ahawi ati e pueng vâ naseh, hatei a napanaw e miphun hah vâ awh naseh telah ati.
Ga abin da Ubangiji ya umarta saboda’ya’ya matan nan na Zelofehad. Za su iya auri duk wanda suka ga dama, muddin sun yi aure a cikin kabilar kakanninsu.
7 Hatdawkvah, Isarel catounnaw e ram teh, miphun alouklouk koe voutsout puen laipalah, Isarel catounnaw ni a na mintoenaw e ram teh pou a ham awh han.
Ba gādon Isra’ilan da za a ba wa wata kabila daga wata kabila, gama kowane mutumin Isra’ila zai riƙe gādonsa na kabilar da ya gāda daga kakanninsa.
8 Isarel catounnaw thung dawk râw ka pang hane canunaw pueng teh, Isarel catounnaw ni a na mintoenaw e ram lah kaawm e pou a ham thai nahan, a na pa miphun thung e a yu a la hanlah ao.
Kowace’ya wadda ta ci gādon ƙasa, a kowace kabilar Isra’ilawa, dole tă auri wani cikin kabilar kakanninta, saboda kowane mutumin Isra’ila yă mallaki gādon kakanninsa.
9 Ram teh miphun alouklouk koe puen thai mahoeh. Bangkongtetpawiteh, Isarel catounnaw ni amamae ram hah pou a pang awh e lah kaawm han telah a dei.
Ba gādon da za a ba wa wata kabila daga wata kabila, gama kowace kabilar Isra’ilawa za tă riƙe mallaka da ta gāda.”
10 Hottelah, BAWIPA ni Mosi kâ a poe e patetlah Zelophehad canunaw ni a sak awh van.
Saboda haka’ya’yan Zelofehad mata suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa.
11 Zelophehad canunaw Mahlah, Tirzah hoi Hoglah, Milkah hoi Noah tinaw ni a na pa e hmaunawnghanaw e capanaw hah a vâ awh.
’Ya’yan Zelofehad mata, Mala, Tirza, Hogla, Milka da Nowa, suka auri’ya’yan’yan’uwa na gefen mahaifinsu.
12 Joseph capa Manasseh e capa hah a vâ awh teh, a ram teh a na pa miphunnaw ni a coe e râw lah pou a kangning.
Suka yi aure cikin kabilar zuriyar Manasse ɗan Yusuf, gādonsu kuwa ya kasance a cikin iyali da kuma kabilar mahaifinsu.
13 Hetnaw heh Jeriko tengpam Jordan namran Moab tanghling dawkvah, BAWIPA ni Mosi hno lahoi Isarelnaw koevah, kâ a poe e kâpoelawknaw hoi lawkcengnaenaw doeh.
Waɗannan su ne umarnai da ƙa’idodin da Ubangiji ya ba wa Isra’ilawa ta wurin Musa, a filayen Mowab kusa da Urdun, ɗaura da Yeriko.