< Luk 2 >

1 Hatnavah Sizar Augustus ni talaivan milu parei hanelah kâ a poe.
A waɗancan kwanaki, Kaisar Augustus ya ba da doka cewa ya kamata a yi ƙidaya a dukan masarautar Roma.
2 Siria ram dawk Quirinius ni a uk navah, hote miilu pareinae teh hmaloe pasuek poung e lah ao.
(Wannan ce ƙidaya ta fari da aka yi a lokacin da Kwiriniyus yake gwamnar Suriya.)
3 Taminaw pueng teh min poe hanelah ama kho lengkaleng a ban awh.
Sai kowa ya koma garinsa don a rubuta shi.
4 Devit e catoun lah kaawm e Joseph hoi a ham tangcoung lah kaawm e Meri teh min poe hanelah,
Saboda haka Yusuf ma ya haura daga Nazaret a Galili zuwa Yahudiya, ya tafi Betlehem garin Dawuda, don shi daga gida da kuma zuriyar Dawuda ne.
5 Galilee ram Nazareth kho koehoi Judah ram Bethlehem telah min poe e Devit kho lah a cei roi. Hatnavah Meri e a von thung e camo teh a tang toe.
Ya tafi can don a rubuta shi tare da Maryamu, wadda aka yi masa alkawari zai aura, tana kuwa da ciki.
6 Bethlehem kho ao navah, camo khe nahan hnin a kuep toung dawkvah camin teh a khe.
Yayinda suke can, sai lokacin haihuwar jaririn ya yi,
7 A kâhat nahane hmuen ao hoeh dawkvah, camo teh hni hoi a kayo teh maito dokko dawk a pâ i roi.
ta kuwa haifi ɗanta na fari. Ta nannaɗe shi a zane ta kuma kwantar da shi cikin wani kwami, don ba su sami ɗaki a masauƙi ba.
8 Hote ram dawk, tukhoumnaw ni khohmo vah amamae tuhu hah kahrawngum vah a ring awh.
Akwai makiyaya masu zama a fili kusa da wurin, suna tsaron garkunan tumakinsu da dare.
9 Hatnavah Cathut e kalvantami buet touh ahnimouh koe a kamnue teh Cathut e raeng teh atengpam pheng a ang dawkvah, ahnimouh teh a lungtâsue awh teh a taki awh.
Sai wani mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare su, ɗaukakar Ubangiji kuma ta haskaka kewaye da su, suka kuwa tsorata ƙwarai.
10 Kalvantami nihai, na lungtâsue awh hanh awh, taminaw pueng hane, lunghawinae kamthang kahawi nangmouh koe na dei pouh awh. Hote kamthang kahawi ni tami pueng lunghawinae koe a pha sak han.
Amma mala’ikan ya ce musu, “Kada ku ji tsoro. Na kawo muku labari mai daɗi na farin ciki mai yawa ne wanda zai zama domin dukan mutane.
11 Sahnin vah, Devit kho dawk, rungngangkung Bawi Khrih teh a khe toe.
Yau a birnin Dawuda an haifa muku Mai Ceto; shi ne Kiristi Ubangiji.
12 Nangmouh ni bangtelah hoi maw na panue awh han tetpawiteh, camo teh hni hoi a kayo vaiteh maito dokko dawk a payan e na hmu awh han telah atipouh.
Wannan zai zama alama a gare ku. Za ku tarar da jariri a nannaɗe a zane kwance a kwami.”
13 Hatnavah, kalvantaminaw hoi kalvanlae ransahu a kamnue awh teh, Bawipa a pholen awh.
Ba labari sai ga taron rundunar sama suka bayyana tare da mala’ikan, suna yabon Allah suna cewa,
14 Cathut teh lathoung poung lah bawilennae awm lawiseh. Talai van roumnae awm lawiseh, telah a ti awh.
“Ɗaukaka ga Allah a can cikin sama, a duniya kuma salama ga mutane waɗanda tagomashinsa yake bisansu.”
15 Kalvantaminaw, kalvan lah a luen hnukkhu tukhoumnaw ni, maimanaw Bethlehem kho koe lah cet awh sei. Cathut ni na patue e hno khen a sei telah buet touh hoi buet touh a ka dei awh.
Da mala’ikun suka bar su, su suka koma sama, sai makiyayan suka ce wa juna, “Mu je Betlehem mu ga wannan abin da ya faru, wanda Ubangiji ya sanar mana.”
16 Hathnukkhu, ahnimanaw teh karanglah a cei awh teh, Joseph hoi Meri ni maito dokko dawk a pâ i e camo hah a hmu awh.
Sai suka tafi da sauri, suka tarar da Maryamu da Yusuf, da kuma jaririn kwance a kwami.
17 A hmu hnukkhu hoi amamouh ni a thai e camo e a kong hah hmuen tangkuem koe a pâpho awh.
Sa’ad da suka gan shi, sai suka baza maganar da aka gaya musu game da yaron,
18 Tukhoumnaw ni, a dei e lawk kathainaw pueng ni kângai lah a ru awh.
duk kuwa waɗanda suka ji wannan, suka yi mamaki a kan abin da makiyayan suka faɗa.
19 Meri teh hote a konglamnaw pueng a pâkuem teh luepluep a pouk.
Amma Maryamu ta riƙe dukan waɗannan abubuwa ta kuma yi ta tunaninsu a zuciyarta.
20 Tukhoumnaw teh amamouh koe pâpho pouh e patetlah a hmu awh navah Cathut a pholen awh teh a ban awh.
Makiyayan kuwa suka koma, suna ɗaukaka suna kuma yabon Allah saboda dukan abubuwan da suka ji, suka kuma gani, yadda aka gaya musu.
21 Ataroe hnin a pha navah camo teh vuensoma awh, camo a von hoeh nahlan vah kalvantami ni min poe e patetlah Jisuh telah a phung awh.
A rana ta takwas, da lokaci ya yi da za a yi masa kaciya, sai aka ba shi suna Yesu, sunan da mala’ika ya ba shi kafin a yi cikinsa.
22 Hathnukkhu hoi Mosi e kâlawk patetlah kâpasu thoungnae hnin a kuep navah, a manu hoi a na pa ni camo teh Jerusalem kho lah a ceikhai roi.
Da lokacin tsarkakewarsu bisa ga Dokar Musa ya cika, sai Yusuf da Maryamu suka ɗauke shi suka haura zuwa Urushalima don su miƙa shi ga Ubangiji
23 Ca caminnaw pueng teh Cathut hanelah thoungsak han telah kâlawk dawk thut tangcoung e patetlah Cathut koe a kâhnawng hnukkhu,
(yadda yake a rubuce a Dokar Ubangiji cewa, “Kowane ɗan fari, za a keɓe shi ga Ubangiji”),
24 Âbakhu kahni touh hoi thuengnae na sak han telah kâlawk dawk a dei e patetlah a sak awh.
don kuma su miƙa hadaya bisa ga abin da aka faɗa a Dokar Ubangiji cewa, “kurciyoyi biyu ko’yan tattabarai biyu.”
25 Hatnavah Jerusalem kho dawk Simeon tie tami buet touh ao. Hote tami teh tamikalan, a lawk dawk kaawm e tami, Isarelnaw hloutnae ka ngaihawi e tami lah ao. Kathoung Muitha teh ahni dawk ao.
To, akwai wani mutum a Urushalima mai suna Siman, shi mai adalci da kuma mai ibada. Yana jiran fansar Isra’ila, Ruhu Mai Tsarki kuwa yana tare da shi.
26 Ahni teh Bawipa Khrih hah na hmu hoehnahlan na dout mahoeh telah, Kathoung Muitha e pâpho pouh e ka coe e tami lah ao.
An bayyana masa ta wurin Ruhu Mai Tsarki cewa ba zai mutu ba sai ya ga Kiristi na Ubangiji.
27 Hatnavah, ahni teh Muitha lahoi bawkim dawk a cei teh, a manu hoi a na pa ni Camo teh kâlawk patetlah sak hanelah a hrawi roi.
Da Ruhu ya iza shi, sai ya shiga cikin filin haikali. Sa’ad da iyayen suka kawo jaririn nan Yesu don su yi masa abin da al’adar Doka ta bukaci,
28 Simeon ni ahni hah a tawm teh, Cathut a pholen.
sai Siman ya karɓi yaron a hannuwansa ya yabi Allah, yana cewa,
29 Bawipa, na lawk patetlah nange na san kai lungmawngnae ka hmu toe.
“Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kamar yadda ka yi alkawari, yanzu ka sallami bawanka lafiya.
30 Bangkongtetpawiteh, Bawipa e miphunnaw tawmdawm hanelah hai thoseh,
Gama idanuna sun ga cetonka,
31 Jentelnaw ang sak hanelah hai thoseh,
wanda ka shirya a gaban dukan mutane,
32 Isarel taminaw pueng hanelah rakueng tangcoung e rungngangnae teh atu ka mit hoi ka hmu toe telah a dei.
haske don bayyanawa ga Al’ummai da kuma ɗaukaka ga mutanenka Isra’ila.”
33 Hote lawk hah Joseph hoi Meri ni a thai navah kângai lah a ru roi.
Mahaifin yaron da kuma mahaifiyarsa suka yi mamaki abin da aka faɗa game da shi.
34 Simeon ni ahnimanaw hah yawhawinae a poe teh, Meri koevah, hete camo teh Isarelnaw moikapap rawp nahane hoi thaw nahanelah ao vaiteh, oun e lah ao nahanelah hruek e lah ao toe.
Sa’an nan Siman ya sa musu albarka ya ce wa Maryamu mahaifiyarsa, “An ƙaddara yaron nan yă zama sanadin fāɗuwa da tashin mutane da yawa a Isra’ila, zai kuma zama alamar da mutane ba za su so ba,
35 Taminaw e pouknae pueng a kamnue nahanelah, na lungthin hai tahloi ni a sei han telah a dei.
ta haka za a fallasa tunanin zukatan mutane da yawa. Ke ma, takobi zai soki zuciyarki.”
36 Asher miphun, Fanuel e canu Anna telah a min kâphung e profet napui a kum kacue e buet touh ao. Ahni teh a vâ hoi kum sari touh ao hnukkhu hoi,
Akwai wata annabiya ma, mai suna Anna, diyar Fanuwel, na kabilar Asher. Ta tsufa kutuf; ta yi zama da mijinta shekaru bakwai bayan sun yi aure,
37 a kum, rui taroe kum pali totouh lahmai lah ao teh, ratoumnae hoi rawcahainae lahoi yah, khohmo khodai Cathut koe a kâpoe teh bawkim dawk ao.
ta kuwa zama gwauruwa sai da ta kai shekaru tamanin da huɗu. Ba ta taɓa barin haikali ba, tana sujada dare da rana, tana kuma azumi da addu’a.
38 Ahni hai tang a kâen teh Cathut a pholen. Jerusalem kho dawk ratangnae kangaihawinaw pueng koe hote Como e a kong a dei pouh.
Tana haurawa wurinsu ke nan a wannan lokaci, sai ta yi wa Allah godiya ta kuma yi magana game da yaron nan ga dukan waɗanda suke sauraron fansar Urushalima.
39 A manu hoi na pa ni hai Cathut e kâlawk patetlah koung a tarawi hnukkhu, ama kho Galilee ram Nazareth kho lah a ban roi.
Bayan da Yusuf da Maryamu suka gama yin dukan abubuwan da Dokar Ubangiji ta bukaci, sai suka koma Galili suka tafi Nazaret garinsu.
40 Camo hai a roung teh lungangnae hoi akawi. Cathut e lungmanae teh ahni dawk ao.
Yaron kuwa ya yi girma ya yi ƙarfi; ya cika da hikima, alherin Allah kuwa yana bisansa.
41 Kum tangkuem ceitakhai pawi saknae tueng a pha navah a manu hoi a na pa teh Jerusalem kho lah ouk a cei awh.
Kowace shekara, iyayen Yesu sukan je Urushalima don Bikin Ƙetarewa.
42 Jisuh kum hlaikahni touh a pha navah pawi e singyoe patetlah Jerusalem kho lah a cei awh teh,
Da Yesu ya cika shekaru goma sha biyu, sai suka tafi Bikin bisa ga al’ada.
43 pawi a baw hnukkhu vah a manu hoi a na pa teh a ban roi nah, camo Jisuh teh Jerusalem khovah ao e hah panuek roi hoeh.
Bayan Bikin, da iyayen suka kama hanya don su koma gida, sai Yesu, yaron nan, ya tsaya a Urushalima, ba da saninsu ba.
44 A huikonaw hoi a tho mue telah a pouk dawkvah hnin touh lamcei a cei awh toe.
Su kuwa sun ɗauka yana tare da su, saboda haka, suka yi ta tafiya har na yini guda. Sa’an nan suka fara nemansa cikin’yan’uwansu da abokansu.
45 Camo teh a huikonaw koe ao hoeh toung dawkvah, Jerusalem kho lah bout a ban roi.
Da ba su gan shi ba, sai suka koma Urushalima nemansa.
46 Hnin thum touh a ro hnukkhu vah, Jisuh teh bawkim dawk kacangkhainaw e rahak a tahung teh ahnimanaw hoi lawk kâ pacei awh e hah a manu hoi a na pa ni a hmu roi.
Bayan kwana uku, sai suka same shi a filin haikali zaune a tsakiyar malamai, yana sauraronsu yana kuma yi musu tambayoyi.
47 Jisuh e lungangnae hoi panuenae lawk ka thai e naw pueng ni a kângairu awh.
Dukan waɗanda suka ji shi, suka yi mamakin fahimtarsa, da amsoshinsa.
48 A na pa yuvâ ni ahni teh a kâhmo navah, a kângairu roi. A manu niyah ka ca bangkongmaw kaimouh roi koe telah koe na o. Na pa kaimouh roi ni ka puen roi dawkvah na tawng roi atipouh.
Da iyayensa suka gan shi sai suka yi mamaki. Mahaifiyarsa ta ce masa, “Ɗana, don me ka yi mana haka? Ni da mahaifinka duk mun damu muna nemanka.”
49 Jisuh ni bangkongmaw kai khuek na tawng roi vaw, kai teh a Pa e im dawk ka o han tie hah na panuek hoeh na maw.
Sai ya ce, “Don me kuke nemana? Ba ku san cewa, dole in kasance a gidan Ubana ba?”
50 Hateiteh, Jisuh ni a dei e a manu hoi a na pa ni thai panuek roi hoeh.
Amma ba su fahimci abin da yake faɗin musu ba.
51 Hattoteh Jisuh ni ahnimouh koe a cei van teh Nazareth kho a pha navah a manu hoi a na pa e kâ a ngai pouh. A manu ni teh hete a konglamnaw pueng a lungthin dawk khik a pâkuem.
Sai ya koma Nazaret tare da su, yana yi musu biyayya. Mahaifiyarsa kuma ta riƙe dukan waɗannan abubuwa a zuciyarta.
52 Jisuh teh thoumthai lungangnae dawk a roung teh, Cathut hmalah hoi tami hmalah, minhmai kahawi a hmu.
Yesu kuwa ya yi girma, ya kuma ƙaru cikin hikima, ya kuma sami tagomashi a wurin Allah da mutane.

< Luk 2 >