< Jawhan 11 >

1 Bethani kho kaawm e Meri hoi Martha e a thangroi Lazarus tie teh a pataw.
To, an yi wani mutum mai suna Lazarus wanda ya yi rashin lafiya. Shi daga Betani ne, ƙauyen su Maryamu da’yar’uwarta Marta.
2 Ka pataw e Lazarus e a tawncanu Meri teh Jisuh khok dawk hmuitui a hluk pouh teh a sam hoi ka hui e Meri doeh.
Maryamun nan kuwa, wadda ɗan’uwanta Lazarus yake rashin lafiya, ita ce ta zuba wa Ubangiji turare ta kuma goge ƙafafunsa da gashin kanta.
3 A hmaunawngha roi ni, Jisuh koevah tami a ceisak teh, Bawipa na lungpataw e Lazarus teh a pataw atipouh.
Saboda haka’yan’uwansa mata suka aika da saƙo wa Yesu cewa, “Ubangiji, wannan da kake ƙauna yana rashin lafiya.”
4 Jisuh ni a thai navah, hote patawnae teh due patawnae nahoeh. Cathut a lentoe a kamnue nahane doeh. Hote patawnae dawk Cathut Capa e a lentoe a kamnue han, atipouh.
Sa’ad da ya ji haka, sai Yesu ya ce, “Wannan rashin lafiya ba zai kai ga mutuwa ba. A’a, sai dai don a ɗaukaka Allah a kuma ɗaukaka Ɗan Allah ta wurin wannan.”
5 Jisuh ni Martha nuca hoi Lazarus hai a lungpataw.
Yesu kuwa yana ƙaunar Marta da’yar’uwarta da kuma Lazarus.
6 Lazarus a pataw e a thai ei teh roup cet laipalah hote hmuen koe hnin hni touh ao takhai.
Duk da haka sa’ad da ya ji Lazarus ba shi da lafiya, sai ya ƙara kwana biyu a inda yake.
7 Hahoi a hnukkâbangnaw hanlah, Judah lah bout cet awh sei atipouh.
Sai ya ce wa almajiransa, “Mu koma Yahudiya.”
8 A hnukkâbangnaw ni Bawipa, atuvah Judahnaw ni talung hoi dêi hanelah, nang na tawng awh nahlangva vah, hote hmuen koe bout na cei han rah maw telah a pacei awh.
Sai suka ce, “Rabbi, ba da daɗewa ba ne Yahudawa suka nemi su jajjefe ka, duk da haka za ka koma can?”
9 Jisuh ni, khodai dawk suimilam hlaikahni touh ao nahoehmaw. Apihai kho a ang nah ka cet e ni talaivan angnae thung a cei dawkvah tâlaw mahoeh.
Yesu ya amsa ya ce, “Ba sa’a goma sha biyu ce yini guda ba? Mutumin da yake tafiya da rana ba zai yi tuntuɓe ba gama yana ganin hasken duniyan nan.
10 Hatei, khohmo cet awm pawiteh angnae ao hoe dawkvah a tâlaw thai, atipouh.
Sai a sa’ad da yake tafiya da dare ne zai yi tuntuɓe, don ba shi da haske.”
11 Hahoi Jisuh ni maimae hui Lazarus teh a i, hatei, pâhlaw hanlah ka cei han, atipouh.
Bayan ya faɗa haka, sai ya ƙara ce musu, “Abokinmu Lazarus ya yi barci, amma za ni in tashe shi.”
12 A hnukkâbangnaw ni, Bawipa ka ip e ngoun teh bout a dam han doeh, atipouh.
Almajiransa suka ce, “Ubangiji, in barci ne yake, to, ai, zai sami sauƙi.”
13 Jisuh ni Lazarus a due e hah a dei ngainae ei, a hnukkâbangnaw ni teh a mahmawk ka ip e doeh telah pouknae a ton awh.
Yesu kuwa yana magana mutuwarsa ce, amma almajiransa suka ɗauka yana nufin barcin gaskiya ne.
14 Hatdawkvah, Jisuh ni, Lazarus a due toe, telah a dei pouh.
Saboda haka sai ya gaya musu a fili cewa, “Lazarus ya mutu,
15 Hatei, na yuem awh nahanelah hote hmuen koe kai ka o hoeh e hah ka lunghawi. Bangtelah nakunghai ahni koe cet awh sei atipouh.
amma saboda ku na yi farin ciki da ba na can, domin ku gaskata. Amma mu dai je wurinsa.”
16 Samphei tie Thomas ni, a hnukkâbang huinaw hanlah, Bawipa hoi cungtalah due hanlah maimouh hai kâbang awh sei atipouh.
Sai Toma (wanda ake kira Didaimus) ya ce wa sauran almajiran, “Mu ma mu je, mu mutu tare da shi.”
17 Jisuh haw a pha nah Lazarus pakawp hoi hnin pali touh a pha toe tie a panue awh.
Da isowarsa, Yesu ya tarar Lazarus ya riga ya yi kwana huɗu a kabari.
18 Bethani kho teh Jerusalem kho hoi meng hni touh ahla.
Betani bai kai mil biyu ba daga Urushalima,
19 Martha hoi Meri e a thangroi a due dawkvah Judah taminaw ni tahungkhai hanlah a tho sin awh.
Yahudawa da yawa kuwa suka zo wurin Marta da Maryamu don su yi musu ta’aziyya, saboda rasuwar ɗan’uwansu.
20 Jisuh a tho e Martha ni a thai navah, Bawipa dawn hanelah a cei, hatei, Meri teh im vah ao.
Sa’ad da Marta ta ji cewa Yesu yana zuwa, sai ta fita don ta tarye shi, amma Maryamu ta zauna a gida.
21 Martha ni, Bawipa nang na awm pawiteh, ka thangroi dout mahoeh.
Sai Marta ta ce wa Yesu, “Ubangiji, da kana nan da ɗan’uwana bai mutu ba.
22 Hatei, atu kadout nakunghai, Bawipa nang ni Cathut koe ratoum e patetlah Cathut ni na poe han tie ka panue, atipouh.
Amma na san cewa ko yanzu ma Allah zai ba ka duk abin da ka roƙa.”
23 Jisuh nihai, na thangroi bout a thaw han, atipouh.
Yesu ya ce mata, “Ɗan’uwanki zai sāke tashi.”
24 Martha ni a hnukteng boutthawnae tueng toteh, ahni hai bout a thaw han tie ka panue atipouh.
Marta ta amsa ta ce, “Na sani zai sāke tashi a tashin matattu a rana ta ƙarshe.”
25 Jisuh ni, kai teh boutthawnae hoi hringnae doeh. Kai ka yuem pueng ni kadout nakunghai bout a hring han.
Yesu ya ce mata, “Ni ne tashin matattu da kuma rai. Duk wanda ya gaskata da ni zai rayu, ko ya mutu;
26 Ka hring ni teh Kai na kayuemnaw pueng nâtuek hai dout mahoeh. Kaie ka lawk na yuem maw telah a pacei navah, Martha ni oe ka yuem atipouh. (aiōn g165)
kuma duk wanda yake raye ya kuma gaskata da ni ba zai taɓa mutuwa ba. Kin gaskata wannan?” (aiōn g165)
27 Martha ni, oe Bawipa nang teh het talaivan ka kumcathuk hane Cathut Capa Khrih doeh tie ka yuem toe atipouh.
Sai ta ce masa, “I, Ubangiji, na gaskata kai ne Kiristi, Ɗan Allah, mai zuwa cikin duniya.”
28 Hahoi, Martha ni Meri koe a cei teh, Bawipa a tho, nang na kaw, telah duem a dei pouh.
Bayan ta faɗa haka kuwa, sai ta koma ta je ta kira’yar’uwarta Maryamu a gefe. Ta ce, “Ga Malam ya zo, kuma yana kiranki.”
29 Meri ni hote lawk a thai navah, karanglah a thaw teh Bawipa koe a cei.
Sa’ad da Maryamu ta ji haka sai ta yi wuf ta tafi wurinsa.
30 Jisuh teh kho thung kâen laipalah Martha ni a dawnnae koe doeh ao rah.
Yesu dai bai riga ya shiga ƙauyen ba tukuna, har yanzu yana inda Marta ta tarye shi.
31 Im dawk Meri hoi cungtalah ao navah, Meri lung ka pahawi e Judahnaw ni Meri karanglah a thaw teh a tâco e hah a hmu awh navah, khuika hanlah phuen koe vai a cei telah a pouk awh dawkvah, Meri hnuk a kâbang awh.
Da Yahudawan da suke tare da Maryamu a cikin gida, suke mata ta’aziyya, suka ga ta yi wuf ta fita, sai suka bi ta, suna tsammani za tă kabarin ne tă yi kuka a can.
32 Meri ni Jisuh aonae koe a pha teh Bawipa a hmu navah, a khok koe a tabo teh, Bawipa, nang na awm pawiteh kaie ka thangroi dout mahoeh ei atipouh.
Sa’ad da Maryamu ta kai inda Yesu yake, ta kuma gan shi, sai ta fāɗi a gabansa ta ce, “Ubangiji, da kana nan, da ɗan’uwana bai mutu ba.”
33 Meri hoi a hnukkâbang e Judahnaw khuika e Jisuh ni a hmu navah, Jisuh a lungmathoe teh,
Da Yesu ya ga tana kuka, Yahudawan da suka zo tare da ita ma suna kuka, sai ya yi juyayi ƙwarai a ruhu ya kuma damu.
34 Ahnimouh koe, na maw na pakawp awh, telah a pacei. Ahnimouh ni, Bawipa tho nateh khenhaw! atipouh.
Sai ya yi tambaya ya ce, “Ina kuka sa shi?” Suka amsa suka ce, “Ubangiji zo ka gani.”
35 Jisuh a ka.
Yesu ya yi kuka.
36 Judahnaw ni, khenhaw! Lazarus banghloimaw a lungpataw, ati awh.
Sai Yahudawa suka ce, “Dubi yadda yake ƙaunarsa!”
37 Tami bangpatet niteh, a mit ka dawn patenghai ka hmawt sak thai e ni, Lazarus a due hoeh nahanlah sak thai mahoeh ma aw, ati awh.
Amma waɗansunsu suka ce, “Anya, wanda ya buɗe wa makahon nan idanu, ba zai iya yin wani abu yă hana wannan mutum mutuwa ba?”
38 Jisuh teh lungreithai hoi tangkom koe a cei. Hote tangkom teh talung hoi a teng awh.
Yesu, har yanzu cike da juyayi, ya zo kabarin. Kogo ne da aka rufe bakin da dutse.
39 Jisuh ni talung paawng awh haw, atipouh. Martha ni, Bawipa pakawpnae hnin pali touh a pha toe, atuvah a hmui a tho han toe atipouh.
Sai Yesu ya ce, “Ku kawar da dutsen.” Marta,’yar’uwan mamacin ta ce, “Ubangiji, yanzu, ai, zai yi wari, don yau kwanansa huɗu ke nan a can.”
40 Jisuh ni hai na yuem pawiteh Cathut bawilennae na hmu han ka ti toung nahoehmaw.
Sai Yesu ya ce, “Ban gaya miki cewa in kin gaskata za ki ga ɗaukakar Allah ba?”
41 Hatdawkvah taminaw ni tangkom tengnae talung hah a takhoe awh. Hatnavah Jisuh ni kahlun lah a moung teh, Oe a Pa ka hei e hah na thai pouh toung dawkvah ka lunghawi.
Saboda haka suka kawar da dutsen. Sa’an nan Yesu ya dubi sama ya ce, “Uba, na gode maka da ka saurare ni.
42 Bawipa nang ni kaie ratoum lawk pou na thai pouh tie ka panue. Hatei, hete ka heinae teh na kaven e taminaw hanelah a tho teh, kai hah na patoun e doeh tie a yuem awh nahanelah doeh, telah atipouh.
Na san kullum kakan saurare ni, na dai faɗa haka ne saboda amfanin mutanen nan da suke tsaitsaye, don su gaskata cewa kai ka aiko ni.”
43 Hottelah a dei hnukkhu Lazarus tâcawt, telah puenghoi hram laihoi a kaw.
Sa’ad da ya faɗa haka, sai Yesu ya yi kira da babbar murya ya ce, “Lazarus, ka fito!”
44 Hatnavah, kadout tangcoung e teh a kut, a khok, a minhmai pueng hni hoi muen kâkayo laihoi a thaw teh a tâco. Jisuh ni ratham pouh awh, cetsak awh atipouh.
Sai mamacin ya fito, hannuwansa da ƙafafunsa a daure da ƙyallayen lilin, fuskarsa kuwa an naɗe da mayafi. Yesu ya ce musu, “Ku tuɓe kayan bizo, ku bar shi yă tafi.”
45 Hatdawkvah Meri koe ka tho e naw ni, Jisuh ni a sak e naw hah a hmu awh toteh, Bawipa hah a yuem awh.
Saboda haka Yahudawa da yawa da suka zo don su ziyarci Maryamu, suka kuma ga abin da Yesu ya yi, suka ba da gaskiya gare shi.
46 Hatei, tami tangawn ni Farasinaw koe a cei awh teh Jisuh ni a sak e hno a dei pouh awh.
Amma waɗansunsu suka je wurin Farisiyawa suka gaya musu abin da Yesu ya yi.
47 Hatnavah vaihma bawinaw hoi Farasinaw teh sanhedrin lawkceng bawinaw hoi a kamkhueng awh teh, Bangtelane ti awh han, ahni ni kângairunae moi a sak toe.
Sai manyan firistoci da Farisiyawa suka kira taron Majalisa. Suka yi tambaya suna cewa, “Me muke yi ne? Ga mutumin nan yana yin abubuwan banmamaki masu yawa.
48 Telah sut khen pawiteh tami pueng ni a yuem awh han toe. Rom taminaw ni tho awh vaiteh maimae hmuen, hoi miphun a pathup awh han toe ati awh.
In fa muka ƙyale shi ya ci gaba da haka, kowa zai gaskata da shi, Romawa kuma su zo su karɓe wurinmu su kuma ƙwace ƙasarmu.”
49 Hat nah e kum nah vaihma kacue ka tawk e Kaiaphas ni, nangmouh ni bang na panuek awh hoeh.
Sai waninsu, mai suna Kayifas, wanda ya kasance babban firist a shekarar ya ce, “Ku dai ba ku san kome ba!
50 Maimouh miphun abuemlah rawk awh hlak teh tami buet touh ni tami pueng e yueng lah a due e ahawihnawn tie na pouh awh hoeh bo vaw atipouh.
Ba ku gane ba, ai, gwamma mutum ɗaya yă mutu saboda mutane da duk ƙasar ta hallaka.”
51 Hottelah a dei e heh amae kâtawnnae lahoi a dei e laipalah hote kum dawk vaihma kacue lah ao e patetlah Jisuh ni Judah miphunnaw hanlah a due han ati tangcoung e doeh.
Bai faɗa haka bisa nufinsa ba, sai dai a matsayinsa na babban firist a shekarar, ya yi annabci ne cewa Yesu zai mutu saboda ƙasar Yahudawa,
52 Ahnimouh han dueng laipalah alouke kampek e lah kaawm e Cathut e canu capanaw a pâkhueng hanlah a due han tie ao toe.
ba don ƙasan nan kaɗai ba amma don yă tattaro’ya’yan Allah da suke warwatse ma, su zama ɗaya.
53 Hat hnin hoi teh Bawipa thei hanelah a kâcai awh toe.
Saboda haka, daga wannan rana suka ƙulla su ɗauke ransa.
54 Hatdawkvah, Jisuh ni Judahnaw aonae koe cet toung laipalah, haw hoi a tâco teh thingyei yawn hoi kahnai e, Ephraim kho lah a hnukkâbangnaw hoi a cei awh teh hawvah ao awh.
Saboda haka Yesu bai ƙara tafiya a cikin Yahudawa a sarari ba. A maimako haka sai ya janye zuwa yankin kusa da hamada, a wani ƙauye da ake kira Efraim, inda ya zauna da almajiransa.
55 Judahnaw e ceitakhai pawi a hnai dawkvah, taminaw mahoima thoungsak hanelah ceitakhai pawi hoehnahlan alouklouk lahoi Jerusalem lah a tho awh.
Sa’ad da lokaci ya yi kusa a yi Bikin Ƙetarewa na Yahudawa, da yawa suka haura daga ƙauyuka zuwa Urushalima, don su tsarkake kansu kafin Bikin Ƙetarewa.
56 Hotnaw ni, Jisuh a hmu awh hoeh dawkvah, bawkim teng vah, bangtelamaw na pouk awh, pawi koe ahni tho mahoeh maw ati awh teh a kâpacei awh.
Suka yi ta neman Yesu, da suke a tsaitsaye a filin haikali kuwa suka dinga tambayar juna, suna cewa, “Me kuka gani? Anya, zai zo Bikin kuwa?”
57 Hatnavah Farasinaw hoi vaihma bawinaw ni, Jisuh onae na panuek pawiteh man hanlah na dei awh han telah kâ a poe.
Manyan firistoci da Farisiyawa tuni sun riga sun yi umarni cewa duk wanda ya san inda Yesu yake, yă faɗa don su kama shi.

< Jawhan 11 >