< Jeremiah 38 >
1 Hahoi, Mattan capa Shephatiah, Pashhur capa Gedaliah, Shelemiah capa Jukal hoi Malkhijah capa Pashur tinaw ni, tami moikapap koe Jeremiah ni,
Shefatiya ɗan Mattan, Gedaliya ɗan Fashhur, Yukal ɗan Shelemiya da Fashhur ɗan Malkiya ya ji abin da Irmiya yana faɗa wa dukan mutane sa’ad da ya ce,
2 BAWIPA ni hettelah a dei, hete khopui dawk kaawm rae hah tahloi, takang hoi lacik hoi a due awh han. Hatei, Khaldean taminaw koe ka kâhmoun e tami teh a hring han. A hringnae teh ahnimouh koe poe e phu lah ao vaih a hring han.
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Duk wanda ya zauna a wannan birni zai mutu ta takobi, yunwa ko annoba, amma duk wanda ya je wurin Babiloniyawa zai rayu. Zai tsira da ransa, ya rayu.’
3 BAWIPA ni hettelah a dei, hete khopui heh Babilon siangpahrang ransanaw koe poe e lah ao vaiteh, a la awh han telah a dei awh e hah a thai awh.
Kuma ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Tabbatacce za a ba da wannan birni ga sojojin sarkin Babilon, wanda zai ci shi.’”
4 Hatdawkvah, kahrawikungnaw ni siangpahrang koevah pahren lahoi hete tami heh thei e lah awm naseh. Bangkongtetpawiteh, ahni ni ahnimouh koe hettelah lawk a dei teh, hete khopui thung e taran ka tuk hane naw hoi taminaw tha a youn sak. Hete tami ni taminaw hawi nahane tawng laipalah thoenae doeh a tawng telah ati awh.
Sai fadawa suka ce wa sarki, “Ya kamata a kashe wannan mutum. Yana karya zuciyar sojojin da suka ragu a birnin, da zuciyar sauran mutane, ta wurin abubuwan da yake faɗa musu. Wannan mutum ba ya neman jin daɗin zaman wannan sai dai wahala.”
5 Siangpahrang Zedekiah ni khenhaw! ahni teh nangmae kut dawk poe lah ao toe nahoehmaw. Bangkongtetpawiteh, siangpahrang ni na ngai awh hoeh e ouk sak thai boihoeh telah a ti.
“Yana a hannuwanku” Sarki Zedekiya ya amsa. “Sarki ba zai iya yin kome ya hana ku ba.”
6 Jeremiah a ceikhai awh teh, ramveng rapan thung kaawm e siangpahrang capa Malkhijah talai rahim tangkom dawk a tâkhawng awh. Jeremiah teh tangkom thung tangdong dawk a pabo awh teh, tangdong dawk ao.
Saboda haka suka kama Irmiya suka sa a rijiyar da ba ruwa a ciki ta Malkiya, ɗan sarki, wadda take a sansanin matsara. Suka saukar da Irmiya cikin rijiyar da ba ruwa da igiya; babu ruwa a cikinta, sai laka, Irmiya ya nutse cikin laka.
7 Ethiopia tami siangpahrang im ouk kaawm boi e, Ebedmelek ni Jeremiah talai thung tangkom dawk a ta tie hah a la thai. Hatnavah siangpahrang teh Benjamin longkha koe a la tahung.
Amma Ebed-Melek mutumin Kush, wani hafsa a fada, ya ji cewa sun sa Irmiya a rijiyar da ba ruwa. Yayinda sarki yana zama a Ƙofar Benyamin,
8 Ebedmelek teh siangpahrang im hoi a tâco teh, siangpahrang koevah,
Ebed-Melek ya fita daga fadar ya ce masa,
9 ka bawipa siangpahrang, hete taminaw ni profet Jeremiah talai thung tangkom dawk pabo e hah kalenpounge yonnae a sak awh e doeh. Vonhlam hoi a onae hmuen koe a due yawkaw han doeh, bangkongtetpawiteh, khopui thung vaiyei awm hoeh toe telah a ti.
“Ranka yă daɗe sarki, waɗannan mutane sun yi mugun abu a duk abin da suka yi wa Irmiya annabi. Sun jefa shi cikin rijiyar da ba ruwa, inda zai mutu da yunwa gama ba sauran wani burodi a birnin.”
10 Hahoi siangpahrang ni Ethiopia tami Ebedmelek hah kâ a poe teh hi hoi tami 30 touh hoi cet awh nateh, talai thung tangkom dawk a due hoehnahlan profet Jeremiah teh lat awh telah kâ a poe.
Sai sarki ya umarce Ebed-Melek mutumin Kush, “Ka ɗauko mutane talatin daga nan ku fid da Irmiya annabi daga rijiyar kafin ya mutu.”
11 Hottelah Ebedmelek ni tami a ceikhai teh, siangpahrang hnopai tanae im rahim a kâen teh angki karuem tâkhawng e hoi hnikapon hah a la teh, tangkom thung Jeremiah koe rui hoi a pabo pouh.
Saboda haka Ebed-Melek ya ɗauki mutane tare da shi suka shiga ɗaki a ƙarƙashin baitulmali a cikin fada. Ya ɗauko waɗansu tsofaffin tsummoki da tsofaffi riguna daga can ya kuma zurara su da igiya wa Irmiya a cikin rijiyar.
12 Ethiopia tami Ebedmelek ni Jeremiah koe hete angki ka pon hoi hnikapon naw heh na yakba rahim rui hoi pakhit atipouh e patetlah Jeremiah ni a sak.
Ebed-Melek mutumin Kush ya ce wa Irmiya, “Ka sa waɗannan tsummoki da tsofaffin rigunan a hammatarka, ya zarga igiya.” Irmiya ya yi haka,
13 Jeremiah teh talai thung tangkom dawk hoi rui hoi a rasa awh. Hottelah, Jeremiah teh ramvengnaw e rapan thung ka saw lah ao.
suka kuma ja shi sama da igiya suka fid da shi daga rijiyar. Irmiya kuwa ya zauna a sansanin matsara.
14 Hahoi siangpahrang Zedekiah ni Jeremiah hah a kaw teh, BAWIPA e im kâennae apâthum e dawk ahni teh a kâenkhai. Siangpahrang ni lawk na pacei han banghai pâphat hanh loe telah a ti.
Sai Sarki Zedekiya ya aika a kawo Irmiya annabi, ya sa aka kawo shi a ƙofa ta uku ta haikalin Ubangiji. Sai sarki ya ce wa Irmiya, “Zan tambaye ka wani abu, kada ka ɓoye mini wani abu.”
15 Jeremiah ni ka dei pawiteh, na thei payon han boma. Pouknae na poe nakunghai bout na ngai mahoeh telah atipouh.
Irmiya ya ce wa Zedekiya, “In na ba ka amsa, ba za ka kashe ni ba? Ko da na ba ka shawara, ba za ka saurare ni ba.”
16 Siangpahrang Zedekiah ni, BAWIPA ka hringnae kasakkung a hring e patetlah na thet mahoeh, nang na ka thet hane naw hai na poe mahoeh, telah arulahoi thoe a kâbo.
Amma Sarki Zedekiya ya yi wannan rantsuwa a kaɗaice ga Irmiya cewa, “Muddin Ubangiji yana a raye, wanda ya ba mu numfashi, ba zan kashe ka ko in ba da kai ga waɗanda suke neman ranka ba.”
17 Hat toteh, Jeremiah ni BAWIPA Isarel Cathut ransahu BAWIPA ni hettelah a dei, Babilon siangpahrang kahrawikungnaw koe na kâhmoun awh pawiteh, na hringnae a hlout han, hete khopui hai hmai kang mahoeh, nama hoi na imthungnaw hai na hring awh han.
Sa’an nan Irmiya ya ce wa Zedekiya, “Ga abin da Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘In ka miƙa wuya ga hafsoshin sarkin Babilon, za a bar ka da rai ba za a kuma ƙone wannan birni ba; da kai da iyalinka za ku rayu.
18 Hatei, Babilon siangpahrang kahrawikungnaw koe na kâhmoun awh hoehpawiteh, hete khopui heh Khaldean taminaw kut dawk poe lah ao han, hmaisawi awh vaiteh, ahnimae kut dawk hoi na hlout awh roeroe mahoeh telah atipouh.
Amma in ba ka miƙa wuya ga hafsoshin sarkin Babilon ba, za a ba da wannan birni ga Babiloniyawa za su kuma cinna mata wuta; kai kanka ba za ka tsira daga hannuwansu ba.’”
19 Siangpahrang Zedekiah ni Jeremiah koevah, Khaldean taminaw ka kâhmoun e Judah tami hah na man sak vaiteh, panuilai lah kaawm payon vaih tie ka lungpuen, atipouh.
Sarki Zedekiya ya ce wa Irmiya, “Ina jin tsoron Yahudawan da suka tafi wurin Babiloniyawa, gama Babiloniyawa mai yiwuwa su ba da ni gare su su kuma wulaƙanta ni.”
20 Hatei, Jeremiah ni na man sak mahoeh, nang koe ka dei e BAWIPA e lawk ma yuem. telah pawiteh nang hanlah ahawi han, hring hai bout na hring han.
Irmiya ya ce, “Ba za su ba da kai ba, ka yi biyayya ga Ubangiji ta wurin yin abin da na faɗa maka. Ta haka zai zama maka da amfani, za ka kuwa rayu.
21 Hatei, na kâhmoun hoehpawiteh, hethateh BAWIPA e lawk ni na hmusak e doeh.
Amma in ka ƙi miƙa wuya, ga abin da Ubangiji ya bayyana mini.
22 Khenhaw! Judah siangpahrang im dawk kaawm e napuinaw pueng Babilon siangpahrangnaw koevah, ceikhai lah ao vaiteh, hote napuinaw niyah, na hui kahawinaw ni na dum awh teh na tâ awh toe, na khok hah tangdong dawk a mang tahma vah koung na cei takhai awh han, telah ati awh han.
Za a fitar da dukan matan da suka ragu a fadan sarkin Yahuda wa hafsoshin sarkin Babilon. Waɗannan mata za su ce maka, “‘Sun ruɗe ka suka kuma rinjaye ka, waɗannan abokanka. Ƙafafunka sun nutse a cikin laka; abokanka sun yashe ka.’
23 Na yu na canaw hah Khaldean taminaw koe a ceikhai awh vaiteh, a kut dawk hoi na tâcawtkhai mahoeh toe. Babilon siangpahrang kut dawk man e lah na o vaiteh, nang kecu dawk hete khopui hmaisawi awh han telah atipouh.
“Za a kawo dukan matanka da’ya’yanka wa Babiloniyawa. Kai kanka ba za ka tsira daga hannuwansu ba amma za su sa sarkin Babilon zai kama ka; za a kuma ƙone wannan birni.”
24 Zedekiah ni Jeremiah koevah, hete lawk apinihai thai hanh naseh, telah pawiteh na dout mahoeh telah atipouh.
Sai Zedekiya ya ce wa Irmiya, “Kada ka bar wani ya san wannan zance, in ba haka ba za ka mutu.
25 Hatei, kahrawikungnaw ni a kâpato roi e hah a thai awh. Nang koe a tho awh teh, siangpahrang na dei e hoi siangpahrang ni nang koe a dei e hai na dei pouh haw, kaimouh koe banghai pâphat hanh, na thet awh mahoeh, telah tet awh pawiteh,
In fadawa suka ji cewa na yi magana da kai, suka kuma zo wurinka suka ce, ‘Faɗa mana abin da ka faɗa wa sarki da kuma abin da sarki ya faɗa maka; kada ka ɓoye mana, in ba haka za mu kashe ka,’
26 Ahnimouh koevah Jonathan im lah na ban sak nateh, hawvah ka due hoeh nahane lah doeh siangpahrang koe ka kâhei, telah na ti pouh han telah atipouh.
sai ka ce musu cewa, ‘Na roƙi sarki kada yă mai da ni gidan Yonatan in mutu a can.’”
27 Hahoi, Jeremiah koe a tho awh toteh kahrawikungnaw ni a pacei awh. Siangpahrang ni kâ a poe e patetlah a dei pouh. Hat toteh, bout pacei awh hoeh toe. Bangkongtetpawiteh, pouknae hah panuek awh hoeh.
Dukan fadawa kuwa suka zo wurin Irmiya suka tambaye shi, ya kuma faɗa musu dukan abin da sarki ya umarce shi ya faɗa. Saboda haka ba su ƙara ce masa kome ba, gama ba wanda ya ji zance da suka yi da sarki.
28 Hottelah Jerusalem a tuk awh teh a lanae hnin totouh, Jeremiah teh thongim rapan thung ao rah. Hahoi Jerusalem teh a la awh.
Irmiya kuwa ya zauna a sansanin masu gadi har ranar da aka ci Urushalima da yaƙi. Ga yadda aka ci Urushalima,