< Kamtawngnae 31 >
1 Laban e canaw ni, Jakop ni kaimae apa e hno pueng koung a la pouh dawkvah, hete tawnta e naw pueng heh a hmu e doeh, telah a dei awh e lawk hah Jakop ni a thai.
Yaƙub ya ji cewa’ya’ya Laban mazan suna cewa, “Yaƙub ya kwashe dukan abin da mahaifinmu yake da shi, ya kuma sami dukan wannan arziki daga abin da yake na mahaifinmu.”
2 Jakop ni, Laban e minhmai a khet nah a hmoun e patetlah minhmai kahawi ka hmawt hoeh toe tie hah a panue.
Yaƙub kuma ya lura cewa halin Laban gare shi ya canja ba kamar yadda yake a dā ba.
3 Hatdawkvah, BAWIPA ni Jakop koevah, na mintoenaw e ram hoi na imthungkhu lah ban nateh, nang koe vah ka o han, telah ati.
Sai Ubangiji ya ce wa Yaƙub, “Koma ƙasar kakanninka da kuma danginka, zan kuwa kasance tare da kai.”
4 Jakop ni tami a patoun teh Rachel hoi Leah hah saring onae law vah tho hanelah a kaw sak.
Saboda haka Yaƙub ya aika a ce wa Rahila da Liyatu su zo jeji inda garkunan suke.
5 Ahnimouh roi koe, na pa e minhmai ka hmu navah, ahmoun e patetlah minhmai kahawi ka hmawt hoeh toe tie hah ka panue, hateiteh Apa Cathut teh kai koe ao toe.
Sai ya ce musu, “Na ga cewa halin mahaifinku gare ni ba kamar yadda dā yake ba, amma Allah na mahaifina yana tare da ni.
6 Ka thayung abuemlahoi na pa e thaw ka tawk e hah na panue awh.
Kun san cewa na yi aiki wa mahaifinku da dukan ƙarfina,
7 Hot nahlangva na pa ni na dum teh, ka hmu hane aphu hah vai hra touh na dum toe. Hatei patawnae na poe hane teh Cathut ni na pasoung hoeh.
duk da haka mahaifinku ya cuce ni ta wurin sauya albashina sau goma. Amma dai, Allah bai yardar masa yă yi mini lahani ba.
8 Tarakcak e pueng hah aphu lah ao han telah a dei teh saring pueng ni tarakcak lah koung a khe. Taracak hoi kâkalawt lah a khe e pueng aphu lah ao han ati ei nakunghai, saring pueng ni tarakcak lah koung a khe.
In ya ce, ‘Dabbare-dabbare ne za su zama ladanka,’ sai dukan garkunan su haifi dabbare-dabbare, in kuma ya ce, ‘Masu zāne-zāne ne za su zama ladanka,’ sai dukan garkunan su haifi ƙananan masu zāne-zāne.
9 Hottelah, Cathut ni na pa e saringhu hah a la pouh teh kai na poe e doeh.
Ta haka Allah ya kwashe dabbobin mahaifinku ya ba ni.
10 Hahoi hettelah ao. Saring âvâ yawng hane a kamtawng nah ka mang lah ka khet teh, khenhaw! âvâ ka cawt e a tan hah a em lah kaawm e hoi a em tarakcak e hoi, a em dakdak kaawm e naw hah ka hmu.
“A lokacin ɗaukar cikin garken, na taɓa yin mafarki inda na ga bunsuran da suke barbara da garken, masu dabbare-dabbare, ko babare-babare, ko masu zāne-zāne ne.
11 Ka mang lah Cathut e kalvantami ni, Jakop ati teh kai ni, hi vah ka i doeh, ka ti pouh.
Sai mala’ikan Allah ya ce mini a mafarkin, ‘Yaƙub.’ Sai na amsa na ce, ‘Ga ni.’
12 Ahni ni, moung na teh, khenhaw! a tan ni âvâ a yawng e pueng hah a em kaawm hoi a em tarakcak e hoi a em dakdak kaawm naw seng doeh. Bangkongtetpawiteh, Laban ni nang dawk a sak e naw pueng hah be ka panue.
Ya ce, ‘Ɗaga idanunka ka gani, dukan bunsuran da suke hawan garken, masu dabbare-dabbare, ko babare-babare, ko masu zāne-zāne ne, gama na ga dukan abin da Laban yake yin maka.
13 Kai teh talung na ungnae dawk satui na awinae, kai koe lawkkam na saknae Bethel, hote Bethel Cathut lah ka o. Atu thaw nateh hete ram heh tâcawt takhai, na khenae ram koe lah ban leih, telah ati.
Ni ne Allah na Betel, inda ka zuba wa al’amudi mai, da kuma inda ka yi mini alkawari. Yanzu ka bar wannan ƙasa nan take, ka koma ƙasarka ta ainihi.’”
14 Rachel hoi Leah ni a pathung roi teh, apa im e maimouh hanelah ham hane hoi râw ao rah maw.
Sai Rahila da Liyatu suka amsa suka ce, “Muna da wani rabo a gādon kayan mahaifinmu ne?
15 Ahni ni imyin patetlah na pouk awh toung nahoehmaw. Bangkongtetpawiteh, na yo awh teh maimae tangka hai be a ca awh toe.
Ba kamar baƙi ne yake ɗaukarmu ba? Ba sayar da mu kaɗai ya yi ba, har ma ya yi amfani da abin da aka biya saboda mu.
16 Bangkongtetpawiteh, Cathut ni maimae na pa koehoi a la e naw pueng teh, maimae canaw hane doeh. Hottelah Cathut ni nang koe a dei e pueng teh sak yawkaw, telah atipouh.
Tabbatacce dukan dukiyar da Allah ya kwashe daga mahaifinmu ya zama namu da’ya’yanmu. Saboda haka ka yi duk abin da Allah ya faɗa maka.”
17 Jakop hah a thaw teh, a capanaw hoi a yu roi hah kalauk dawk a kâcui sak.
Sa’an nan Yaƙub ya sa’ya’yansa da matansa a kan raƙuma,
18 Kanaan ram a na pa Isak koe cei hanelah a saringnaw hoi hnopai a pâtung e a hmu e saringnaw pueng, Paddanaram ram e a tawn e naw pueng be a sin awh.
ya kuma kora dukan dabbobinsa, suka ja gabansa, tare da dukan abubuwan da ya samu a Faddan Aram, don su tafi wurin mahaifinsa Ishaku a ƙasar Kan’ana.
19 Laban teh amae tu muen ngaw hanelah a cei teh Rachel ni a cei teh a na pa e Terah meikaphawk hah yout a la pouh.
Sa’ad da Laban ya tafi don askin tumakinsa, sai Rahila ta sace gumakan gidan mahaifinta.
20 Jakop teh Siria tami Laban panuek laipalah, arulahoi a cei. A cei hane hah dei pouh hoeh.
Yaƙub kuwa ya ruɗe Laban mutumin Aram da bai sanar da shi zai gudu ba.
21 Hottelah a tawn e naw pueng hoi a yawng. A thaw teh palang a raka teh Gilead mon lah pâtam lahoi a cei.
Saboda haka ya gudu da dukan abin da ya mallaka, ya ƙetare Kogi, ya nufi yankin tuddan Gileyad.
22 Jakop a yawng tie hah apâthum hnin vah Laban koe a dei pouh awh.
A rana ta uku, sai aka faɗa wa Laban cewa Yaƙub ya gudu.
23 A hmaunawnghanaw a hrawi teh, hnin sari touh thung a pâlei teh Gilead mon dawk rek a pha awh.
Sai Laban ya ɗauki danginsa tare da shi, ya bi bayan Yaƙub har kwana bakwai, ya kuma same shi a yankin tuddan Gileyad.
24 Hateiteh, Siria tami Laban koe karum a mang lahoi Cathut a tho teh, Jakop koe a thoe hoi hawi banghai na dei hoeh nahanelah kâhruetcuet, telah atipouh.
Sai Allah ya bayyana ga Laban mutumin Aram a mafarki da dare, ya ce masa, “Ka yi hankali kada ka faɗa wa Yaƙub wani abu, ko mai kyau ko marar kyau.”
25 Hottelah Laban ni Jakop hah rek a pha. Jakop ni rim hah mon dawk a yap teh, Laban hoi a hmaunawnghanaw ni Gilead mon dawk ahnimae rim hah a yap awh van.
Yaƙub ya riga ya kafa tentinsa a yankin tuddan Gileyad sa’ad da Laban ya same shi. Laban da danginsa suka kafa sansani a can su ma.
26 Laban ni Jakop koe, na sak e hno heh bangmaw. Ka thai laipalah dung na cei awh teh, tarantuknae koe man e patetlah ka canunaw na yawngkhai.
Sai Laban ya ce wa Yaƙub, “Me ke nan ka yi? Ka ruɗe ni, ka kuma ɗauki’ya’yana mata kamar kamammun yaƙi.
27 Bang kecu dawk maw, arulahoi tapueng hoi ratoung hoi na thak thai nahanlah dei laipalah na o.
Me ya sa ka gudu a ɓoye ka kuma ruɗe ni? Me ya sa ba ka faɗa mini don in sallame ka da farin ciki da waƙoƙi haɗe da kiɗin ganguna da garayu ba?
28 Ka capanaw hoi ka canunaw ka paco han na pasoung hoeh. Hottelae pathunae hno hah na sak.
Ba ka ma bari in sumbaci jikokina da’ya’yana mata in yi musu bankwana ba. Ka yi wauta.
29 Kai ni koung na raphoe thai han ei teh, na pa Cathut ni karum ka mang lah, Jakop koe a thoe hoi hawi banghai na dei hoeh nahanelah kâhruetcuet, telah na dei pouh.
Ina da iko in cuce ka; amma jiya da dare Allahn mahaifinka ya faɗa mini, ‘Ka yi hankali kada ka faɗa wa Yaƙub wani abu ko mai kyau ko marar kyau.’
30 Na pa im na rabui poung kecu dawkvah, na ka cet e katang lah na o. Hatei bang kecu dawk maw ka cathutnaw na paru pouh awh, telah ati.
Yanzu ka gudu domin kana marmari komawa gidan mahaifinka. Amma don me ka sace mini gumakana?”
31 Jakop ni a pathung teh Laban koe, na canunaw heh thama lah na lawm vai tie hah ka puen dawk doeh.
Yaƙub ya amsa wa Laban, “Na ji tsoro ne, domin na yi tsammani za ka ƙwace’ya’yanka mata daga gare ni ƙarfi da yaji.
32 Namae cathut ka lat e teh hring sak hanh. Ka hmaunawnghanaw mithmu vah na cathut kai koe kaawm e teh kahawicalah khen nateh, lat yawkaw, telah ati. Bangkongtetpawiteh, Rachel ni a paru e hah Jakop ni la panuek hoeh.
Amma in ka sami wani wanda yake da gumakanka, ba zai rayu ba. Kai da kanka ka duba a gaban danginmu, ko akwai wani abin da yake naka a nan tare da ni; in ka gani, ka ɗauka.” Yaƙub dai bai san cewa Rahila ta sace gumakan ba.
33 Laban teh Jakop e rim hoi Leah e rim hoi a sannu kahni touh roi e rim koe a tawng teh, hmawt hoeh. Hahoi, Leah e rim hoi a tâco teh Rachel e rim dawk a kâen.
Saboda haka Laban ya shiga tentin Yaƙub, ya shiga tentin Liyatu da kuma tentuna matan nan biyu bayi, amma bai sami kome ba. Bayan ya fita daga tentin Liyatu, sai ya shiga tentin Rahila.
34 Rachel ni meikaphawk hah a la teh kalauk ni phunae hno thung vah a hro. Laban ni rim thung naw pueng hah pheng a pâphue eiteh hmawt hoeh.
Rahila fa ta kwashe gumakan gidan ta sa su cikin sirdin raƙumi, ta kuma zauna a kansu. Laban ya bincika cikin kowane abu a tentin amma bai sami kome ba.
35 Rachel ni a na pa koe, na hmalah ka thaw ngai tho hoeh. Ka bawipa, na lungkhuek sak hanh, ka kampheng lahun lah ao dawk doeh, telah ati. Pheng a pâphue eiteh meikaphawk hah hmawt thai awh hoeh.
Sai Rahila ta ce wa mahaifinta, “Kada ka yi fushi, ranka yă daɗe da ban tashi tsaye a gabanka ba; gama ina al’adar mata ne.” Saboda haka ya bincika amma bai sami gumakan gidan ba.
36 Jakop teh a lungkhuek teh, Laban hah a yue. Jakop ni Laban koe, bang e phung maw ka ek, bangmaw ka yonnae ao teh, na lungkhuek laihoi na pâlei.
Yaƙub ya fusata, ya kuma yi wa Laban faɗa. Ya tambayi Laban, “Mene ne laifina? Wanda zunubi na yi da kake farautata?
37 Ka hnopainaw pueng be na pâphue teh, namae hnopai bangmaw na hmu. Maimouh roi teh lawkkâceng thai nahan ka hmaunawnghanaw hoi nange hmaunawnghanaw e hmalah tat.
Yanzu da ka bincika dukan kayayyakina, me ka samu da yake na gidanka? Kawo shi nan a gaban danginka da kuma dangina, bari su zama alƙali tsakaninmu biyu.
38 Kum 20 totouh nang koe ka o teh, na tu hoi na hmaenaw ni ca khe laipalah awm boihoeh. Na tuhu thung e a tan hai ka cat boihoeh.
“Na kasance tare da kai shekaru ashirin. Tumakinka da awakinka ba su yi ɓarin ciki ba, ban kuwa ci raguna daga garkunanka ba.
39 Moimatheng ni a kei e hai nang koe ka phatkhai boihoeh. Kai ni paleipalang kahmat e yueng lah ouk ka rawng. Kanîthun lah a paru e naw karum lah a paru e naw hai na patho sak.
Ban kawo dabbobinka da namun jeji suka yayyaga; na kuma ɗauki hasarar ba? Ka nemi in biya dukan abin da aka sace da rana ko da dare.
40 Hettelah ouk ka o. Kanîthun khumbei um hai, karum a pâding nahai, rucat um hai, ka tawk. Ihmu boum lah ka ip boihoeh.
Yanayin da na kasance ke nan, da rana na sha zafin rana da dare kuma na sha sanyi, ga rashin barci.
41 Hottelah kum 20 touh thung na im vah ka o teh, na canu roi ka hni touh kutphu e dawk kum 14, na thaw ka tawk. Na saring kutphu dawk kum 6 ka tawk teh, kutphu hah vai hra totouh bout na dum.
Haka ya kasance shekaru ashirin da na yi a gidanka. Na yi maka aiki shekaru goma sha huɗu domin’ya’yanka mata biyu, na kuma yi shekaru shida domin garkunanka, ka kuma canja albashina sau goma.
42 Apa Cathut, Abraham Cathut, Isak Cathut ni a taki e hah kai koe awm hoehpawiteh, atu patenghai tak caici lah ban sak han na noe. Cathut ni karucatnae hoi ka patangnae hah a panue, paduem vah na yue toe, telah ati.
Da ba don Allah na mahaifina, Allah na Ibrahim da kuma Tsoron Ishaku ya kasance tare da ni ba, tabbatacce da ka sallame ni hannu wofi. Amma Allah ya ga wahalata da famar hannuwana, ya kuwa tsawata maka da dare jiya.”
43 Laban ni a pathung teh, Jakop koe, napuinaw heh kaie canunaw doeh. Tongpanaw hai kaie capanaw doeh. Saringnaw hai kaie saringnaw doeh. Na tawn e naw pueng heh kaie seng doeh. Hateiteh, sahnin vah hete ka canunaw hoi a canaw e a lathueng vah bangmaw ka sak thai han.
Laban ya amsa wa Yaƙub, “Matan,’ya’yana ne,’ya’yansu,’ya’yana ne, garkunan kuma garkunana ne. Dukan abin da kake gani, nawa ne. Duk da haka me zan yi a rana ta yau ga waɗannan’ya’yana mata, ko kuma ga’ya’yan da suka haifa?
44 Hatdawkvah, nang hoi kai lawkkamnae sak roi sei. Hothateh, nang hoi kai rahak dawk kapanuekkhaikung lah awm seh, telah ati.
Zo, bari mu ƙulla yarjejjeniya, da kai da ni, bari kuma ta kasance shaida a tsakaninmu.”
45 Hottelah, Jakop ni talung a la teh talung hah a ung.
Saboda haka Yaƙub ya ɗauki dutse ya kafa yă zama al’amudi.
46 Telah Jakop ni a hmaunawnghanaw koevah, talung pung awh haw, telah ati. Talung hah a la awh teh, a pung awh. Hot van vah bu a ca awh.
Ya ce wa danginsa. “Ku tattara waɗansu duwatsu.” Sai suka kwashe duwatsu suka tsiba, suka kuwa ci abinci a can kusa da tsibin.
47 Laban ni talung pung e hah Jegarsahdutha telah a phung. Hateiteh Jakop ni Galeed telah ati.
Laban ya sa masa suna Yegar Sahaduta, Yaƙub kuwa ya kira shi Galeyed.
48 Laban ni hete pung e talung heh sahnin vah, kai hoi nang rahak vah, lawk kapanuekkhaikung lah ao telah ati. Hatdawkvah a min lah Galeed telah ati e lah ao.
Laban ya ce, “Wannan tsibi, shi ne shaida tsakaninka da ni a yau.” Shi ya sa aka kira shi Galeyed.
49 Mizpah telah hai ati awh. Bangkongtetpawiteh, Laban ni kamphei awh hnukkhu hoi BAWIPA ni maimanaw na ring lawiseh.
Aka kuma kira shi Mizfa, domin ya ce, “Ubangiji yă sa ido tsakanin ni da kai sa’ad da muka rabu da juna.
50 Ka canunaw heh roedeng na poe teh, yu alouke na tawn pawiteh, apihai maimouh koe awm hoeh eiteh, khenhaw! Cathut teh nang hoi kai rahak vah, kapanuekkhaikung lah ao, telah ati.
Laban ya ce in ka wulaƙanta’ya’yana mata, ko ka auri waɗansu mata ban da’ya’yana mata, ko da yake babu wani da yake tare da mu, ka tuna cewa Allah shi ne shaida tsakaninka da ni.”
51 Laban ni Jakop koe hete talung ung e hoi hete talung pung e heh kai hoi nang rahak vah ka ta e lah ao.
Laban ya kuma ce wa Yaƙub, “Ga wannan tsibi, ga kuma wannan al’amudin da na kafa tsakaninka da ni.
52 Patawnae poe hanelah kai ni hete talung pung e hoi talung ung e hloilah ka tho mahoeh, tie hoi nang ni hai hete talung pung e hoi talung ung e hloilah tapuet hoi na tho mahoeh, telah hete talung pung e hah kapanuekkhaikung lah awm nateh, hete talung ung e hai kapanuekkhaikung lah awm naseh.
Wannan tsibin shi ne shaida, wannan al’amudi kuma shaida ne, cewa ba zan tsallake wannan tsibi zuwa gefenka don in cuce ka ba, kai kuma ba za ka tsallake wannan tsibi da al’amudi zuwa gefena don ka cuce ni ba.
53 Abraham Cathut, Nahor Cathut, a na pa Cathut ni maimae rahak lawkceng naseh, telah ati. Hahoi Jakop ni a na pa Isak ni taki e noe lahoi thoe a bo.
Bari Allah na Ibrahim da Allah na Nahor, Allah na iyayensu, yă zama alƙali tsakaninmu.” Saboda haka Yaƙub ya yi rantsuwa da sunan Tsoron mahaifinsa Ishaku.
54 Jakop ni mon dawkvah, thuengnae a sak teh a hmaunawnghanaw hah vaiyei ca hanelah a kaw teh, vaiyei hah a ca awh. Mon dawkvah a roe awh.
Ya miƙa hadaya a can a ƙasar tudu, ya kuma gayyaci danginsa zuwa wurin cin abinci. Bayan suka ci, sai suka kwana a can.
55 Laban teh amom vah a thaw teh, a capanaw hoi a canunaw hah a paco teh yawhawi a poe hnukkhu Laban teh a ma onae koe lah a ban.
Da sassafe kashegari sai Laban ya sumbaci jikokinsa da’ya’yansa mata, ya sa musu albarka. Sa’an nan ya yi bankwana da su, ya koma gida.