< Ezra 10 >

1 Hahoi Cathut im koelah kangvawi teh, tabo teh, ka laihoi Ezra ni yon ngaithoumnae a kâhei. Hatnavah Isarelnaw tamihupui napui, tongpa, camonaw ahni koe a kâracut awh teh, tamihupui teh puenghoi a khuika awh.
Yayinda Ezra yake addu’a, yake kuma furta laifi, yana kuka, yana a durƙushe da kansa ƙasa a gaban gidan Allah, sai babban taron jama’ar Isra’ilawa, maza, mata da yara, suka taru a wurinsa. Su ma suka yi kuka mai zafi.
2 Elam catoun thung hoi Jehiel capa Shekaniah ni Ezra koevah, maimouh Cathut koevah yon sak awh tangngak toe, hahoi hete ram dawk e miphun alouke canunaw hah yu lah paluen awh toe. Hatei Isarelnaw hanelah ngaihawinae ao rah doeh.
Sai Shekaniya ɗan Yehiyel, daga zuriyar Elam ya ce wa Ezra, “Mun yi wa Allah rashin aminci ta wurin yin auratayya da maƙwabtanmu, amma duk da haka bai yashe mutanen Isra’ila ba.
3 Hatdawkvah, bawipa ni pouknae na poe e patetlah Cathut e kâpoelawk ka bari e tami ni, yucanaw ceitakhai vaiteh maimae Cathut koe lawkkamnae sak awh vaiteh kâlawk patetlah tarawi awh sei.
Yanzu bari mu yi alkawari da Allahnmu, mu kori matan da yaransu bisa ga abin da ranka yă daɗe da sauran shugabannin da kuke girmama umarnin Allah kuka shawarce mu, bari mu yi haka bisa ga doka.
4 Thaw leih, bangkongtetpawiteh, hete heh nange thaw doeh, kaimouh hai nang koe lah doeh kampang awh. Lung kacakcalah awm nateh, tawk leih, telah ati awh.
Sai ka tashi, gama wannan hakkinka ne, za mu ba ka goyon baya. Saboda haka ka yi ƙarfin hali ka aikata shi.”
5 Hahoi, Ezra a thaw teh, vaihma bawinaw, Levih miphunnaw hoi Isarel taminaw abuemlah, hote lawk patetlah lawkkamnae a sak sak teh, Hot patetlah lawkkamnae a sak awh.
Sai Ezra ya tashi ya sa firistoci da suke shugabanni, da Lawiyawa, da dukan mutanen Isra’ila su rantse, cewa za su yi abin da aka ce. Sai suka yi rantsuwar.
6 Hahoi, Ezra ni Cathut e im dawk hoi a thaw teh, Eliashib capa Jehohanan e imthung a kâen teh, hawvah rawca hai cat hoeh, tui hai net laipalah ao. Bangkongtetpawiteh, san dawk hoi ka hlout e taminaw yonnae kecu dawk khuika laihoi ao.
Sa’an nan Ezra ya tashi daga gidan Allah ya tafi gidan Yehohanan ɗan Eliyashib, a can ma bai ci wani abu ba, bai sha ruwa ba domin ya ci gaba da yin baƙin cikin rashin aminci na waɗanda suka dawo daga bauta.
7 San dawk hoi ka hlout e taminaw pueng Jerusalem vah kamkhueng hanelah,
Aka yi shela a duk fāɗin Yahuda da Urushalima cewa dukan waɗanda suka dawo daga bauta su tattaru a Urushalima.
8 Kahrawikungnaw hoi kacuenaw ni a dei e patetlah hnin 3 touh thung ka tho hoeh e tami teh, san hloutnae dawk hoi pâlei vaiteh, a tawnta e hnopai pueng lawp vaiteh, ama hai pâlei lah ao han telah, Jerusalem hoi kamtawng teh Judah ram totouh a pathang awh.
Duk wanda bai zo a cikin kwana uku ba, za a washe shi, a kuma ware shi daga jama’ar da suka dawo daga bauta. Haka shugabanni da dattawa suka zartar.
9 Hot patetvanlah Judahnaw hoi Benjamin miphun tongpanaw teh hnin 3 touh thung Jerusalem vah a kamkhueng awh. Thapa yung 9, hnin 21 nah kho puenghoi a rak dawkvah, taminaw teh Cathut e im hmalah sut a tahung awh teh a pâyaw awh.
A cikin kwana uku duk mutanen Yahuda da na Benyamin suka taru a Urushalima. A ranar ashirin ga watan tara, dukan mutanen suka zauna a dandali a gaban gidan Allah cike da ɓacin rai saboda abin da ya faru da kuma ruwan da aka yi.
10 Hatnavah, vaihma Ezra ni a thaw teh ahnimouh koevah yonnae na sak awh toe, Isarel miphun dawk yonnae a len nahanelah miphun alouke napuinaw hoi na kâpaluen awh.
Sai Ezra firist ya miƙe tsaye ya yi musu magana ya ce, “Kun yi rashin aminci; kun aure mata baƙi, ta haka kuka ƙara kan zunubin Isra’ila.
11 Hatdawkvah, mintoenaw e BAWIPA Cathut koe yon ngaithoum het awh, a ngainae hah sak awh nateh, hete ram dawk e miphun alouke e na yunaw hoi kâkapek awh, telah ati.
Yanzu sai ku furta zunubanku ga Ubangiji, Allahn kakanninku, ku kuma yi nufinsa. Ku raba kanku da mutanen da suke kewaye da ku, ku kuma rabu da baƙin mata.”
12 Hahoi, taminaw ni puenghoi kacailah a dei awh e teh, bokheiyah na dei e patetlah ka sak awh roeroe han.
Mutanen kuwa suka tā da murya da ƙarfi suka ce, “Gaskiya ka faɗa, dole mu yi yadda ka ce,
13 Hateiteh, tami moipap awh teh khoraknae tueng lahai bout ao, alawilah kaimouh pou kangdout thai mahoeh, hahoi hnin hnin touh hoi sak hane lahai tho hoeh, bangkongtetpawiteh, hete hno dawk tami moikapap ni yonnae sak awh toe.
Amma akwai mutane da yawa, kuma lokacin damina ne; saboda haka ba za mu iya tsayawa a waje ba. Ban da haka ma, aikin nan ba na kwana ɗaya ko biyu ba ne, domin ba ƙaramin laifi muka yi ba.
14 Tamimaya e yueng lah kahrawikungnaw ni mah na pouk pouh lawiseh. Kaimae lathueng vah kalenpounge BAWIPA lungkhueknae a roum nahanelah mae kho dawk Jentelnaw yu lah paluen e khonaw dawk e kahrawikungnaw hoi lawkcengkungnaw ni a tueng khoe e dawk rip tho awh naseh telah, ati awh.
Bari shugabanninmu su yi wani abu a madadin mutane duka, sa’an nan sai duk wanda ya san ya auri baƙuwar mace a garuruwanmu, sai yă zo nan a lokacin da aka shirya tare da dattawa da alƙalan kowane gari, har sai Allah ya huce fushinsa mai zafi da yake kanmu.”
15 Asahel capa Jonathan hoi Tikvah capa Jahaziah ni hnâ bawt roi hoeh, hatei Levih miphun Meshullam hoi Shabbethai ni teh hnâ a bo roi.
Yonatan ɗan Asahel, da Yazehiya ɗan Tikba su ne kaɗai ba su yarda da wannan shirin ba, sai Meshullam da Shabbetai Balawe kuma suka goyi bayansu.
16 Hahoi san dawk hoi kahloutnaw ni hottelah a sak awh. Vaihma Ezra ni imthung kahrawikungnaw thung hoi minnaw a la e patetlah thapa ayung 10 nae, apasuek hnin navah hote kong kâdei hanelah a kamkhueng awh.
Sai waɗanda suka dawo daga bauta suka yi yadda aka zartar. Ezra firist ya zaɓi mutane waɗanda su ne shugabannin iyalai, ɗaya daga kowane sashe, aka rubuta sunan kowannensu. A ranar ɗaya ga watan goma kuwa suka zauna don su yi binciken waɗannan abubuwa.
17 Hahoi Thapa yung pasuek, apasuek hnin nah, miphun alouke yu lah ka lat e kong kâdei e teh a cum awh.
A rana ta farko ga watan farko, suka gama da bincike duk waɗanda suka auri baƙin mata.
18 Hahoi, vaihma capanaw thung dawk hoi miphun alouke yu lah ka lat e taminaw teh, Jeshua hoi a hmaunawngha thung e Jozadak capa hoi a hmaunawngha Maaseiah, Eliezer, Jarib hoi Gedaliah tinaw doeh.
A cikin zuriyar firistoci, ga waɗanda suka auri mata baƙi. Daga zuriyar Yeshuwa ɗan Yozadak da’yan’uwansa, akwai Ma’asehiya, da Eliyezer, da Yarib, da Gedaliya.
19 Ahnimanaw ni a yunaw kapek hanelah lawk a kam awh. Yon pâphonae dawk ngaithoum lah o nahanelah, tutan buet touh hoi thuengnae a sak awh.
(Su ne suka miƙa hannuwansu suka nuna sun yarda su kori matansu baƙi, kowannensu kuma ya ba da rago daga cikin garkensa don a miƙa hadaya don zunubi.)
20 Immer catoun thung hoi Hanani hoi Zebadiah.
Daga zuriyar Immer, akwai Hanani da Zebadiya.
21 Harim catoun thung hoi Maaseiah, Elijah, Shemaiah, Jehiel hoi Uzziah.
Daga zuriyar Harim, akwai Ma’asehiya, Iliya, Shemahiya, Yehiyel da Uzziya.
22 Pashhur catoun thung hoi Elioenai, Maaseiah, Ishmael, Nethanel, Jozabad hoi Eleasah tinaw doeh.
Daga zuriyar Fashhur, akwai Eliyohenai, Ma’asehiya, Ishmayel, Netanel, Yozabad da Eleyasa.
23 Levih miphunnaw thung hoi Jozabad, Shimei, Kalaiah, Pethahiah, Judah hoi Eliezer tinaw doeh.
Cikin Lawiyawa, akwai Yozabad, Shimeyi, Kelaya (wato, Kelita), Fetahahiya, Yahuda, Eliyezer.
24 La kasaknaw thung hoi Eliashib, longkha karingkungnaw thung hoi Telem hoi Uri tinaw doeh.
Daga mawaƙa, akwai Eliyashib. Daga masu tsaron ƙofofin haikali, akwai Shallum, Telem da Uri.
25 Isarelnaw thung hoi Parosh capa thung hoi Ramiah, Jeriah, Malkhijah hoi Benaiah.
Ga sunayen sauran mutanen Isra’ilan da suke da wannan laifi. Daga zuriyar Farosh, akwai Ramiya, da Izziya, Malkiya, Miyamin, Eleyazar, Malkiya da Benahiya.
26 Elam capa thung hoi Mattaniah, Zekhariah, Jehiel, Abdi, Jerimoth hoi Elijah tinaw doeh.
Daga zuriyar Elam, akwai Mattaniya, Zakariya, Yehiyel, Abdi, Yeremot, da Iliya.
27 Zattu capanaw thung hoi Elioenai, Eliashib, Mattaniah Jerimoth, Zabad hoi Aziza tinaw doeh.
Daga iyalin Zattu, akwai Eliyohenai, Eliyashib, Mattaniya Yeremot da Zabad da Aziza.
28 Bebai capanaw thung hoi Jehohanan, Hananiah, Zabai hoi Athlai.
Daga zuriyar Bebai, akwai Yehohanan, Hananiya, Zabbai, da Atlai.
29 Bani capanaw thung hoi Meshullam, Malluck, Adaiah, Joshub, Sheal hoi Jerimoth tinaw doeh.
Daga zuriyar Bani, akwai Meshullam, Malluk, Adahiya, Yashub, Sheyal, da Ramot.
30 Phathmoab capanaw thung hoi Adna, Khelal, Benaiah, Maaseiah, Mattaniah, Bezalel, Binnui, hoi Manasseh tinaw doeh.
Daga zuriyar Fahat-Mowab, akwai Adna, Kelal, Benahiya, Ma’asehiya, Mattaniya, Bezalel, Binnuyi, da Manasse.
31 Harim capanaw thung hoi Eliezer, Isshijah, Malkhijah, Shemaiah, Simeon.
Daga zuriyar Harim, akwai Eliyezer, Isshiya, Malkiya, Shemahiya, Simeyon,
32 Benjamin, Malluck hoi Shemariah tinaw doeh.
Benyamin, Malluk da Shemariya.
33 Hashum capanaw thung hoi Mattenai, Mattattah, Zabad, Eliphelet, Jeremai, Manasseh hoi Shimei tinaw doeh.
Daga zuriyar Hashum, akwai Mattenai, da Mattatta, Zabad, Elifelet, Irmai, Manasse, da Shimeyi.
34 Bani capanaw thung hoi Maadai, Amram, Uel.
Daga zuriyar Bani, akwai Ma’adai, Amram, Yuwel,
35 Benaiah, Bedeiah, Kheluh.
Benahiya, Bedeya, Keluhi,
36 Vaniah, Meremoth, Eliashib.
Baniya, Meremot, Eliyashib,
37 Mattaniah, Mattenai, Jaasu.
Mattaniya, Mattenai da Ya’asu.
38 Bani, Binnui, Shimei.
Daga zuriyar Binnuyi, akwai Shimeyi,
39 Shelemiah, Nathan, Adaiah.
Shelemiya, Natan, Adahiya,
40 Maknadebai, shashai, Sharai.
Maknadebai, Shashai, Sharai,
41 Azarel, Shelemiah, Shemariah.
Azarel, Shelemiya, da Shemariya,
42 Shallum, Amariah, hoi Joseph tinaw doeh.
Shallum da Amariya da Yusuf.
43 Nebo capanaw thung hoi Jeiel, Mattithiah, Zabad, Zebina, Iddo, Joel hoi Benaiah tinaw doeh.
Daga zuriyar Nebo, akwai Yehiyel, Mattitiya, Zabad, Zebina, Yaddai, Yowel da Benahiya.
44 Hetnaw pueng teh miphun alouke yu lah ka lat e taminaw doeh, tami tangawn ni a yunaw koehoi ca catoun a hmu awh.
Dukan waɗannan sun auri baƙin mata, waɗansunsu suna da’ya’ya.

< Ezra 10 >