< Ezekiel 8 >
1 Ataruknae kum, ataruknae thapa, hnin panga hnin vah, kai teh kama im ka tahung navah, Judah miphun kacuenaw kaie hmalah a tahung awh navah, Bawi Jehovah e kut hah kaie lathueng vah a pha.
A shekara ta shida, a wata shida a ranar ta biya, yayinda nake zaune a gidana dattawan Yahuda kuma suna zaune a gabana, hannun Ubangiji Mai Iko Duka ya zo a kaina a can.
2 Ka khet navah hmai patetlah ka kamnuek e tami hah ao. A keng koehoi a rahim lah hmai patetlah a kamnue. A keng koehoi a lathueng lah a kamnue teh a ang poung.
Na duba, sai na ga siffa kamar na mutum. Daga kwankwaso zuwa ƙasa ya yi kamar wuta, kuma daga kwankwaso zuwa sama kamanninsa ya yi haske yana ƙyalli kamar ƙarfe mai haske.
3 Kut patet e a dâw teh, ka tampa sam dawk hoi na man. Muitha ni talai hoi kalvan rahak vah na tawm teh, Cathut a kamnuenae im Jerusalem vah a ceikhai. Jerusalem a tung lae tumdumnae thung hoi longkha tho tarennae a kung koe, na phakhai. Hawvah lungkhueknae meikaphawk tahungnae hmuen ao teh, hote ni a lungkhuek sak.
Ya miƙa abin da ya yi kamar hannu ya kama a gashin kaina. Ruhu ya ɗaga ni tsakanin sama da ƙasa, a cikin wahayoyi kuma Allah ya ɗauke ni zuwa Urushalima, zuwa ƙofa zuwa gabas na cikin fili, inda gunki mai tsokanar kishi yake tsaye.
4 Khenhaw! ayawn dawk ka hmu e patetlah haw tueng vah Isarel Cathut bawilennae ao.
A can gabana kuwa ga ɗaukakar Allah na Isra’ila, kamar a wahayin da na gani a fili.
5 Ahni ni tami capa atunglah kamlang nateh na mit hoi radoung haw telah ati. Hottelah atunglah kangvawi laihoi ka mit hoi ka radoung navah, khenhaw! khoungroe takhang kâennae koe lungkhueknae meikaphawk teh ao.
Sai ya ce mini, “Ɗan mutum, duba waje arewa.” Sai na duba, a mashigin arewa na ƙofar bagaden kuwa na ga wannan gunki na tsokanar kishi.
6 Ahni ni kai koevah, tami capa hmuen kathoung koehoi kahlatpoung lah na kacetkhaikung ahnimouh ni panuet hoe ka tho e hah Isarel imthung ni hitueng vah a sak awh. Hmuen kathoung koehoi kahlatpoung lah ka cei nahanelah, a sak awh e hah na hmu maw. Atu kamlang haw panuet hoe ka tho e na hmu han.
Ya kuma ce mini, “Ɗan mutum, ka ga abin da suke yi, abubuwan banƙyamar da gidan Isra’ila ke yi a nan, abubuwan da za su kore ni daga wuri mai tsarkina? Amma za ka ga abubuwan da suka ma fi banƙyama.”
7 Thongma e takhang koe totouh kai hah na ceikhai teh, ka khet navah tapang dawk a kâko teh ao.
Sa’an nan ya kawo ni mashigin filin. Na duba, na kuma ga rami a bango.
8 Tami capa, tapang hah tai haw ati e patetlah kai ni ka tai teh takhang ka aw e ka hmu.
Ya ce mini, “Ɗan mutum, yanzu ka haƙa cikin bangon.” Da na haƙa cikin bangon sai na ga ƙofar shiga a can.
9 Kâen haw hie hmuen koe na sak awh e panuettho e kahawi hoeh e a sak awh e khenhaw! telah ati.
Sai ya ce mini, “Shiga ka ga mugaye da kuma abubuwa banƙyamar da suke yi a can.”
10 Ka kâen teh ka khet navah, tapang tangkuem dawk vonpui hoi kâva e khe hoi, panuettho e moithang phunkuep hoi Isarel imthungnaw ni a bawk awh e meikaphawknaw e mei kaawm pueng hah a vo awh.
Na kuwa shiga na duba, sai na ga zāne-zāne ko’ina a bangon na kowane irin abubuwa masu rarrafe da kuma dabbobi masu ƙazanta da dukan gumakan gidan Isra’ila.
11 Hote a hmalah Isarel kacuenaw thung hoi tami 70 touh a kangdue awh. A lungui vah Shaphan capa Jaazaniah hah a kangdue. Tami pueng ni tongben rip a patuep awh teh, hmuitui hmai a sawi awh teh, hmaikhu teh a tung lah a luen.
A gabansu ga dattawa saba’in na gidan Isra’ila tsaye a cikinsu, Ya’azaniya ɗan Shafan kuwa yana tsaye a cikinsu. Kowa yana da farantin ƙona turare a hannunsa, tulin hayaƙin turare mai ƙanshi ya tunnuƙe zuwa sama.
12 Tami capa, Isarel imthung kacuenaw ni ka hmawt e rakhan thung kaawm e a sak awh e hno hah na hmu toung. Ahnimouh ni BAWIPA ni na hmawt hoeh, BAWIPA ni ram teh a ceitakhai toe telah ati awh.
Ya ce mini, “Ɗan mutum, ka ga abin da dattawan gidan Isra’ila suke yi a cikin duhu, kowa yana a ɗakin tsafin gunkinsa? Suna cewa, ‘Ubangiji ba ya ganinmu; Ubangiji ya yashe ƙasar.’”
13 Ahni ni kai koevah, bout kamlang haw, a sak awh e panuetthopounge hah na hmu hah telah ati.
Ya kuma ce, “Za ka gan su suna yin abubuwan da suka fi waɗannan banƙyama.”
14 BAWIPA im atunglah hoi kâennae longkha tho koe na ceikhai. Khenhaw! haw vah napuinaw Tammuz pouk laihoi a ka awh teh a tahung awh.
Sa’an nan ya kawo ni mashigin arewa na ƙofar gidan Ubangiji, sai na ga mata zaune a can, suna makokin Tammuz.
15 Ahni ni kai koevah, Oe tami capa, hetheh na hmu maw. Hethlak patenghai panuettho e hai a na hmu han rah telah ati.
Ya ce mini, “Ɗan mutum, ka ga wannan? Za ka ga abubuwan da suke masu banƙyama fiye da wannan.”
16 BAWIPA im thongma a thung totouh na ceikhai teh, bawkim takhang bawkim alawilah hoi khoungroe rahak vah, tami 25 touh bawkim hnamthun takhai hoi kanîtholah a kamlang awh teh, Kanîtholae kanî hah a bawk awh.
Sa’an nan ya kawo ni cikin fili na cikin gidan Ubangiji, a can kuwa a ƙofar haikali, tsakanin shirayi da bagade, akwai kamar mutum ashirin da biyar. Suka ba haikalin Ubangiji baya suna fuskanta wajen gabas, suna rusuna wa rana a gabas.
17 Ahni ni kai koe hetheh na hmu ou. Oe tami capa, panuettho e a sak awh teh, hi tueng a sak awh e hah Judah imthung hanelah hno titca namaw. Ram teh kâyue kâounnae hoi a kawi sak awh teh, ka lungkhuek sak awh, thinghna hoi a hnawng a ramuk awh.
Ya ce mini, “Ka ga wannan, ɗan mutum? Ƙaramin abu ne gidan Yahuda su yi abubuwan banƙyamar da suke yi a nan? Dole ne su cika ƙasar da rikici su kuma ci gaba da tsokane ni in yi fushi? Dube su suna tsokanata!
18 Hatdawkvah, kai ni hai lungkhueknae lahoi ka sak van han. Ka mit ni roun mahoeh, ka pahren mahoeh. Ka hnâkâko dawk kacaipounglah ka hram nakunghai ka thai pouh mahoeh telah ati.
Saboda haka zan hukunta su cikin fushi; Ba zan dube su da tausayi ko kuwa in ƙyale su ba. Ko da yake suna ihu a kunnuwana, ba zan saurare su ba.”