< Ezekiel 25 >
1 BAWIPA e lawk kai koe a pha teh,
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 tami capa Ammonnaw kangdout sin haw, ahnimouh taranlahoi pâpho.
“Ɗan mutum, ka fuskanci wajen Ammonawa ka kuma yi annabci a kansu.
3 Ammonnaw koevah, Bawipa Jehovah e lawk hah thai awh, Bawipa Jehovah ni hettelah a dei, hmuen kathoung hah na khin sak lahun navah, Isarel ram taran lahoi, raphoe lah ao lahun nah, Judah imthung hah san lah a hrawi navah, haha! telah na ti dawkvah,
Ka ce musu, ‘Ku ji maganar Ubangiji Mai Iko Duka. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kun ce “Yauwa” a kan wuri mai tsarkina sa’ad da aka ƙazantar da shi da kuma a kan ƙasar Isra’ila sa’ad da aka mai da ita kufai da lokacin da aka kai mutanen Yahuda bautar talala,
4 nang teh Kanîtholae taminaw koe a coe awh hanelah na poe han, nang dawkvah roenae rim a sak awh vaiteh, haw e hmuen koe ao awh han, nange a pawhik a ca vaiteh, nange maito sanutui a nei awh han.
saboda haka zan ba da ku ga mutanen Gabas abin mallaka. Za su kafa sansanoninsu su yi tentunansu a cikinku; za su ci’ya’yan itatuwanku su kuma sha madararku.
5 Rabbah kho teh kalauk im lah ka sak vaiteh, Ammon hah saringhunaw a tabonae lah ka coung sak han, hottelahoi BAWIPA lah ka o tie a panue awh han.
Zan mai da Rabba wurin kiwo don raƙuma, Ammon kuma wurin hutu don tumaki. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
6 Bangkongtetpawiteh, Bawipa Jehovah ni hettelah a dei, Isarel ram thung vah na kut na tambei teh, na khok na pano, a rawknae kong dawkvah, lungthin abuemlah na lunghawi dawkvah,
Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kun tafa hannuwanku kuka kuma buga ƙafafunku, kuna farin ciki don nuna dukan ƙiyayyarku a kan ƙasar Isra’ila,
7 khenhaw! na lathueng vah ka kut ka dâw teh, miphunnaw koe lawphno patetlah na man sak han. Ram pueng koehoi nang teh na thei vaiteh, hote ram dawk hoi koung na pâmit han. Na raphoe vaiteh, BAWIPA lah ka o tie hah na panue han telah ati.
saboda haka zan miƙa hannuna gāba da ku in kuma ba da ku ganima ga al’ummai. Zan datse ku daga al’ummai in kuma kore ku daga ƙasashe. Zan hallaka ku, za ku kuwa san cewa ni ne Ubangiji.’”
8 Bawipa Jehovah ni hettelah a dei, Moab hoi Seir ni khenhaw! Judah imthung teh miphun alouke patetlah doeh ao van telah ati awh dawkvah,
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Mowab da Seyir sun ce, “Duba, gidan Yahuda ta zama sauran al’ummai,”
9 khenhaw! Moab khopui e ram, a khopui e khori hah kamceng sak vaiteh, ka lentoe e ram Bethjeshimoth, Baalmeon Kiriathaim naw hah,
saboda haka zan buɗe ƙofar shiga Mowab, farawa daga garuruwan da suke kan iyaka, Bet-Yeshimot, Ba’al-Meyon da Kiriyatayim, darajar ƙasar.
10 Ammonnaw hah miphunnaw thung dawk hoi pou panuekhai e lah o hoeh nahan, Kanîtholae taminaw a coe hane ham hah, Ammonnaw hoi cungtalah ka poe han.
Zan ba da Mowabawa tare da Ammonawa ga mutanen Gabas abin mallaka, don kada a ƙara tuna da Ammonawa a cikin al’ummai;
11 Moab ram dawk lawkcengnae hah ka kuep sak vaiteh, BAWIPA lah ka o tie a panue awh han telah ati.
zan hukunta Mowabawa. Ta haka za su san cewa ni ne Ubangiji.’”
12 Bawipa Jehovah ni hettelah a dei. Edom ni Judah imthungnaw taranlahoi moi a pathung teh, a mahmawk lahoi ahnimae lathueng vah, kalenpoung lah yonnae a sak.
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Edom ya ɗauki wa kanta fansa a kan gida Yahuda, ta yi babban laifi ta wurin yin haka,
13 Hatdawkvah, Bawipa Jehovah ni hettelah a dei. Edom lathueng vah, ka kut ka dâw vaiteh, amae thung hoi tami hoi saring he ka raphoe han. Teman kho teh kingdi sak han. Dedan totouh tahloi hoi a rawp awh han.
saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan miƙa hannuna a kan Edom in kashe mutanenta da dabbobinsu. Zan sa ta zama kufai, kuma tun daga Teman har zuwa Dedan za a kashe su da takobi.
14 Ka tami Isarelnaw e kut hoi a moi ka pathungnae hah, ka pha sak han, Edom e lathueng vah ka lungkhueknae hoi ka lungreithainae patetlah a sak awh han. A moipathungnae pawlawk dawk hoi a panue awh han telah Bawipa Jehovah ni a dei.
Zan ɗau fansa a kan Edom ta hannun mutanena Isra’ila, za su kuwa hukunta Edom bisa ga fushina da hasalata; za su san sakayyata, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
15 Bawipa Jehovah ni hettelah a dei, Filistinnaw ni ayan hoi na maithoe awh kecu dawkvah, tami thei ngainae lungthin hah tawn laipalah, moipathung awh dawkvah,
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Filistiyawa sun yi sakayya, suka ɗauki fansa da mugunta a zukatansu, da kuma daɗaɗɗen ƙiyayya sun nemi su hallaka Yahuda,
16 Bawipa Jehovah ni hettelah a dei, khenhaw! Filistinnaw taranlahoi ka kut ka dâw vaiteh, Kherethnaw hah tâkhawng teh, tuipuipaling teng e kacawie hah be ka raphoe han.
saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gab da miƙa hannuna a kan Filistiyawa, zan kuwa datse Keretawa in kuma hallaka waɗanda suka rage a bakin teku.
17 Ka patawpoung e tounnae hoi ka patawpoung lah moi ka pathung han, hot patetlah ahnimae lathueng vah, moi ka pathung torei teh, BAWIPA lah ka o tie hah a panue awh han, telah ati.
Zan yi musu babbar sakayya da hukunci mai tsanani cikin hasalata. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na ɗauki fansa a kansu.’”