< 2 Samuel 5 >
1 Isarel miphunnaw Hebron kho Devit aonae koe a tho awh. Kaimanaw hah na hru hoi na thitak katang doeh.
Dukan kabilar Isra’ila suka zo wurin Dawuda a Hebron suka ce, “Mu nama da jininka ne.
2 Ayan vah kaimae lathueng Sawl siangpahrang lah ao navah, Isarelnaw katâcawtkhaikung hoi kâenkhaikung lah ao. BAWIPA ni ka tami Isarelnaw na paca han, na uk han telah nang koe ati telah a ti.
A dā da Shawulu yake sarauta a bisanmu, kai ne kake bi Isra’ilawa zuwa yaƙe-yaƙensu. Ubangiji kuwa ya ce maka, ‘Za ka zama makiyayi mutanena Isra’ila, za ka kuma zama sarkinsu.’”
3 Hatdawkvah, Isarel kacuenaw Hebron kho siangpahrang koevah a tho awh. Devit siangpahrang ni Hebron vah BAWIPA e hmalah ahnimouh hoi lawkkamnae ka sak. Devit teh Isarelnaw e siangpahrang lah satui a awi awh.
Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka zo wurin Sarki Dawuda a Hebron, sarki ya yi yarjejjeniya da su a gaban Ubangiji, suka kuwa naɗa Dawuda sarki bisa Isra’ila.
4 Devit ni uknae a kamtawng navah kum 30 a pha teh kum 40 touh a uk.
Dawuda yana da shekara talatin ɗaya sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara arba’in.
5 Hebron kho dawk ao teh, Judahnaw kum 7 thapa 6 touh a uk. Jerusalem vah Isarel hoi Judahnaw kum 33 a uk.
A Hebron ya yi mulki a bisa Yahuda shekara bakwai da wata shida, a Urushalima kuma ya yi mulki a bisa Isra’ila da Yahuda shekara talatin da uku.
6 Siangpahrang ni a taminaw a kaw teh, hote ram dawk kho ka sak e Jebusit tami onae koe Jerusalem kho lah a cei awh. Ahnimanaw ni hete kho dawk na kâen awh mahoeh. Mitdawn hoi khokkhemnaw ni hai Devit teh hete kho thung kâen mahoeh, ahnimouh ni na ngang awh han telah ati awh.
Sarki da mutanensa suka tafi Urushalima don su kai wa Yebusiyawan da suke zaune a can hari, Yebusiyawa suka ce wa Dawuda, “Ba za ka shiga nan ba; ko makafi da guragu kaɗai ma za su kore ka.” Suka yi tsammani suna cewa, “Dawuda ba zai iya shiga can ba.”
7 Hateiteh, Devit ni Devit khopui tie Zion rapanim a tuk teh a tâ.
Duk da haka, Dawuda ya kame kagarar Sihiyona, wadda ta zama Birnin Dawuda.
8 Hote hnin dawk Devit ni, Devit hringnae ni a hmuhma e Jebusit tami mitdawn hoi khokkhem thei hanelah tui pat ka raka e ransa pueng teh ransabawinaw e lû lah ka o sak han, hatdawkvah mitdawn hoi khokkhemnaw teh im thung kâen mahoeh telah a ti.
A ranar, Dawuda ya ce, “Duk wanda zai kame Yebusiyawa, dole yă yi amfani da wuriyar ruwa don yă kai ga waɗannan ‘guragu da makafi’ waɗanda suke abokan gāban Dawuda.” Shi ya sa suka ce, “‘Makafi da guragu’ ba za su shiga fadan sarki ba.”
9 Devit teh rapanim dawk ao teh, Devit khopui telah min a phung. Millo hmuen a tengpam thoseh, a thung lahai thoseh a sak.
Sai Dawuda ya zauna a kagarar, ya kuma kira ta Birnin Dawuda. Ya gina wuraren da suke kewaye da ita, tun daga madogaran gini zuwa ciki.
10 Hottelah hoi Devit teh hoe a roung teh ransahu BAWIPA Cathut hoi rei ao.
Ya yi ta ƙara ƙarfi, gama Ubangiji Allah Maɗaukaki yana tare da shi.
11 Taire siangpahrang Hiram ni Devit koe patounenaw a patoun teh, Sidar thing, imsakkathoum, talungdêikathoum a patoun awh teh, Devit hane im a sak pouh awh.
To, Hiram sarkin Taya ya aiki manzanni wurin Dawuda tare da gumaguman itacen al’ul, da kafintoci, da kuma maginan duwatsu, suka kuwa gina wa Dawuda fada.
12 BAWIPA ni Isarelnaw koe siangpahrang lah ahni teh a caksak e hoi, a tami Isarelnaw hanelah uknaeram a tawmrasang tie Devit ni a panue.
Dawuda kuwa ya gane Ubangiji ya naɗa shi sarki bisa Isra’ila, ya kuma ɗaukaka masarautarsa saboda mutanensa Isra’ila.
13 Devit ni Hebron kho hoi a kampuen hnukkhu, Jerusalem khothung e yu a puidonaw bout a la teh, a ca moikapap bout a tawn.
Bayan ya bar Hebron, Dawuda ya ƙara ɗauko wa kansa waɗansu ƙwarƙwarai da mata a Urushalima. Aka haifa masa’ya’ya maza da mata.
14 Jerusalem kho sak Devit ni a khe e a canaw e min teh: Shammua, Shobab, Nathan, Solomon,
Waɗannan su ne sunayen’ya’yan da aka haifa masa a can. Shammuwa, Shobab, Natan, Solomon,
15 Ibhar, Elishua, Nepheg, Japhia,
Ibhar, Elishuwa, Nefeg, Yafiya,
16 Elishama, Eliada hoi Eliphelet naw hah doeh.
Elishama, Eliyada da Elifelet.
17 Filistinnaw ni Devit hah Isarelnaw koe siangpahrang lah ao nahan satui a awi tie a panue awh navah, Filistinnaw pueng ni Devit tawng hanelah a cei awh. Devit ni hote hah a thai toteh rapanim dawk hoi a kum.
Da Filistiyawa suka ji labari an shafe Dawuda sarki a bisa Isra’ila, sai suka haura da ƙarfi sosai don su nema shi, amma Dawuda ya ji labarin sai ya gangara zuwa mafaka.
18 Filistinnaw hai a cei awh teh, Rephaim yawn dawk phang a kâkayei awh.
To, fa, Filistiyawa suka zo suka baje ko’ina a cikin Kwarin Refayim;
19 Devit ni Filistinnaw tuk hanelah ka cei han maw, ka kut dawk na poe han maw telah BAWIPA a pacei. BAWIPA ni Devit koe, cet loe. Kai ni Filistinnaw na kut dawk na poe han telah atipouh.
saboda haka Dawuda ya nemi nufin Ubangiji ya ce, “In tafi in kai wa Filistiya hari? Za ka bashe su a hannuna?” Ubangiji ya amsa masa ya ce, “Je ka, gama tabbatacce zan bashe Filistiyawa a hannunka.”
20 Devit teh Baalperazim lah a cei teh, hawvah Devit ni ahnimouh a thei. BAWIPA ni, tui ni a raphoe e patetlah katarannaw hah ka hmaitung vah koung na raphoe pouh telah ati. Hatdawkvah, hote hmuen hah Baalperazim telah min a phung.
Saboda haka Dawuda ya tafi Ba’al-Ferazim, a can ya ci su da yaƙi. Sai ya ce, “Kamar yadda ruwa yakan fasu, haka Ubangiji ya kakkarya abokan gābana a gabana.” Saboda haka aka kira wurin Ba’al-Ferazim.
21 Hote hmuen koe Filistinnaw ni a ceitakhai e meikaphawknaw hah Devit hoi a taminaw ni koung a raphoe pouh.
Filistiyawa suka bar gumakansu a can, Dawuda da mutanensa kuwa suka kwashe su.
22 Filistinnaw bout a tho awh teh, Rephaim yawn dawk phang a kâkayei awh.
Har yanzu Filistiyawa suka sāke haurawa suka bazu a Kwarin Refayim;
23 Devit ni BAWIPA koe a pacei navah, ahni ni takhang awh hanh, a hnuk lahoi kalup awh nateh batue kahrawng koehoi rongyawn awh.
saboda haka Dawuda ya nemi nufin Ubangiji, ya kuwa ce, “Kada ka haura kai tsaye, amma ka kewaya ta bayansu ka fāɗa musu a gaban itatuwan balsam.
24 Batuekung koe a pawlawk na thai toteh tuk awh loe, bangkongtetpawiteh, Filistinnaw tuk hanelah na hmalah BAWIPA a la cei toe tinae doeh.
Da zarar ka ji tafiya kamar na takawar sojoji tana a bisan itatuwan balsam, sai ka yi maza, gama wannan alama ce cewa Ubangiji ya sha gabanka don yă karkashe sojojin Filistiyawa.”
25 BAWIPA ni kâlawk a poe e patetlah Devit ni a sak. Filistinnaw hah Geba hoi Gezer totouh a thei.
Saboda haka Dawuda ya aikata yadda Ubangiji ya umarce shi, ya kuma karkashe Filistiyawa tun daga Geba har zuwa Gezer.