< 2 Siangpahrang 19 >
1 Siangpahrang Hezekiah ni hote hah a thai toteh, a khohna hah a phi teh, burihni a kâkhu teh BAWIPA im vah a kâen.
Da sarki Hezekiya ya ji haka, sai ya kyakketa tufafinsa, ya sa tufafin makoki, ya shiga haikalin Ubangiji.
2 Imthung kahrawikung Eliakim hoi cakathutkung Shebna hoi vaihma kacuenaw ni burihni a kâkhu awh teh Amos capa profet Isaiah koevah a patoun awh.
Ya aiki Eliyakim sarkin fada, Shebna marubuci da shugabannin firistoci, dukansu sanye da tufafin makoki, zuwa wurin annabi Ishaya ɗan Amoz.
3 Siangpahrang ni Isaiah koevah, sahnin teh rucatnae hoi yuenae hoi pacekpahleknae hnin doeh. Bangkongtetpawiteh, camo a khenae tue yo a pha ei teh khe nahane a tha awm hoeh.
Suka ce masa, “Hezekiya ya ce, yau ranar wahala ce, da ta cin mutunci, da ta shan kunya, ga shi,’ya’ya suna gab da a haife su, amma ba ƙarfin da za a yi yunƙuri a haife su.
4 A bawipa Assiria siangpahrang ni, kahring Cathut pacekpahlek hanlah, a patoun e Rebshakeh ni a dei e lawknaw pueng hah BAWIPA Cathut ni thai vaiteh BAWIPA Cathut ni a thai e lawk dawk hoi a yue thai. Hote kecu dawk kaawmnaw hanlah ratoum pouh naseh.
Mai yiwuwa Ubangiji Allahnka ya ji dukan maganganun sarkin yaƙi, wanda maigidansa, sarkin Assuriya, ya aiko don yă rena Allah mai rai. Bari Ubangiji Allahnka yă tsawata masa saboda maganar da ya ji. Saboda haka ka yi addu’a domin raguwar da har yanzu suke a raye.”
5 Hahoi teh, Siangpahrang Hezekiah e taminaw teh Isaiah koevah a cei awh.
Da fadawan sarki Hezekiya suka isa wurin Ishaya,
6 Isaiah ni, ahnimouh koe na bawipa koe hettelah na dei awh han, BAWIPA ni hettelah a dei, na thai awh e lawk Assiria siangpahrang e taminaw ni na pacekpahlek awh e hah taket hanh awh.
Ishaya ya ce musu, “Ku faɗa wa maigidanku, in ji Ubangiji, ‘Kada abin da ka ji yă firgita ka, wato, waɗannan kalmomin da karen nan na sarkin Assuriya ya yi saɓo da su.
7 Khenhaw! ahnimouh koe muitha buet touh ka patoun han. Kamthang a thai vaiteh, ama ram lah a ban han. Hahoi teh amae ram dawk roeroe vah, tahloi hoi ka kamlei sak han telah atipouh.
Saurara! Zan sa masa wani ruhun da zai sa yă ji wata jita-jitar da za tă sa yă koma ƙasarsa. A can zan sa a kashe shi da takobi a ƙasarsa.’”
8 Hahoi Rebshakeh teh, a ban teh Assiria siangpahrang ni, Libnah a tuk nah a hmu, bangdawk Lakhish hai yo a tâco toe tie hah a thai.
Da sarkin yaƙin ya ji cewa sarkin Assuriya ya bar Lakish, sai ya janye, ya kuma iske sarkin yana yaƙi da Libna.
9 Hahoi khenhaw! nang hoi kâtuk hanelah, a kamthaw toe telah, Tirhakah, Ethiopia siangpahrang kong ayâ ni a dei e hah a thai. Hahoi Hezekiah koe patounenaw bout a patoun.
To, Sennakerib ya sami labari cewa Tirhaka, mutumin Kush sarkin Masar, yana zuwa masa da yaƙi. Saboda haka ya sāke aika manzanni zuwa wurin Hezekiya cewa,
10 Hettelah Judah siangpahrang Hezekiah koe na dei pouh han, na kângue awh e na Cathut ni, Jerusalem heh Assiria siangpahrang kut dawk poe mahoeh na ti awh e hah, telah na dum hanh naseh.
“Ku faɗa wa Hezekiya sarkin Yahuda, kada ka bar allahn da kake dogara gare shi yă ruɗe ka cewa, ‘Urushalima ba za tă fāɗi a hannun sarkin Assuriya ba.’
11 Khenhaw! Assiria siangpahrangnaw ni, ramnaw pueng koung a raphoe teh, ahnimouh lathueng a sak e naw na thai toe. Nang hah na rungngang han tangngak ma aw
Ba shakka ka riga ka ji abin da sarkin Assuriya ya yi da dukan ƙasashe, yana hallaka su gaba ɗaya. Kai kuwa kana ji za a cece ka?
12 Kaie mintoenaw ni a raphoe e Gozan, Haran, Rezeph, Eden tami Telassar ahnimae cathutnaw ni a rungngang awh nama aw.
Allolin al’umman da kakannina suka hallaka, sun cece su ne, allolin Gozan, da na Haran, da na Rezef, da kuma na mutane Eden da suke a Tel Assar?
13 Hamath siangpahrang, Arpad siangpahrang, Sepharvaim khopui siangpahrang, Hamath siangpahrang hoi Ivvah siangpahrangnaw hateh, namaw koung ao awh vaw telah atipouh.
Ina sarkin Hamat, da sarkin Arfad, da sarkin birnin Sefarfayim, ko na Hena da kuma na Iffa?”
14 Hezekiah ni, a patounenaw kut dawk e ca hah a hmu teh a touk pouh. Hahoi teh Hezekiah teh BAWIPA im a kâen teh BAWIPA hmalah ca teh a kadai.
Hezekiya ya karɓi wasiƙar daga manzannin ya karanta. Sa’an nan ya tashi ya tafi haikalin Ubangiji ya shimfiɗa wasiƙar a gaban Ubangiji.
15 Hezekiah ni BAWIPA hmalah a ratoum teh Oe Bawipa, Cherubim rahak vah kho ka sak e Isarel Cathut, nang nama dueng doeh talai van pueng uknaeram thung Cathut lah na kaawm, talai hoi kalvan hai nang ni na sak e doeh.
Hezekiya kuwa ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda yake zaune tsakanin kerubobi, kai kaɗai ne Allah bisa dukan mulkokin duniya. Kai ka yi sama da duniya.
16 Oe BAWIPA, na hnâpakeng haw nateh, na thai pouh haw. Oe BAWIPA na mit padai nateh khenhaw! kahring Cathut pacekpahlek e Sennacherib ni lawk a dei e hah thai haw.
Ka kasa kunne, ya Ubangiji, ka ji; ka buɗe idanunka ya Ubangiji ka gani; ka saurari kalmomin da Sennakerib ya aiko don yă yi wa Allah mai rai ba’a.
17 BAWIPA, Assiria siangpahrangnaw ni, miphunnaw hoi a ramnaw teh a raphoe ei.
“Da gaske ne, ya Ubangiji, cewa sarakunan Assuriya sun hallakar da waɗannan al’ummai da ƙasashensu.
18 A cathutnaw hai hmai dawk koung a phum pouh ei. Bangkongtetpawiteh, hotnaw teh cathutnaw ka tang na hoeh. Tami kut hoi sak e, thing hoi talung doeh, hatdawkvah a raphoe awh.
Sun jefar da allolinsu cikin wuta, suka hallaka su, gama ba alloli ba ne, katakai ne da kuma duwatsu, ayyukan hannuwan mutane.
19 Hatdawkvah oe BAWIPA, kaimae Cathut nang nama dueng doeh, BAWIPA Cathut lah na kaawm tie talai uknaeramnaw pueng ni, nang na panue thai nahan, na kut hoi na rungngang lah, telah atipouh.
To, ya Ubangiji Allahnmu, ka cece mu daga hannunsa, don dukan mulkokin duniya su san cewa kai kaɗai, ya Ubangiji ne Allah.”
20 Hote tueng dawk Amos capa Isaiah ni, Hezekiah koevah Isarel BAWIPA Cathut ni telah a dei. Assiria siangpahrang Sennacherib taran lahoi yah, kai koe a ratoum e teh ka thai toe.
Sai Ishaya ɗan Amoz ya aika da saƙo zuwa wurin Hezekiya cewa, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, na ji addu’arka game da Sennakerib sarkin Assuriya.
21 Hetheh, hot kong dawk hoi BAWIPA ni a dei e doeh. Zion canu tanglakacuem ni, pacekpahlek hoi na panuikhai e hah, Jerusalem canu ni a lû a kahek.
Ga abin da Ubangiji yana cewa game da shi, “‘Budurwar Sihiyona ta rena ka tana kuma yin maka ba’a. Diyar Urushalima ta kaɗa kanta yayinda kake gudu.
22 Apimaw a min na mathoe sak teh, na pacekpahlek. Apimaw lawk hoi na hram sin, na mit na ueng sin, Isarel tami kathoung koe kai ma.
Wane ne ka zaga, ka kuma yi masa saɓo? Wa kake gāba da shi har ka ɗaga muryarka, har ka tā da idanunka da fahariya? Kana gāba da Mai Tsarki na Isra’ila!
23 Na patounenaw hno lahoi BAWIPA teh na pacekpahlek. Kaie rangleng moikapap hoi Lebanon ram kadung poung hoi monnaw koe ka pha teh, haw e sidar thing kahawinaw hoi hmaica thingnaw ka tâtueng vaiteh, talai ahawinae ratu, kho a rasang na koe hoe a dung nah koevah, ka kâen han.
Ta wurin manzanninka ka tara wa Ubangiji zagi. Ka kuma ce, “Da yawa kekunan yaƙina na haye kan ƙwanƙolin duwatsu, wurin mafi tsawo na Lebanon. Na sassare itacen al’ul nasa mafi tsawo mafi daraja na itacen fir nasa. Na ratsa har can tsakiyar kurmi, mafi kyau na kurminsa.
24 Ram alouknaw e tui hah ka tai teh, ka tâco sak teh ouk ka nei, ka khoktabei ni Izip ramnaw pueng koung ka hak sak han telah ati.
Na tona rijiyoyi a ƙasashen waje na kuma sha ruwa a can. Da tafin ƙafafuna na busar da dukan rafuffukan Masar.”
25 Kai ni ayan hai ka sak e nahoehmaw, Atu teh kai ni ka sak e ti teh na panuek hoeh maw. Vaipuen lah a coung nahan raphoe e khopui rapan lah na o nahanelah, hottelah atu koung kahma sak toe.
“‘Ba ka taɓa ji ba? Tun da daɗewa na ƙaddara haka. Tuntuni kuwa na shirya shi; yanzu kuma na sa ya faru, cewa ka mai da birane masu katanga tarin duwatsu.
26 Hatdawkvah a thung a kaawm e taminaw teh, tha a youn awh dawkvah, a yawng awh teh yeirai a phu awh.
Ƙarfin mutanensu ya tsiyaye, suka razana aka kuma kunyata su. Suna kama da tsirai a gona, kamar sabon toho kamar ciyawa mai tohuwa bisa rufin ɗaki wanda ya bushe saboda zafi, kafin yă yi girma.
27 Hatei na onae hmuen na kâen, na tâco, kai taranlahoi na lungphuen tie ka panue.
“‘Amma na san wurin zamanka da fitarka da shigarka da yadda kake fushi da ni.
28 Bangkongtetpawiteh, kai taranlahoi na lungphuen pawiteh, kai koe ut na sin e teh ka hnâ koe koung a pha toe. Hatdawkvah na hnawng dawk hradang ka ta vaiteh, na pahni hah khakkhui vaiteh, hahoi na thonae koe lam hoi bout na ban sak han.
Domin kana fushi da ni reninka ya iso kunnuwata, zan sa ƙugiyata a hancinka da linzamina a bakinka, zan kuma sa ka koma a ta hanyar da ka zo.’
29 Hetheh, nang hanlah kamnuenae lah ao han. Takum teh amahmawk ka paw e hah, na khan awh vaiteh, palawng haiyah, amahmawk ka paw e na khan awh han. A kum pâthum teh, cang tu awh nateh, misur takha hah sak awh nateh a paw hah cat awh.
“Wannan zai zama alama a gare ka, ya Hezekiya, “Bana, za ku ci amfanin gonar da ya tsira da kansa, baɗi kuma amfanin gonar da ya tsiro daga na bara. Amma a shekara ta uku, za ku yi shuki, ku kuma girbe, ku dasa gonakin inabi, ku kuma ci’ya’yansa.
30 Judah imthungkhunaw thung dawk ka hlout ni teh kacawiraenaw ni, rahim lah khongyang a pabo vaiteh lathueng lah a paw a paw awh han.
Sau ɗaya kuma ragowar masarautar Yahuda za tă yi saiwoyi a ƙasa ta kuma ba da’ya’ya a bisa.
31 Bangtelah tetpawiteh, kaawm e naw hah Jerusalem lahoi a ban awh han. Zion mon dawk kacawiraenaw hah a cei awh han. Ransahu BAWIPA ngaikhainae lahoi hothateh, a sak han.
Gama daga Urushalima za a sami ragowa, daga Dutsen Sihiyona kuma za a sami waɗanda suka tsira. Himmar Ubangiji Maɗaukaki za tă cika wannan.
32 Hatdawkvah BAWIPA ni Assiria siangpahrang kong teh, telah doeh a dei. Ahni teh hete khopui kâen mahoeh. Khokhu dawk pala pathui mahoeh. Khopui hmalah bahling hah patue mahoeh, kho lawi vah talai na paten mahoeh.
“Saboda haka ga abin da Ubangiji ya ce game da sarkin Assuriya, “Ba zai shiga birnin nan ba ko yă harba kibiya a nan. Ba zai kusace ta da garkuwa ko yă yi mata zoben yaƙi ba.
33 A thonae lam koe lahoi a ban vaiteh, khopui thung kâen mahoeh.
Ta hanyar da ya zo ne zai koma; ba zai shiga birnin nan ba, in ji Ubangiji.
34 Kai kecu dawk hoi thoseh, ka san Devit kecu dawk hoi thoseh, hete khopui teh ka rungngang hanelah ka ring han, BAWIPA ni ati, telah tami a patoun.
Zan kāre birnin nan in cece ta, saboda kaina da kuma bawana Dawuda.”
35 Hahoi teh hote tangmin vah, BAWIPA kalvantami hah a cei teh, Assirianaw ni a roenae hmuen dawk 185,000 a thei awh. Amom maya a thaw toteh khenhaw! ro doeh patkâhai toe.
A daren nan mala’ikan Ubangiji ya fita ya kashe dakaru dubu ɗari da tamanin da biyu a sansanin Assuriyawa. Da mutane suka farka da safe, sai ga gawawwaki ko’ina.
36 Hahoi Assiria siangpahrang Sennacherib teh, a tâco, im vah a ban teh Nineveh kho vah pou ao.
Saboda haka Sennakerib sarkin Assuriya ya tā da sansanin ya kuma janye. Ya koma Ninebe ya zauna a can.
37 Hahoi, a cathut Nisroch im vah a bawk lahun nah a capa Adrammelek hoi Sharezer ni, tahloi hoi a thei roi teh, Ararat ram vah a yawng roi. Hahoi a capa Esarhaddon ni a yueng lah a uk.
Wata rana yayinda yake sujada a haikalin Nisrok, allahnsa, sai’ya’yansa maza, Adrammelek da Sharezer suka kashe shi da takobi, suka gudu zuwa ƙasar Ararat. Sai Esar-Haddon ɗansa ya gāje shi.